Sashe 29
Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Tab mummy ai babu wanda yake da tasiri akan Hafsah sama da ke. Shi waye? Yayi kadan ya sauya mata tunani. Kawai karatu ne tsakanin su shikenan. Na sha kallonsu daga nesa kuma abunda na fuskanta kenan. Kuma tunda anyi sa’a tana ganewa yanzu ai ke abun alfaharin ki ne mummy.”
Mummy ta murza zoben hannunta tace, “hakane kuma. Kawai ina tsoron kar wani abu ya tsarga a zuciyarta ne kasan halin ta da taurin kai yadda naga tana rawar jiki in yazo.”
“Watakila rawar jikin ma duk dan saboda tayi karatun ne ta burge ki. Kaf gidan nan babu wanda yake kokarin ya burge ki sama da Hafsah. In muka zauna kullum zancen ta kenan saboda mummy.”
Mummyn taji dadi. Take zuciyarta tayi wasai. Itama duk da basa jituwa da Hafsahn daban take jinta a ranta kamar yadda take jin Sadiq din daban. Shi kadai ne yake iya kwantar mata da hankali akan kowa. A take ta dauki maganar sa.
“Toh zan duba in sha Allah.”
Bai amsa ba Hafsah ta shigo tana ajiye tray din a gabansa.
“Kuma wallahi nafita iya abinci.. ci kaji!” Suka kwashe da dariya.
Mummy ta kurawa Hafsah ido sai taji wata kwalla ta taho mata. Ta maida ta sannan tayi murmushi gami da mikewa ta bar falon ta bar su suna musu.
******
Jikin Mukhtar yayi kyau don har ya tashi ya koma aiki ma. Yamma ce lis yana ta faman wanki yaji sallama. A zabue ya juya saboda jin muryar wadda take sallamar. Suka hada ido da Rashida da yaranta biyu dukun dukun dasu kamar yan gudun hijira. Ya kalli gefenta yaga Ghana must go. Gaban sa ya fadi. Ba dai ta kaso auren ba?
Tsame hannunsa yayi daga wankin yana amsa sallamar su ita kuma tana karasa shigowa.
“Ban dari biyu dan Allah na bawa dan iskan nan.” Ta roka. Mukhtar yaji takaici ya cika masa zuciya amma ya ciro ya bata inda ta fita ta wullawa me adaidaitar gami da yin tsaki sannan ta dawo cikin gidan tana mita.
“Aikin banza. Ya dauka dari biyun wata abar arziki ce.” Mukhtar ya bita da ido har ta shige dakin inna ta dire kayan nasu sannan ta fito.
Ya matsa zai dauki yaronta yaji zarnin fitsari ya doki hancinsa.
“Fitsari yayi?”
Ta tabe baki. “Bar shegen yaron nan mana a hanya ya sakar min shi kamar baida baki.” Ta talle keyarsa ai kuwa ya tsala ihu.
Mukhtar ya ja shi gefe yana tafiya dasho bakin rijiya. Ya cire masa kayan ya dauraye masa jiki yana jinjina kazantar Rashida da yadda gabaki daya ta chanza daga kalamai har dabi’u. Bai taba sanin cewa inda mutum yake zaune nada tasiri gameda yadda zai yi rayuwarsa ba sai akan Rashida. Ya dauka sanda tayi aure tayi girman da babu wani abu da zai chanja mata halaye.
Da yake ana rana sosai ruwan da ya yiwa yaron wanka yasa yaji dadi har gyangyadi ya fara. Rashida dai sai kallonsa take tana tabe baki. Har ya gama wankin, ya shinfidawa yaron dadduma gami da lullube shi da zanin Inna kafin kayan su bushe bata ce uffan ba.
Sai da yaron ya fara minshari ta kalle shi. “Sai katon kai kamar na uban sa.”
Mukhtar ya samu wuri ya zauna. “Wallahi Rashida ki gyara hali.”
Ta murguda baki. “Ina Inna?”
Sanin halinta yasa ya bata amsa. “Ta fita. Su Hajara suna Islamiyya yanzu zasu shigo.”
“Toh ai gwara dai su dawo don abunda yake damuna mace ce kadai zata fahimta. Mazan nan duk halin ku daya.” Ta tofar da yawu a gefenta sannan ta mike.
“Bari na zagaya.”
Mukhtar yabi bayanta da kallo yana ji kamar yayi kuka. Wannan wace irin rayuwa ce ta daurawa kanta? Bata jima ba ta dawo.
“Ba wani abun jefewa bakin salati ne?”
“Bakin zagi dai.”
“Me kace?” Ta fada tana lekawa kicin din Innar ko zata samu abu. Mukhtar ya mata shiru bai ce komai ba har ta samu wuri.
“Wai yanzu yaya ba zaka tambayeni me aka min ba?” Mukhtar ya tabe baki.
Sallamar su Hajara yasa yayi hamdala sannan ya mike yana barin gidan cike da bacin ran da duk randa ya ganta sai ta cusa masa. Shi kenan da yake dan uwanta bare kuma mijinta.
****
Tunda suka shigo suka gaishe ta sukayi daki don su chanja kaya, Hajara ta yatsina fuska tana kallan Juwairiyya. "Wai me ya kawo ta?" Juwairiyya ta watsa hannu gefe alamun bata sani ba. Ita kuwa Hajara sai haushin yayar duk yabi ya cikata da yake daman sakuwar ta ce ga fada, ga kazanta. Yanzu Inna sai tace daki daya zasu kwana wanda babu yadda zatayi. Amma in akace kwanan zatayi, wannan karan sai dai ita ta dinga kwanan tsakar gida. Gwara taji da sauro da taji da aikin gyaran fitsarin kwance na yaran Yayar.
Hajara ta linke hijab dinta sannan ta daura zani tana tunanin me zai kawo yayar tasu gida. Ita kuwa Juwairiyya kawai daga labulen dakin tayi ta fice ba tare da ta bata amsa ba.
Kusan a tare suka nemi wajen zama kusa da ita suna zama. "Sannu da zuwa Yaya, ya gidan?"
Juwairiyya ta tambaya tana kallon fuskar yayar wadda duk ta fada.
"Hnmm ya akurki zaki ce min dai. Wannan wajen har kya kira shi da gida? Allah na tuba ba gara kwanan bakin titi ba." Yarinyar ta ta zuba mata ido kamar tana so ta fahimci me uwar tata take fada. Juwairiyya ce ta lura hakan ya sanya ta kama hannun yarinyar.
"Muje in miki wanka..." da haka ta bar wajen ta barsu da Hajara dan ita ba zata iya tankawa yayar ba.
Hajara ta tabe baki. "Toh me kike nufi yaya?"
Rashida ta sosa kai har dan kwalinta yana zamewa gefe wanda yasa Hajara ta lura da tsohuwar kalbar dake kanta. Hajara ta kalle ta da mamaki kamar yadda Mukhtar yayi mamakinta. A gidan ita da Hajara sune yan gayu da kwalliya kuma ba abunda yake hana su yi. Ko rashin lafiya take sai tayi kwalliyar nan. In bata da kudi kuwa a cinikin Inna take sayar hoda da turare dan zubi.
Kullum tas take amma sai gashi lokaci guda ta rikide. Dole ma tayi nesa da aure yanzu.
"Yaji nayi. Ai wallahi ba zan koma ba sai anyi magana da shi. Ace mutum ba ci ba sha kullum sai dai ya dimama katifa?"
Hajara ta sake tabe baki. "Toh dama ai kinsan baya aiki."
"Ai da yana nema yanzu kuwa bacci yasa gaba. Ni wallahi ba wahalalliya bace. In ya ga zai gyara toh, in ba zai gyara ba wallahi yazo ya debi yaransa ya bar takarda ta na kara gaba. Ai da saura na."
Hajara ta zuba mata ido. Bakinta yayi nauyi ta rasa abun fada duk haushin yadda Rashida ta zama ya cikata. Ta cigaba da kallonta har ta mike ta dauki buta.
Ta kalli gefe taga yaronta yana bacci har yanzu. A nan take ta lula duniyar tunani. Garba yana da sana'a, shin watarana haka shima zai daina? Shin haka rayuwarta zata koma ita ma? Tab di jam. Ai wallahi ita sana'a zata nema. Ba zata iya zaman wahala ba. Ba zata yarda ta yarda wannan kwalliyar a gidan su ba. Ta ja numfashi saboda nauyin da taji zuciyarta tayi. Tana son Garba, amma bata son rayuwar talauci ko zaman kauye. Bata son ya dauke ta ya kaita nesa. Dole ma ta masa magana tun yanzu suyi yarjejeniyar inda zata zauna.
Rashida ta tako a hankali tana shafa cikin ta wanda babu tsammani ta dauke shi. Ta ja tsaki sannan ta sake zama.
"Wai Inna ba zata dawo bane?"
Hajarah ta murmusa. "Dawowarta kam sai bayan Isha. Gidan Kawu taje." Su ka danyi shiru na wani lokaci ko wannen su da abunda yake sakawa aransa.
“Yaya wai auren ba dadi ne? Duk soyayyarki da Nura ina ta tafi?”
Rashida ta tabe baki. “ Wace soyyaya kuma babu kudi. Ai wallahi duk yadda zakiyi kiyi aure gidan kudi. Nima kaina sai da mukayi auren naga duk wasu kadarori da yace yana da ita karyace. Kinga kuwa dole ma na kaso auren nan yasin. Ya nemi yar wahala irin sa.”
Sallamar Mukhtar ta saka Hajarah ta hadiye amsar da zata bayar. Har ya shigo da ya zauna gefen su da yar ledarsa a hannu ya ajiye basu sake cewa komai ba.
“Oh har yanzu bacci yake? Ga biscuit na siyo musu.”
“Kai yaya ni kuma me ka kawon?” Ta tambaya tana daukar ledar. Kan ya amsa ta dauki daya ta bare.
Hajara ta kalle ta ta mike. Ta bar wajen kanta cike da tunani kala kala.
“Kinsan wannan zaman ba zai yiwu ba ko Rashida. Ya kamata ki nemi sana’a ki rufawa iyalinki asiri.”
Ta juya keya tana magana kasa kasa. “Ni fa wallahi yaya gara kawai ya sake ni.”
Mukhtar ya sake jinjina al’amarinta. “Nan fa kika ce in ba shi ba sai rijiya.”
“Da ake ma magana yanzu kuwa wallahi kamar sartse nake jin sa a zuciyata.”
Mukhtar ya furzar da iska. “Allah ya gyara. Ke dai na baki kwana daya kiyi tunanin sana’ar da kike son yi na baki jarinta.”
Rashida ta washe baki. Gara dai wasu kudi su shigo hannunta ta samu na siyan tsire tana ci a tsakar gida tana waqen ta na habaici kamar yadda tayi wancan karan da ya bata jari.
“Ba kudin zan baki ba Rashida, don nasan cinyewa zakiyi. Abunda kike bukata zan kawo miki dukka.”
Wayarsa ta fara ringing hakan ya sanya shi ciro ta yaga wa yake kiransa. Salisu ne. Saurin tafiyarsa ya karu sosai sannan ya fice daga gidan ya bar Rashida tana ta mitar yadda shi sam baya goyan bayanta yadda ya kamata. Tana yi tana cin biscuit din da aka kawo wa yaranta ko a jikinta.
*****
“Kar ka zama rago mana, kawai ka sauke nauyin da kake ji a zuciyarta gane da ita tun kafin wani ya riga ka wallahi.” Salisu ya bashi shawara bayan ya zauna a tsakar gidan nasu daidai kofar dakin Salisu.
Mukhtar ya shafa kansa yace, “kai ba zaka gane bane. Nauyinta nake ji wallahi. Kwarjininta yawa ne dashi.”
Mummy ta murza zoben hannunta tace, “hakane kuma. Kawai ina tsoron kar wani abu ya tsarga a zuciyarta ne kasan halin ta da taurin kai yadda naga tana rawar jiki in yazo.”
“Watakila rawar jikin ma duk dan saboda tayi karatun ne ta burge ki. Kaf gidan nan babu wanda yake kokarin ya burge ki sama da Hafsah. In muka zauna kullum zancen ta kenan saboda mummy.”
Mummyn taji dadi. Take zuciyarta tayi wasai. Itama duk da basa jituwa da Hafsahn daban take jinta a ranta kamar yadda take jin Sadiq din daban. Shi kadai ne yake iya kwantar mata da hankali akan kowa. A take ta dauki maganar sa.
“Toh zan duba in sha Allah.”
Bai amsa ba Hafsah ta shigo tana ajiye tray din a gabansa.
“Kuma wallahi nafita iya abinci.. ci kaji!” Suka kwashe da dariya.
Mummy ta kurawa Hafsah ido sai taji wata kwalla ta taho mata. Ta maida ta sannan tayi murmushi gami da mikewa ta bar falon ta bar su suna musu.
******
Jikin Mukhtar yayi kyau don har ya tashi ya koma aiki ma. Yamma ce lis yana ta faman wanki yaji sallama. A zabue ya juya saboda jin muryar wadda take sallamar. Suka hada ido da Rashida da yaranta biyu dukun dukun dasu kamar yan gudun hijira. Ya kalli gefenta yaga Ghana must go. Gaban sa ya fadi. Ba dai ta kaso auren ba?
Tsame hannunsa yayi daga wankin yana amsa sallamar su ita kuma tana karasa shigowa.
“Ban dari biyu dan Allah na bawa dan iskan nan.” Ta roka. Mukhtar yaji takaici ya cika masa zuciya amma ya ciro ya bata inda ta fita ta wullawa me adaidaitar gami da yin tsaki sannan ta dawo cikin gidan tana mita.
“Aikin banza. Ya dauka dari biyun wata abar arziki ce.” Mukhtar ya bita da ido har ta shige dakin inna ta dire kayan nasu sannan ta fito.
Ya matsa zai dauki yaronta yaji zarnin fitsari ya doki hancinsa.
“Fitsari yayi?”
Ta tabe baki. “Bar shegen yaron nan mana a hanya ya sakar min shi kamar baida baki.” Ta talle keyarsa ai kuwa ya tsala ihu.
Mukhtar ya ja shi gefe yana tafiya dasho bakin rijiya. Ya cire masa kayan ya dauraye masa jiki yana jinjina kazantar Rashida da yadda gabaki daya ta chanza daga kalamai har dabi’u. Bai taba sanin cewa inda mutum yake zaune nada tasiri gameda yadda zai yi rayuwarsa ba sai akan Rashida. Ya dauka sanda tayi aure tayi girman da babu wani abu da zai chanja mata halaye.
Da yake ana rana sosai ruwan da ya yiwa yaron wanka yasa yaji dadi har gyangyadi ya fara. Rashida dai sai kallonsa take tana tabe baki. Har ya gama wankin, ya shinfidawa yaron dadduma gami da lullube shi da zanin Inna kafin kayan su bushe bata ce uffan ba.
Sai da yaron ya fara minshari ta kalle shi. “Sai katon kai kamar na uban sa.”
Mukhtar ya samu wuri ya zauna. “Wallahi Rashida ki gyara hali.”
Ta murguda baki. “Ina Inna?”
Sanin halinta yasa ya bata amsa. “Ta fita. Su Hajara suna Islamiyya yanzu zasu shigo.”
“Toh ai gwara dai su dawo don abunda yake damuna mace ce kadai zata fahimta. Mazan nan duk halin ku daya.” Ta tofar da yawu a gefenta sannan ta mike.
“Bari na zagaya.”
Mukhtar yabi bayanta da kallo yana ji kamar yayi kuka. Wannan wace irin rayuwa ce ta daurawa kanta? Bata jima ba ta dawo.
“Ba wani abun jefewa bakin salati ne?”
“Bakin zagi dai.”
“Me kace?” Ta fada tana lekawa kicin din Innar ko zata samu abu. Mukhtar ya mata shiru bai ce komai ba har ta samu wuri.
“Wai yanzu yaya ba zaka tambayeni me aka min ba?” Mukhtar ya tabe baki.
Sallamar su Hajara yasa yayi hamdala sannan ya mike yana barin gidan cike da bacin ran da duk randa ya ganta sai ta cusa masa. Shi kenan da yake dan uwanta bare kuma mijinta.
****
Tunda suka shigo suka gaishe ta sukayi daki don su chanja kaya, Hajara ta yatsina fuska tana kallan Juwairiyya. "Wai me ya kawo ta?" Juwairiyya ta watsa hannu gefe alamun bata sani ba. Ita kuwa Hajara sai haushin yayar duk yabi ya cikata da yake daman sakuwar ta ce ga fada, ga kazanta. Yanzu Inna sai tace daki daya zasu kwana wanda babu yadda zatayi. Amma in akace kwanan zatayi, wannan karan sai dai ita ta dinga kwanan tsakar gida. Gwara taji da sauro da taji da aikin gyaran fitsarin kwance na yaran Yayar.
Hajara ta linke hijab dinta sannan ta daura zani tana tunanin me zai kawo yayar tasu gida. Ita kuwa Juwairiyya kawai daga labulen dakin tayi ta fice ba tare da ta bata amsa ba.
Kusan a tare suka nemi wajen zama kusa da ita suna zama. "Sannu da zuwa Yaya, ya gidan?"
Juwairiyya ta tambaya tana kallon fuskar yayar wadda duk ta fada.
"Hnmm ya akurki zaki ce min dai. Wannan wajen har kya kira shi da gida? Allah na tuba ba gara kwanan bakin titi ba." Yarinyar ta ta zuba mata ido kamar tana so ta fahimci me uwar tata take fada. Juwairiyya ce ta lura hakan ya sanya ta kama hannun yarinyar.
"Muje in miki wanka..." da haka ta bar wajen ta barsu da Hajara dan ita ba zata iya tankawa yayar ba.
Hajara ta tabe baki. "Toh me kike nufi yaya?"
Rashida ta sosa kai har dan kwalinta yana zamewa gefe wanda yasa Hajara ta lura da tsohuwar kalbar dake kanta. Hajara ta kalle ta da mamaki kamar yadda Mukhtar yayi mamakinta. A gidan ita da Hajara sune yan gayu da kwalliya kuma ba abunda yake hana su yi. Ko rashin lafiya take sai tayi kwalliyar nan. In bata da kudi kuwa a cinikin Inna take sayar hoda da turare dan zubi.
Kullum tas take amma sai gashi lokaci guda ta rikide. Dole ma tayi nesa da aure yanzu.
"Yaji nayi. Ai wallahi ba zan koma ba sai anyi magana da shi. Ace mutum ba ci ba sha kullum sai dai ya dimama katifa?"
Hajara ta sake tabe baki. "Toh dama ai kinsan baya aiki."
"Ai da yana nema yanzu kuwa bacci yasa gaba. Ni wallahi ba wahalalliya bace. In ya ga zai gyara toh, in ba zai gyara ba wallahi yazo ya debi yaransa ya bar takarda ta na kara gaba. Ai da saura na."
Hajara ta zuba mata ido. Bakinta yayi nauyi ta rasa abun fada duk haushin yadda Rashida ta zama ya cikata. Ta cigaba da kallonta har ta mike ta dauki buta.
Ta kalli gefe taga yaronta yana bacci har yanzu. A nan take ta lula duniyar tunani. Garba yana da sana'a, shin watarana haka shima zai daina? Shin haka rayuwarta zata koma ita ma? Tab di jam. Ai wallahi ita sana'a zata nema. Ba zata iya zaman wahala ba. Ba zata yarda ta yarda wannan kwalliyar a gidan su ba. Ta ja numfashi saboda nauyin da taji zuciyarta tayi. Tana son Garba, amma bata son rayuwar talauci ko zaman kauye. Bata son ya dauke ta ya kaita nesa. Dole ma ta masa magana tun yanzu suyi yarjejeniyar inda zata zauna.
Rashida ta tako a hankali tana shafa cikin ta wanda babu tsammani ta dauke shi. Ta ja tsaki sannan ta sake zama.
"Wai Inna ba zata dawo bane?"
Hajarah ta murmusa. "Dawowarta kam sai bayan Isha. Gidan Kawu taje." Su ka danyi shiru na wani lokaci ko wannen su da abunda yake sakawa aransa.
“Yaya wai auren ba dadi ne? Duk soyayyarki da Nura ina ta tafi?”
Rashida ta tabe baki. “ Wace soyyaya kuma babu kudi. Ai wallahi duk yadda zakiyi kiyi aure gidan kudi. Nima kaina sai da mukayi auren naga duk wasu kadarori da yace yana da ita karyace. Kinga kuwa dole ma na kaso auren nan yasin. Ya nemi yar wahala irin sa.”
Sallamar Mukhtar ta saka Hajarah ta hadiye amsar da zata bayar. Har ya shigo da ya zauna gefen su da yar ledarsa a hannu ya ajiye basu sake cewa komai ba.
“Oh har yanzu bacci yake? Ga biscuit na siyo musu.”
“Kai yaya ni kuma me ka kawon?” Ta tambaya tana daukar ledar. Kan ya amsa ta dauki daya ta bare.
Hajara ta kalle ta ta mike. Ta bar wajen kanta cike da tunani kala kala.
“Kinsan wannan zaman ba zai yiwu ba ko Rashida. Ya kamata ki nemi sana’a ki rufawa iyalinki asiri.”
Ta juya keya tana magana kasa kasa. “Ni fa wallahi yaya gara kawai ya sake ni.”
Mukhtar ya sake jinjina al’amarinta. “Nan fa kika ce in ba shi ba sai rijiya.”
“Da ake ma magana yanzu kuwa wallahi kamar sartse nake jin sa a zuciyata.”
Mukhtar ya furzar da iska. “Allah ya gyara. Ke dai na baki kwana daya kiyi tunanin sana’ar da kike son yi na baki jarinta.”
Rashida ta washe baki. Gara dai wasu kudi su shigo hannunta ta samu na siyan tsire tana ci a tsakar gida tana waqen ta na habaici kamar yadda tayi wancan karan da ya bata jari.
“Ba kudin zan baki ba Rashida, don nasan cinyewa zakiyi. Abunda kike bukata zan kawo miki dukka.”
Wayarsa ta fara ringing hakan ya sanya shi ciro ta yaga wa yake kiransa. Salisu ne. Saurin tafiyarsa ya karu sosai sannan ya fice daga gidan ya bar Rashida tana ta mitar yadda shi sam baya goyan bayanta yadda ya kamata. Tana yi tana cin biscuit din da aka kawo wa yaranta ko a jikinta.
*****
“Kar ka zama rago mana, kawai ka sauke nauyin da kake ji a zuciyarta gane da ita tun kafin wani ya riga ka wallahi.” Salisu ya bashi shawara bayan ya zauna a tsakar gidan nasu daidai kofar dakin Salisu.
Mukhtar ya shafa kansa yace, “kai ba zaka gane bane. Nauyinta nake ji wallahi. Kwarjininta yawa ne dashi.”