Sashe 1
Kundi Uku Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
[23/11, 21:00] Ameerah Adam: *KUNDI UKU*
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
GargaÉ—i: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
Tsokaci: Daga Masarautu, Sarakuna da sunayen yanki duka ƙirƙira ne. Idan ya yi daidai da labarin wani/wata arashi ne.
SHAFI NA ÆŠAYA
DAULAR JABAL
Shekara ÆŠari Biyu Baya (1825)
Daular Jabal ta kasance ƙasaitacciyar daula, da ke ɗauke da dubban al'umma. Sunan Jabal ya samo asali daga yawan tsaunikan da yankin yake da su, mafi yawa suna zagaye da daular bakidaya. Daular Jabal tana kewaye da tekun Farjum, wanda yake da tsofaffin tarihi mabambamta masu cike da ban tsoro zuwa almara. Yankin yana ɗauke da tarin ƙabilu, waɗanda suke da bambamcin harshe a ƙalla sama da ɗari. Kuma yanki ne da yake da tarin arziƙin noma, kiwo da kasuwanci.
Tsaunin Jaddum shi ne katafaren tsaunin da ya fi kowanne tsauni girma a Daular Jabal, kuma tsauni ne mai matuƙar tsoratarwa da munanan al'amura suke faruwa a kansa. A labarin kunne ya girmi kaka, an ce a shekarun da suka gabata. Tsaunin matattarar wata ƙabila ce ta Gussum, wasu kuma suka ce sunan ƙabilar Hadira. Waɗannan ƙabilu da ake tantama a kansu, an ce sukan yanka duk jaririya macen da aka haifa ranar Alhamis, su shayar da jininta ga abin bautarsu da ke jingine a jikin tsaunin. Da matar shugabansu ta haihu a ranar Alhamis, sai suka nemi da a yanka jaririyar. Shi kuma Shugaban ya yi tsalle ya dire a kan hakan ba za ta kasance a kan jininsa ba, kuma da yake ya fi su ƙarfin dukiya da iko sai suka haƙura. Tun daga ranar, duk wanda ya hau kan tsaunin sai dai a ga ƙoƙon kansa ya gangaro ƙasa ya faɗi, kuma ba za a sake ganin gangar jikinsa ba.
Wasu kuma suka ce, bayan da aka yi wa shugabansu haihuwar mace ranar Alhamis. Da labarin ya bayyana, bai yi sallama da kowa ba ya tattara iyalinsa da jaririyar da aka haifa suka bar garin. Tun daga wannan ranar suke fuskantar mummunan hukunci ga duk wanda ya hau kan tsaunin da sunan bauta, domin abin bauta ya yi mummunan fushi da su.
Sai dai duk yawan tarin addininan da ke cikin daular, manyan addinai uku ne suke da tasiri a cikinta. Addinin Musulumci, addinin Kiristanci da kuma addinin gargajiya.
Addinin Musulumci
Addinin Musulumci addini ne da Musulmai suke bauta wa Allah Shi kaɗai, ba tare da waninSa ba. Wanda musulmai suke bin doron koyarwar Annabi Muhammad (S.A.W), wacca take ƙunshe cikin littafi mai tsarki (Alƙur'ani) da Allah (S.W.T) Ya yi wa Annabi Muhammad (S.A.W) wahayi, ta hanyar Mala'ika Jibrilu. Tare da bin Hadisansa, waɗanda suke tafe da sunnar yin aiki kyakkyawa da guje wa saɓon Allah.
Addinin Kiristanci
Addinin Kiristanci, addini ne na kiristoci da suke bautar Yesu Almasihu. Wanda mabiyansa suka ce yana koyar da ƙauna, gafara da aminci. Kuma sun yi imani da an gicciye Yesu, har ya tashi daga cikin matattu bayan kwana uku sannan ya hau sama. Kiristoci suna amfani da littafin Bible, daga rubutu daban-daban a cikin harsuna kamar Ibrananci, Aramaic da Girkanci.
Addinin Gargajiya
Addinin gargajiya, addini ne da mabiyansa suke amfani da koyarwar abubuwan bauta tun daga kan iyaye da kakkanni. Sun yi imani da tsafi, bokanci, sihiri da camfe-camfe, musamman a wasu ƙayyadaddun abubuwa kamar wurare, ranaku da sauransu. Addinin gargajiya, yana da bambamci da addinin Musulumci da na kiristanci. Saboda mabiyansa suna da abubuwan bauta kala-kala, wasu sukan bautawa ruwa, wuta, dutse, gumaka, rana, bishiya, kabari da sauransu. Kuma sun yi imani da taimakon aljanu, tare da ruhin kanninsu da suka gabata. Haka zalika ba su da littafin da suka amfani da shi a wurin bauta.
Sai dai kuma a Daular Jabal an samu dubban mabiya addinan gargajiya, sun yi haɗuwar tsintsiya wurin samar da littafi guda. Wanda aka sassaƙa bangon jikinsa da fatar wata tsohuwar damisa, wanda suka ajiye sirrikan kiran aljanu da kirarinsu. A silar haka ne aka samar da kundi ukun da mabiya addininan yankin suke amfani da shi. Sai dai kuma wani al'amari da ya faru a waɗansu shekaru ya sa bayyanar Kundin ke barazana, cimma buri da jefa kokonto a zuciyoyin Sarakuna ukun da ke rayuwa a cikin Daular.
Masarautar Kajjura (Sarki Gambo)
Masarautar Judala (Sarki GiÉ—aÉ—o)
Masarautar Zulwara (Sarki Dikko)
Sune masarautu da sarakunan da ke kewaye da Daular Jabal, kowannensu yana shimfiɗa mulki cike da isa, ƙasaita da izzar mulki. Domin gabaɗaya duka sarakunan babu wanda yake ga maciji da ɗan'uwansa, ba don komai ba. Sai don wasu munanan al'amura da suka gifta a tsakaninsu a lokautan da suka shuɗe.
MASARAUTAR KAJJURA
Zaune yake a kan lallausar kujerar da ta ƙayatu da kayan alatun gidan sarauta, fadawan da ke zagaye da shi gabaɗaya kawunansu a sunkuye yake suna jiran umarninsa. Daga gefe Shamaki ne ya sake russunar da kai, har zai fara magana. Daga jikin bangon gabas, suka ga fatar zakin da ta sha ado mai ɗauke da rubutun tsafin masarauta ta dare gida biyu. Kakkaifan takobi, kuma tsafaffan da ke saƙale a jikin fatar ta fitar da kanta daga cikin gidanta. Kamar walƙiya haka ya yi tsalle ta dira a daidai maƙoshin Sarki Gambo, duk yadda ya so matsawa sai ji ya yi ya manne da jikin kujerar da yake zaune.
Da ido ya dubi fadawansa domin su kawo masa ɗauki, amma ga mamakinsa sai ya ga sun bushe da dariyar ƙeta. Yana cikin wannan yanayin ya ga farin dattijon ya ratso daga bangon da ya dare. Ya ƙaraso gabansa yana sakin murmushi, kafin Sarki Gambo ya yi wani yunƙuri tsohon ya saka wannan takobin ya datse kansa ƙasa.
Firgigit! Sarki Gambo ya tashi zaune a razane daga mummunan mafarkin da ya yi yana shafa wuyansa, gumi ya shiga keto masa cikin tashin hankali.
"Allah Ya taimake ka, Allah Ya ba ka yawan rai..."
"Fulani akwai abin da yake shirin faruwa."
Sarki Gambo ya katse matarsa cikin damuwa, ajiyar zuciya Fulani Sadiya ta sauke ta ce.
"Ina fatan wannan ya kasance tuntuɓen fahimtarka ne ranka shi daɗe."
Bai amsa mata ba, ya miƙe jiki babu ƙwari. Don haka ita ma ta miƙe fuska ɗauke da damuwa ta ce.
"Ranka shi daÉ—e ina za ka je a tsohon daren nan?"
"Zan je na ga Malami!"
Ya furta mata yana naɗe fuskarsa da baƙin ƙyalle, cikin shigar ɓatar da sahu. Ganin har ya je bakin ƙofa ya sa ta bi shi da sauri ta ce.
"Amma ranka shi daÉ—e me zai hana ka bari zuwa safiy..."
"Idan har muka kai wannan lokacin, mummunan abu zai iya faruwa da mu. Kin san Bahaushe ya ce, da zafi-zafi ake dukan ƙarfe."
Ya furta yana fita, ba tare da ya waiwayo ta ba. Ta ɓoyayyar ƙofar da ke cikin ɗakin ajiyar kayan sirrinsa ya shiga, yana tafe cikin duhu yana haskawa da itacen da yake ci da wuta har ya ƙarasa. A bakin bukkarsa ya tsaya, sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya kutsa kansa cikin bukkar.
Kamar bai ji motsinsa ba, haka Malami ya cigaba da shafa yashin da ke kan faifan gabansa. A gefensa Sarki Gambo ya zauna, bayan da Malami ya ƙarasa sannan ya dube shi ya ce.
"Tun da na ganka da kanka ba aike ba, na san banza ba ta kai zomo kasuwa."
Sarki Gambo ya warware rawanin fuskarsa sannan ya ce.
"To ai zuwa da kai ya fi saƙo ne Malami, kuma tun da kuka gan mu yanzu ai kun san akwai gagarumar matsala."
"Ita na kwana ina duba maka, domin niyyata zuwa safiya na zo har ɗaki na same ka da maganar." Malami ya furta yana tsare Sarki Gambo da ido, cikin ƙaguwa ya ce.
"Amma me yake faruwa malami? Haka kuma muna fatan wankin hula ba zai kai mu dare ba."
"Najibullah Bn Muhammad Bn Najibullah Dogaran bulukiya!"
Jin sunan da Malami ya ambata ya sa Sarki Gambo miƙewa zumbur! Nan take jikinsa ya shiga karkarwa kamar wanda ya ji kiɗan gangi.
"A wayewar garin gobe jinin Najibullah wato Najibullah zai shigo masarautar nan, kuma idan har ba ka dakatar da shi ba shukar da ka jima da binnewa za ta bayyana. Domin zuri'arsa za ta bankaɗa maka labulen sirrin da babu wanda ya san da shi daga ni sai kai sai amintacciyarka." Malami ya ƙarasa maganar yana kallon Sarki Gambo, kamar zai yi kuka sarki ya dafa gwiwoyin Malami ya ce.
"Don girman Allah, da matsayin abin bautar da na fi aminta da ita ka taimaka mini Malami." Murmushi ya yi masa ya ce.
"Zan taimaka maka Gambo, kamar yadda na rife sirrin addinin da kake bautawa, saɓanin na Musulumci da kake yaudarar talakawanka da shi." A fili Sarki Gambo ya sauke ajiyar zuciya yana lumshe ido, Malami ya cigaba da cewa.
"Lokacin tashin alƙiyamarka ya zo Gambo, matuƙar ba ka hallaka jinin Najibullah ba. Kuma lokacin mallakar Kundi ukunka ya bayyana, domin kuwa Za a kawo Najibullah tare da aminin kakansa tsoho Sulaimanu. Wanda a shekarun baya na ce maka duk duniya daga marigayi Najibullah, sai tsoho Sulaimanu ne suka san maɓoyar ragowar kundi biyun cikin masarautun nan.
ÆŠaya dai na san yana cikin masarautar nan, amma a ina? Ban sani ba, kuma duk shaiÉ—anun aljanun da ke yi mini aiki ba za su iya bayyana inda suke ba..."
"Yaya kamannin Najibullah yake? Haka shi ma tsoho Sulaimanu?"
Murmushi Malami ya yi ya ce, "Amma me kake ci na baka yana zuba Gambo? Ai duk gaggawarar amarya ta bari a kai ta É—aki."
"Sanin a bari ya huce shi ke kawo da rabon wani, ya sa nake son ka yi gaggawar warware mini zare da abawa. Domin ko babu komai za mu aika Dogarai su bincika mana inda suke."
Da yake murmushi ya zama É—abi'arsa, a wannan karon ma murmushi Malami ya yi ya ce.
"Ka gode wa Dogaran da suke farmaki yankin Baɗiya, domin a wani ƙasurgumin dajin da tsoho Sulaimanu ya ɓoye su a can suka farmake su. Idan da hali ma ka ƙara musu matsayi, ungo wannan turaren."
©AMEERA ADAM
*FIRST CLASS WRITER'S ASSO...*
GargaÉ—i: Ban amince a sarrafa mini littafi ta kowacce siga, ba tare da izinina ba. Yin hakan yana iya kai wa ga matakin Hukuma, don haka a kiyaye.
Tsokaci: Daga Masarautu, Sarakuna da sunayen yanki duka ƙirƙira ne. Idan ya yi daidai da labarin wani/wata arashi ne.
SHAFI NA ÆŠAYA
DAULAR JABAL
Shekara ÆŠari Biyu Baya (1825)
Daular Jabal ta kasance ƙasaitacciyar daula, da ke ɗauke da dubban al'umma. Sunan Jabal ya samo asali daga yawan tsaunikan da yankin yake da su, mafi yawa suna zagaye da daular bakidaya. Daular Jabal tana kewaye da tekun Farjum, wanda yake da tsofaffin tarihi mabambamta masu cike da ban tsoro zuwa almara. Yankin yana ɗauke da tarin ƙabilu, waɗanda suke da bambamcin harshe a ƙalla sama da ɗari. Kuma yanki ne da yake da tarin arziƙin noma, kiwo da kasuwanci.
Tsaunin Jaddum shi ne katafaren tsaunin da ya fi kowanne tsauni girma a Daular Jabal, kuma tsauni ne mai matuƙar tsoratarwa da munanan al'amura suke faruwa a kansa. A labarin kunne ya girmi kaka, an ce a shekarun da suka gabata. Tsaunin matattarar wata ƙabila ce ta Gussum, wasu kuma suka ce sunan ƙabilar Hadira. Waɗannan ƙabilu da ake tantama a kansu, an ce sukan yanka duk jaririya macen da aka haifa ranar Alhamis, su shayar da jininta ga abin bautarsu da ke jingine a jikin tsaunin. Da matar shugabansu ta haihu a ranar Alhamis, sai suka nemi da a yanka jaririyar. Shi kuma Shugaban ya yi tsalle ya dire a kan hakan ba za ta kasance a kan jininsa ba, kuma da yake ya fi su ƙarfin dukiya da iko sai suka haƙura. Tun daga ranar, duk wanda ya hau kan tsaunin sai dai a ga ƙoƙon kansa ya gangaro ƙasa ya faɗi, kuma ba za a sake ganin gangar jikinsa ba.
Wasu kuma suka ce, bayan da aka yi wa shugabansu haihuwar mace ranar Alhamis. Da labarin ya bayyana, bai yi sallama da kowa ba ya tattara iyalinsa da jaririyar da aka haifa suka bar garin. Tun daga wannan ranar suke fuskantar mummunan hukunci ga duk wanda ya hau kan tsaunin da sunan bauta, domin abin bauta ya yi mummunan fushi da su.
Sai dai duk yawan tarin addininan da ke cikin daular, manyan addinai uku ne suke da tasiri a cikinta. Addinin Musulumci, addinin Kiristanci da kuma addinin gargajiya.
Addinin Musulumci
Addinin Musulumci addini ne da Musulmai suke bauta wa Allah Shi kaɗai, ba tare da waninSa ba. Wanda musulmai suke bin doron koyarwar Annabi Muhammad (S.A.W), wacca take ƙunshe cikin littafi mai tsarki (Alƙur'ani) da Allah (S.W.T) Ya yi wa Annabi Muhammad (S.A.W) wahayi, ta hanyar Mala'ika Jibrilu. Tare da bin Hadisansa, waɗanda suke tafe da sunnar yin aiki kyakkyawa da guje wa saɓon Allah.
Addinin Kiristanci
Addinin Kiristanci, addini ne na kiristoci da suke bautar Yesu Almasihu. Wanda mabiyansa suka ce yana koyar da ƙauna, gafara da aminci. Kuma sun yi imani da an gicciye Yesu, har ya tashi daga cikin matattu bayan kwana uku sannan ya hau sama. Kiristoci suna amfani da littafin Bible, daga rubutu daban-daban a cikin harsuna kamar Ibrananci, Aramaic da Girkanci.
Addinin Gargajiya
Addinin gargajiya, addini ne da mabiyansa suke amfani da koyarwar abubuwan bauta tun daga kan iyaye da kakkanni. Sun yi imani da tsafi, bokanci, sihiri da camfe-camfe, musamman a wasu ƙayyadaddun abubuwa kamar wurare, ranaku da sauransu. Addinin gargajiya, yana da bambamci da addinin Musulumci da na kiristanci. Saboda mabiyansa suna da abubuwan bauta kala-kala, wasu sukan bautawa ruwa, wuta, dutse, gumaka, rana, bishiya, kabari da sauransu. Kuma sun yi imani da taimakon aljanu, tare da ruhin kanninsu da suka gabata. Haka zalika ba su da littafin da suka amfani da shi a wurin bauta.
Sai dai kuma a Daular Jabal an samu dubban mabiya addinan gargajiya, sun yi haɗuwar tsintsiya wurin samar da littafi guda. Wanda aka sassaƙa bangon jikinsa da fatar wata tsohuwar damisa, wanda suka ajiye sirrikan kiran aljanu da kirarinsu. A silar haka ne aka samar da kundi ukun da mabiya addininan yankin suke amfani da shi. Sai dai kuma wani al'amari da ya faru a waɗansu shekaru ya sa bayyanar Kundin ke barazana, cimma buri da jefa kokonto a zuciyoyin Sarakuna ukun da ke rayuwa a cikin Daular.
Masarautar Kajjura (Sarki Gambo)
Masarautar Judala (Sarki GiÉ—aÉ—o)
Masarautar Zulwara (Sarki Dikko)
Sune masarautu da sarakunan da ke kewaye da Daular Jabal, kowannensu yana shimfiɗa mulki cike da isa, ƙasaita da izzar mulki. Domin gabaɗaya duka sarakunan babu wanda yake ga maciji da ɗan'uwansa, ba don komai ba. Sai don wasu munanan al'amura da suka gifta a tsakaninsu a lokautan da suka shuɗe.
MASARAUTAR KAJJURA
Zaune yake a kan lallausar kujerar da ta ƙayatu da kayan alatun gidan sarauta, fadawan da ke zagaye da shi gabaɗaya kawunansu a sunkuye yake suna jiran umarninsa. Daga gefe Shamaki ne ya sake russunar da kai, har zai fara magana. Daga jikin bangon gabas, suka ga fatar zakin da ta sha ado mai ɗauke da rubutun tsafin masarauta ta dare gida biyu. Kakkaifan takobi, kuma tsafaffan da ke saƙale a jikin fatar ta fitar da kanta daga cikin gidanta. Kamar walƙiya haka ya yi tsalle ta dira a daidai maƙoshin Sarki Gambo, duk yadda ya so matsawa sai ji ya yi ya manne da jikin kujerar da yake zaune.
Da ido ya dubi fadawansa domin su kawo masa ɗauki, amma ga mamakinsa sai ya ga sun bushe da dariyar ƙeta. Yana cikin wannan yanayin ya ga farin dattijon ya ratso daga bangon da ya dare. Ya ƙaraso gabansa yana sakin murmushi, kafin Sarki Gambo ya yi wani yunƙuri tsohon ya saka wannan takobin ya datse kansa ƙasa.
Firgigit! Sarki Gambo ya tashi zaune a razane daga mummunan mafarkin da ya yi yana shafa wuyansa, gumi ya shiga keto masa cikin tashin hankali.
"Allah Ya taimake ka, Allah Ya ba ka yawan rai..."
"Fulani akwai abin da yake shirin faruwa."
Sarki Gambo ya katse matarsa cikin damuwa, ajiyar zuciya Fulani Sadiya ta sauke ta ce.
"Ina fatan wannan ya kasance tuntuɓen fahimtarka ne ranka shi daɗe."
Bai amsa mata ba, ya miƙe jiki babu ƙwari. Don haka ita ma ta miƙe fuska ɗauke da damuwa ta ce.
"Ranka shi daÉ—e ina za ka je a tsohon daren nan?"
"Zan je na ga Malami!"
Ya furta mata yana naɗe fuskarsa da baƙin ƙyalle, cikin shigar ɓatar da sahu. Ganin har ya je bakin ƙofa ya sa ta bi shi da sauri ta ce.
"Amma ranka shi daÉ—e me zai hana ka bari zuwa safiy..."
"Idan har muka kai wannan lokacin, mummunan abu zai iya faruwa da mu. Kin san Bahaushe ya ce, da zafi-zafi ake dukan ƙarfe."
Ya furta yana fita, ba tare da ya waiwayo ta ba. Ta ɓoyayyar ƙofar da ke cikin ɗakin ajiyar kayan sirrinsa ya shiga, yana tafe cikin duhu yana haskawa da itacen da yake ci da wuta har ya ƙarasa. A bakin bukkarsa ya tsaya, sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya kutsa kansa cikin bukkar.
Kamar bai ji motsinsa ba, haka Malami ya cigaba da shafa yashin da ke kan faifan gabansa. A gefensa Sarki Gambo ya zauna, bayan da Malami ya ƙarasa sannan ya dube shi ya ce.
"Tun da na ganka da kanka ba aike ba, na san banza ba ta kai zomo kasuwa."
Sarki Gambo ya warware rawanin fuskarsa sannan ya ce.
"To ai zuwa da kai ya fi saƙo ne Malami, kuma tun da kuka gan mu yanzu ai kun san akwai gagarumar matsala."
"Ita na kwana ina duba maka, domin niyyata zuwa safiya na zo har ɗaki na same ka da maganar." Malami ya furta yana tsare Sarki Gambo da ido, cikin ƙaguwa ya ce.
"Amma me yake faruwa malami? Haka kuma muna fatan wankin hula ba zai kai mu dare ba."
"Najibullah Bn Muhammad Bn Najibullah Dogaran bulukiya!"
Jin sunan da Malami ya ambata ya sa Sarki Gambo miƙewa zumbur! Nan take jikinsa ya shiga karkarwa kamar wanda ya ji kiɗan gangi.
"A wayewar garin gobe jinin Najibullah wato Najibullah zai shigo masarautar nan, kuma idan har ba ka dakatar da shi ba shukar da ka jima da binnewa za ta bayyana. Domin zuri'arsa za ta bankaɗa maka labulen sirrin da babu wanda ya san da shi daga ni sai kai sai amintacciyarka." Malami ya ƙarasa maganar yana kallon Sarki Gambo, kamar zai yi kuka sarki ya dafa gwiwoyin Malami ya ce.
"Don girman Allah, da matsayin abin bautar da na fi aminta da ita ka taimaka mini Malami." Murmushi ya yi masa ya ce.
"Zan taimaka maka Gambo, kamar yadda na rife sirrin addinin da kake bautawa, saɓanin na Musulumci da kake yaudarar talakawanka da shi." A fili Sarki Gambo ya sauke ajiyar zuciya yana lumshe ido, Malami ya cigaba da cewa.
"Lokacin tashin alƙiyamarka ya zo Gambo, matuƙar ba ka hallaka jinin Najibullah ba. Kuma lokacin mallakar Kundi ukunka ya bayyana, domin kuwa Za a kawo Najibullah tare da aminin kakansa tsoho Sulaimanu. Wanda a shekarun baya na ce maka duk duniya daga marigayi Najibullah, sai tsoho Sulaimanu ne suka san maɓoyar ragowar kundi biyun cikin masarautun nan.
ÆŠaya dai na san yana cikin masarautar nan, amma a ina? Ban sani ba, kuma duk shaiÉ—anun aljanun da ke yi mini aiki ba za su iya bayyana inda suke ba..."
"Yaya kamannin Najibullah yake? Haka shi ma tsoho Sulaimanu?"
Murmushi Malami ya yi ya ce, "Amma me kake ci na baka yana zuba Gambo? Ai duk gaggawarar amarya ta bari a kai ta É—aki."
"Sanin a bari ya huce shi ke kawo da rabon wani, ya sa nake son ka yi gaggawar warware mini zare da abawa. Domin ko babu komai za mu aika Dogarai su bincika mana inda suke."
Da yake murmushi ya zama É—abi'arsa, a wannan karon ma murmushi Malami ya yi ya ce.
"Ka gode wa Dogaran da suke farmaki yankin Baɗiya, domin a wani ƙasurgumin dajin da tsoho Sulaimanu ya ɓoye su a can suka farmake su. Idan da hali ma ka ƙara musu matsayi, ungo wannan turaren."