← Book details Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 43

Sashe 30

Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Salisu ya rike dariyarsa. “Toh shikenan ina fata dai duk randa kaji wani ya dauke ta ba zamu kwantar da kai a asibiti ba.”

Mukhtar ya harare shi. “Bansan raini wallahi shiyasa ma tun farko naki yin shawara da kai.”

Salisu ya make kafadarsa. “Dalla wasa nake. Tashi ka raka ni naje na zuba wa Maryama karatun yau. Kasan sai anayi ana nuna jajircewa.”

Suka fito tare suna tafiya. “Amma wai Salisu da gaske dai ba zaka nemi sana’a ba? Don’t think of it the wrong way. In har sonta kake yakamata ace kana da plan na aurenta.”

Maganar Mukhtar ta sanya a karon farko jikin Salisu yayi sanyi. Shiru yayi har suka karasa layin gidan bai tanka ba. Sai dai suna neman yaron da zai kira musu ita ne mahaifinta ya fito. Kafin kace kwabo, Salisu ya sulale ya arce. Mukhtar ya juya ya kalli gefensa ya hangi dattijo. Da suari yabi bayan Salisu yana tuntsurewa da dariya.

Sai da yayi da gaske ya kamo shi.

“Haba maza, wannan yawa ne.” Salisu ya sosa keya yana nema ya maze. Amma ganin dariyar Mukhtar ba zata tsaya ba ya sanya ya hakura.

“Kuma wallahi idan naji maganar nan a wani wuri sai nayi balangu da kai.”

“Yi hakuri jarumi.”

Salisu ya sha kunu. “Kai wai baka lissafi ne? Yanzu in yace in turo fa ya kake so nayi bayan kasan ban shirya aure ba. Balle kuma ya bincika yaji bana aiki.”

Mukhtar ya gyada kai cike da jin dadin yadda abun ya kasance. Ko babu komai Salisun zai nemi abunyi. In baiyi don Allah ba ko iyayensa, yanzu zai yi saboda soyayya.

Ko da suka koma hanya, gida Salisu yayi. Kana ganinsa ka ga tashin hankali da damuwar da yake ciki. Mukhtar ya mishi sallama sannan shima ya koma gida da Rashida a ransa.

Sana’a rufin asiri ce ga kowa komai kuwa kankantarta. Mutum bai san ta ina Allah zai buda masa ita ba. Ga Innar su nan yana kallo. Albarkar dake sana’arta ce ta taso dasu dukkan su har ma suka zama abun kwatance.

Dole Rashida ta dauke ta a matsayin abun koyi ba ta zauna tana ta mita ba. Sosai yake so ya sake kebencewa da ita ya nuna mata muhimmancin sana’ar da yake so tayi. Ba wai don Nura ba kadai. Don kanta. Shima Nuran zai je ya same shi ya nuna masa sai ya zama namiji zai samu daidaito a cikin gidansa. Zaman gidan da yake kullum ba mafita bace a gareshi saboda kullum Rashida zata ganshi ne ta kara raina shi.

Tabbas yana tausayin ta da yadda rayuwarta ta koma amma yafi ganin lefinta.

*****

Safiyar ranar da zafi aka tashi hakan yasa ko wannen su ya fito tsakar gida aka shimfida tabarma ana fifita tun bayan asuba. Yaran Rashida kuwa suna can gefen bishiya suna wasa bayan Juwairiyya ta yi musu wanka don suji dadi su ma.

Mukhtar ya kalli lokaci a karamar wayarsa sannan yace, “bari na sake wanka na tafi aiki.”

Mikewar sa ke da wuya, Hajarah da Juwairiyya suma suka tashi suka tafi dakin su don shirin tafiya makaranta.

Inna ta kalli Rashida dake kishingide tana gyangyadi tace,

“Rashida ki tashi muyi magana.” Tana goge idonta ta zauna ta bata fuska.

“Komai na duniya da kike gani hakuri ake dashi. Sannan ita rayuwar nan cike take da kalu bale da jarrabawa kala kala. Na sani ke da Nura kuna son junan ku har gobe, saboda haka bai kamata ace kun bari sauyin rayuwa ya jawo tangarda a rayuwarku ba. Dukkaninku masu laifi ne. Kinji dai fadan da na miki jiya…”

Hawaye suka zubowa Rashida. Ita sam ba haka taso ba. So tayi a nuna masa tafi karfin sa. Amma sanin halin Inna yasa bata tanka ba ta gyada kai.

“Shi raini da bakaken maganganu da kika dauka babu ranar da zasuyi miki. Mijinki shine shugaban ki saboda haka ki zama mai hakuri dashi a ko da yaushe. Na sani, zaman babu bai da dadi shiyasa akace miki ki nemi abun yi, zaki rage jin radadin babun.”

Rashida ta sake goge hawayen da yake ta faman zarya a kumatun ta.

“Mukhtar ya kira Kawu jiya kuma sunyi magana da Nuran. Anjima kafin azahar zai zo ya dauke ki ku koma. Dan Allah ki dinga godewa Allah akan duk abunda ya same ki.”

“Inna wallahi ina kokari na.”

Inna ta tashi. “Na sani, ki kara akan wanda kike, wataran sai labari. Muje mu daura karin kumallo.”

Kafin Rashida ta amsa Inna ta tuna abu tace, “kuma don Allah kazantar nan da kika dauka ki jefar da ita a hanyar komawar ki. Tashi ki wanke kan na kitse miki shi.”

A kace ko wanni mutum yaro ne a gaban mahaifan sa. Sai gashi Rashida ta tashi ta wanke kanta inda Inna ta kitse mata kan tsaf, tayi wa yarta ma. Bayan kowa ya bar gidan kuma Inna sun kammala gyare gyare sai ga Nura yazo. Da fara’ar sa ya shigo alamun son ta yana tare da shi kamar ko yaushe.

Ya zauna Inna ta hada su biyun ta kuma yi musu nasiha akan muhimmancin hakuri da karbar kaddara duk yadda tazo wa bawa. Nura ya yi mata godiya ya kama hannun yaran ya koma waje yana jiran Rashida.

Inna ta debo kwano daya na shinkafa da wake danye da wasu kayan abincin ta mikawa Rashida. “Gidan ki shine garkuwar ki. In kin yi da kyau kiga da kyau. Kije, Allah ya muku albarka. Mukhtar zai zagayo miki in an musu albashi.”

Rashida idonta ya cika da kwalla. “Nagode Inna.” Da haka ta fita daga gidan tana jin nauyin da ta shigo da shi gidan yana raguwa.

Tana fita taga Nura tsaye yana magana da yaran. Yasa su gaba suka fara tafiya don samun abun hawa.

****

Yau cike da farin ciki ya tashi ji yake tamkar ya janyo ƙarfe uku domin ya tafi gidan su Hafsa sosai yake missing ɗin ta, Kasancewa yaji sauƙi sosai yasa shi tashi da niyar komawa koyarwar da yake mata, ta ko ina ya yi missing ɗin yarin yar, bayan ya karya ne ya hau duba kayan da zai sa, muryar ta ce ta dawo kunnunwan sa a lokacin sa ya sanya ƙananan kaya "Uncle kayi kyau" tamkar a lokacin ta faɗa haka ya ji sautin nata, murmushi ya yi tare da ture jakar bakkon da yake sa manyan kayan sa ya janyo ledar da ƙanana suke, shiɗin ba gwanin ƙananan kayan bane, kwata kwata basu fi shida ba, wata blue ɗin riga mai haske ya janyo gami da baƙin dogon wandon sa, baki yasa ya cinge tag ɗin rigar tunda Ibrahim ya nana masa ita ya siya bai kuma bi ta kanta ba.

Aje kayan ya yi a bakin katifar sa wadda ya gyare ta tamkar mace, ɗakin ya share tare da fita ya ɗebo garwashi tare da ɗan turara ɗakin sam Muktar baya son ƙazanta mutun ne gwanin son ƙanshi.

Dariya Juwairiyya tasa lokacin da ya fito riƙe da kasko " kaima dai yaya sai kace wani mace, ni ban taɓa ganin inda namiji ke turara turaren wuta ba sai kanka"

Banza ya mata tare da aje kaskon can gefe ya leƙa ɗakin Inna, ganin ɗakin wayam yasa shi cewa "ina Innar?"

"Ka manta yau ake sunan Balaraba ta je taya su aiki" juwairiyar ta faɗa lokacin da take juya miyar da ke kan wuta, jira kawai take ta karasa ta fita da abincin.

"Kingani ko na manta shaf walllahi, bari ma kawai inna fita in leƙa" ya faɗa tare da yin waje ba tare da ya jira amsar Juwairiyya ba.

Gida ne matsaikaci kai yasa ya shiga bayan ya yi sallama, matan da ke ta faman aikace aikace suka amsa, ɗaya cikin masu ɗaura zoɓo ne ta ce "ah Muntari ashe jiki yayi kyau jiya nake cewa zan komo in kuma duba ka."

Murmushi ya yi "walllahi kam jiki ya yi sauƙi, ina kwana" ya gaishe ta.

"Lafiya ƙalau, to Allah ya ƙara sauƙi" ta faɗa lokacin da ta kamfaci zoɓon ta kurɓa.

"Ina mai jegon?" Ya tambaya bayan ya gaggaishe da matan da ke aiki, daga ciki Balaraba tace shigo mata Muntari, a nutse tare da sallama ya shiga, daurewa yayi dan wani irin ƙamshi ko ƙarni zance ya daki hancin sa, kamshin turaren daban ƙarnin jego daban, a daddafe suka gaisa ya ɗan riƙe Jaririyar na mintina kafin ya bawa mai jegon dubu guda ya taso ya fito.

Ƙarfe biyu dai dai ya dawo sannan ya shirya kafin ya bar gidan su, cike da walwala sam fuskar sa ta kasa ɓoye farin cikin da yake ciki, a ƙofar gidan ya tsaya mintina kaɗan da bugun sa aka buɗe Malam Musa ya fito, ganin Muktar ya washe baki "oh ashe ba'a gama karatun ba, har ina cewa Malan ko sallama"

Murmushi shima Muktar ɗin ya yi "walllahi ba'a gama ba banji daɗi bane sam"

"ayya to Allah ya ƙara sauƙi" Malam musa ya faɗa yana bawa Muktar wuri alamun ya shiga, duru duru ya yi da ido yana tunanin ya za'ai Hafsa tassn ya zo, kamar ance juya suka haɗa idanu da Usman wanda ya fito riƙe da makullin mota da alamu fita zaiyi, ƙarasawa Muktar ya yi suka gaisa.

"Malamin Hafsa ko?" Usman ya tambaya.

Gyada kai Muktar ya yi "eh, Allah yasa dai tana na?"

"Eh tana nan but naji tana cewa zasu fita bari in mata magana" ya faɗa tare da juyawa ba tare da ya jira mai Muktar zai ce ba.

Momy na zaune a falo tana kallo, ganin Usman ta ce "ya kuma ka dawo kasan Hajiya Hasina bata son jira fa"

Zama ya yi kujerar da ke kallon ta, "Dama malamin Hafsa ne yazo nace ba inzo in faɗa miki, dan naji kamar zata fita rannan kuma naji kina cewa an dai na," ya yi ƙarya dan in yace mata Hafsan ta faɗa masa faɗa zatayi mata tace tana kai ƙarar ta gun yaran ta.

"Eh yaron ne, take taken sa basu mun ba"
Chapter 30 · 0% Book details