← Book details Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 43

Sashe 2

Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Malam Adamu mutum ne me zuciyar nema duk da bashi da wadata amma ba’a taba kwana da yunwa a gidansa. Yaran sa kuma suna zuwa makaranta har zuwa lokacin da Allah Ya dauke shi. Mukhtar shine dan shi na fari sai mata hudu reras a kasan sa. Mai bin Mukhtar tun bata shekara ba ta rasu sakamakon cutar kyanda da tayi.

Tun bayan rasuwar malam Adamu a lokacin Mukhtar yana gab da kammala sakandire, sauran yaran basu cigaba da karatu ba. Mukhtar haka zai fita yayi buge bugensa a kasuwa ya samo musu na abinci.

Ganin wahalar tayi wa Mukhtar yawa yasa mahaifiyar tasa ta fara sana’ar saida abinci wadda dama shi ta tashi taga mahaifiyarta tana yi sai dai bayan ta auri malam Adamu sai ya nuna sam baya so tayi sana’a. A yanzu kuwa dole ta kama sai tayi.

Haka dai sukayi ta faman ciyar da gidan har suka aurar da Rashida inda sauran yaran kuma suka koma makarantar gomnati. Zuwa yanzu kuma Mukhtar ya kammala jami’a inda ya karanci civil engineering don ya kasance yana da fasaha da kokari. Yanayin rayuwa da halin da kasarmu ke ciki ya sa yanzu shekarar su hudu da gamawa amma bai samu aiki ba.

Satin da ya gabata ne Inna Kulu taji wata sanarwa a rediyo na wata makaranta da take neman malamai. Sai da ta tabbatar ta haddace bayanan da aka yi. Bayan Mukhtar ya dawo daga kasuwa ne take sanar dashi abunda taji ta kuma karfafa masa gwiwa ya gwada ko za’a dace. Duk da ya na ganin kamar bata lokaci ne zaiyi, haka yaje ya gabatar da takardunsa a makarantar. Jiya kuma aka kira shi yazo yau a musu gwaji.

“Ashe Muntari ba zaka yi sauri ka tafi ba?” Ta fada tana juyowa taga me yake yi.

Murmushi yayi. “Tuwon yayi dadi inna. Yanzu zan tashi.”

Ba tare da tace komai ba, ta dauki murfin rijiyar ta rufe sannan ta samu gefe taja kwanon nata tuwon.

“Allah dai yasa a dace.” Ta faɗa cike da damuwa tana kai loma bakinta.

“Amin Inna.” Ya amsa mata a gajarce yana mikewa. Bakin inda take wanke wanke ya nufa ya tarar duk ta dauraye komai saboda haka shima a take ya wanke kwanon nasa.

A hankali ya dubi tsakar gidan da shi kadai ne abunda mahaifinsu ya bari. Idonsa ya fara kan katangar dakinsa da ta fara zubowa daminar da ta wuce. Sannan ya kalli gefen dakin inna wanda babu ko fitila balle fanka cikinsa. Kafin wannan ma yana bukatar gyara. In sha Allahu da albashinsa na farko zai gyarawa Inna dakinta da yake yoyo.

Yana yarfe hannunsa ya nufa inda ya ajiye jakar sa a kofar dakin su Hajara yana tabe baki.

“Sai yaushe zaki tashi wadancan magunan Inna? Wallabi ki dena shagwaba su.” Ya fada yana shan kunu alamun abun yana bata masa rai.

Dan murmushi Innar tayi sannan tace, “maza maza Allah ya kiyaye ya bada nasara.” Ya san ba zata tanka shi ba shiyasa kawai shima yayi mata murmushin yana mata sallama.

****

Harabar makarantar cike yake da jama’a kamar haɗin baki yau iyaye masu biyan kudi sun cika makil ga kuma mutanen da aka gayyata suzo gwaji. Dukkan su a tsaye suke masu hira nayi masu korafi nayi. Wasu daga iyayen kuma suna ofishin admin suna abunda ya kawo su.

Dai-dai lokacin da Mukhtar ya shiga harabar makarantar yaji zuciyarsa ta harba. Bai san dalili ba, kafin ya ankara kuma sai yaji nutsuwa ta saukar masa. Nan ya sami inuwa ya rakube kusa da wata matashiya ita ma rungume da jakar takardunta ta sha gilas amma fuskarta babu kwalliya. Sallama yayi mata ta amsa da fara’arta sannan suka yi shiru.

Suna wannan jiran ne motar me makarantar ta faka a kofar makarantar. Alhaji Muhammad mutum ne mai karamci da sanin ya kamata. Mutum ne da ya bude makaranta don amfanin jama’a sama da neman kudi domin dan kasuwa ne da yake da rufin asirin sa ba laifi kuma ya kasance likitan ilimi ne.

Kamar ko yaushe sanye yake cikin babbar riga. A hankali ya futo daga motarsa, mai gadi ya taho da sauri duk da ko yaushe sai Alhajin ya dakatar dashi.

“Abba ka jira ni mana…” wata murya ta faɗa a shagwabe.

“Hafsah kenan, kin makarar dani ina sake gaya miki.” Ba shiri ta fisgo jakarta tare haƙura da shan shayin da taso ta shanye kafin ta fito.

Kyakkyawa ce. Duk wanda ya kalle ta haka zai fara cewa game da ita. Ba doguwa bace can can amma ba gajera bace. Sanye take a abaya kalar ruwan goro wadda tayi bala’in yi mata kyau.

Da sauri take tafiya ta kamo babannata da har ya shige ciki. Ba tada kiba shi yasa ma saurin nata yayi kamar gudu take. Kallon lokaci tayi taga takwas dinma bata cika ba Baba yake ta wannan saurin.

Sanda ta kamo shi har ya fara gaisawa da mutanen wajen ya kuma tsawarar akan barin su da akayi ba’a bude musu aji sun zauna ba. Nan take aka bude ajin da za’a musu interview din.

Alhaji Muhammad office dinsa ya nufa tana binshi a baya.

“Ni fa ba zama nazo yi ba Abba. Nima so nake naga yadda kakeyin komai.”

“Hafsah kenan.” Abunda yace kawai sannan yayi magana da principal da wasu malamai da suka shigo suka nufi ajin da za’a yi gwajin.

Lokaci na tafiya, Hafsah tana hammar gajiya don ba ita kadai ba har su Baban sun gaji saboda yadda mutanen suke ta wahalar dasu basu san komai ba balle su cancanta. Ko ita da yanzu ta fara jami’a tafi wasun su.

Ganin saura mutum biyu yasa tayi hakuri ta zauna. Ita ma biron ta a hannu bata yadda ba sai grading take.

Wata macece me gilas ta fara magana. Kaf cikin jama’ar babu me kwazon ta. Anan take Hafsah ta sa a ranta an samu malamar wannan subject din. Ganin ita kamar ta gama nata aikin yasa ta jawo wayarta ta fara dannawa tana dora selfie din da tayi a snapchat.

Tunda ya fara magana abu ɗaya Hafsah taji duniyar ta dakata.

“Sunana Mukhtar Adam.” Duk wani abu da yace bayan nan bata ji shi domin ta faɗa wata duniyar daban, ta shagala da kallonsa tana yabonsa a ranta. Ta nutse a duniyar da ya kaga ba tare da ya sani ba, da muryarsa.

Wannan shine mafarin labarin su. Kafin ta fahimci hazakarsa, haibarsa ta fahimta. Kafin ta gane me kokari ne, sai da ta gane me kyau ne. Kafin ta gane ya hadu, sai da ta rasa hankalinta, sainda zuciyarta ta fara kitsa mata wani abu akansa. Wani abu da a lokacin bata san menene shi ba.

Ta so ace, zamanta tayi a gida a wannan ranar!
**************

Jiki ba kwari Hafsa ta bi shi da kallo lokacin da ya bar ajin,idanunta ta maida kan takardar da sunayen masu neman aikin ke kai Muktar ta kuma mai-maitamana, murmushi ta yi kafin ta ja biro jikin sunan nasa kamar yadda ta yiwa matashiyar matar ɗazu alamar ya ci interview ɗin.

Ahankali ta miƙe tana duba agogo kafin ta miƙawa Malamin da suke interview ɗin tare, wanda ke kusa da ita bari in je gun Abba, karɓa kawai ya yi ba tare da ya ce komai ba, bata damu da rashin maganar tasa ba ta bar ofishin.

Har ta wuce ta dawo, fuskar ta ɗauke da murmushi "lah Anti ina kwana?" ta faɗa cikin har shen turanci matar ma murmushi ta mayar mata, "kyace ina kwana mana, anya Hafsa? ace tunda kukai candy ko a ɗan leƙowa a gaisa," matar ta mayar cikin turanci.

"Kai Anti wallahi abububuwa sukai yawa, kuma gani na na yi in nazo ai duk kuna aji zan ɗauke muku hankali, anma ai ina cewa Abba ya gaisar mun da ku."

"Eh fa ya na faɗe wataran, bari in je sauri nake Hafsa ta faɗa"

" nima kin ga aji zan shiga" matar ta fada kafin ta yi gaba.

Abba na zaune yana duba takardu Hafsa ta shigo da Sallamar ta, ɗagowa ya yi yana kallon ta kafin ya ce "to sarkin rikici badai nufin ki anan zaki zauna ba?," girgizar kai ta yi a'a tafiya ma zan yanzun nan naga an mana fixing class 2-4 gwanda in je.

"Towo class kuma gashi ni yanzu ina som mu tattaunawa da team ɗin da sukai interview ɗin, dan mu samu mu a turawa waɗan da suka samu nasara sakon kar ta kwana zuwa gobe su fara zuwa, musanman wanda zai ɗauki Physics ɗin nan."

"Tom shikenan kawai bani kuɗin ɗan sahu da na ƙara masa 200 a kan normal price zai kaini, dan innace sai driver ya zo kaini zan makara."

Dubu Uku Abba muƙo mata "Allah ya bada sa'a," murmushi ta yi "Amin sunma yi yawa ai, Allah ya saka da alkairi" ta faɗa kafin ta wuce.

A nitse Muktar yake tafiya tun da ya baro ɗakin gwajin ya kasa tunanin hukuncin da mutanen zasu yanke tsaf ya tsaya dan naƙaltar su sai dai fuskokinsu ba su nuna sun yi maraba ko akasin haka da jawabin da ya gudanar ba, duda cewa shi a ransa yana jin kwarin gwiwar ya yi abin da ya da ce ko da bai samu Malamin senior ba to su ɗauke shi a matsayin malamin primary.

Har ya wuce mai lemon ya dawo soyayyar Umman sa da lemo mai ɓawo yasan ya bazai iya ganin lemo ya wuce bai sai mata ba, Ɗari biyun sa kenan, "na ɗari za'a bani" ya faɗa a takaice, Baba Yakubu ne ya yi miƙo masa bakar ledar kai dai Muntari kana son siyan lemon ɗari naga randa zaka sai na du ɗari biyun.

Dariya Muktar ya yi, " adai ci gaba da tayamu da addu'a wataran na dubu zan siya," Allah dai yasa ai nima zan so haka.

A kishin giɗe Innan take tana jin radiyo ganin shigowar Muktar ya sata gyara zama, yanayin fuskar ta ya nuna ɗoƙi da son jin labari mai daɗi na an ɗauke shi aikin, ajiyar zuciya ya yi kafin ya zauna kusa da ita ledar lemon ya miƙo mata kafun ya ce "wanne shirin suke?"
Chapter 2 · 0% Book details