Sashe 18
Ko Da So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hayaniyar dake tashi a wajen ta bata mamaki. Ashe dai mutane da yawa sunji labari. Tana bin mutane da ido taji anyi wata kara. Tana kalla taga wata ce ta yanke jiki ta sume, hakan yasa daliban suka yi kanta da gudu har suka bawa Hafsah damar shigewa gaba gaba don ta fi gani.
A kusa da ita wata ta yi ihun murna sannan ta kara wayarta a kunne tace, “baby carryover ta biyu kawai. Alhamdulillah.” Mamaki ya cika Hafsah. Lallai rayuwa wata irin aba ce me mahanga daban daban. Mintina kadan da sula wuce wata ta suma amma ga wata kuma ita murna ma takeyi bata fado da yawa ba. Maimakon ta duba sai ta tsaya nazarin yadda yanayin tunanin mutum ke da tasiri da yadda rayuwa zata zo mishi. In ya dauke ta da sauki, tazo mishi da sauki. In ya dauka da zafi, sai komai yafi karfin sa.
So take ta karfafawa kanta gwiwa kafin ta duba. Nan ta shiga duba reg number din Bilkisu. Ganin babu carryover yasa tayi ajiyar zuciya sannan ta duba GPA din Bilkisun. 3.8. Hankalinta ya kwanta sosai sannan ta duba nata.
Ko da idonta ya sauka akan nata, bata yarda daidai ta gani ba. Ta sake dubawa tana tabbatarwa da cewa carryover din electricity take gani. Take wani gumi ya rufe goshinta. Yatsanta yana rawa ta sauke shi daga notice board din sannan ta sulale daga cikin jama’ar tana jin jiri jiri.
Tafiya take yi cike da heartbreak din faduwa course dinnan tare da kara jin tsanar course din tana shigar ta. Ta rasa menene matsalar. Ta rasa ya zatayi. A gefe guda kuma tunanin yadda zata fadawa Abba take yi tunda yasan an saka musu result din. Hankalinta gaba daya ya tashi don ji take har wani sanyi yana shiga jikinta.
Da kyar ta samu ta karasa motar sannan sula soma tafiya. So take wani ya rarrashe ta. So take wani yace mata that’s not the end. So take wani yace mata its okay to fail. So take tayi magana da wani…
“Ka kaini gida da sauri…” ta fadawa dreban.
Duk da a lokacin ba Bilkisu take so ta gayawa ba, ba ta da zabi sai na kiranta tunda tana jiranta itama taji sakamakon ta.
Tana danna kiran kamar Bilkisun na jira ta dauki wayar. Hafsah ta runtse idonta hawaye na zuba sannan ta samu courage din yin magana. “Result yayi kyau besty. Kina da 3.8 kuma babu carryover…” ihun murna Bilkisu ta tsala sannan cike da farin ciki tace.
“Besty dan Allah wait, bari na gayawa Tariq…”
Hafsah ta sauke wayar sannan ta jinginar da kanta a kan window. Har suka isa gida bata daina tunani ba. Cike da damuwa ta karasa cikin gidan ba tare da tayiwa kowa magana ba. Ko da ta shiga dakinta ma rufo kofar tayi sannan ta kwanta a gefen gadonta ta fara rusa kuka. Sai da tayi me isarta sannan ta tashi ta wanke fuskarta, tayi sallah.
Bayan ta idar ne ta samu nutsuwa sannan ta tuna ma ashe a gidan Goggo take ba gidan su ba. Ko ya akayi ma dreban ya kawota gida ita ba zata iya tunawa ba.
Wayarta ta janyo tayiwa Halimah text tana gaya mata a gida zata kwana.
Har yanzu zuciyarta take ji tayi mata nauyin da sai tayi magana da wani zata samu sauki. A wannan lokacin kuma mutum daya ne ya zo ranta.
Uncle Mukhtar…
************
Ban iskar da aka samu kwana biyu ba tare da anyi ruwa ba yasanya garin yin zafi, wannan yasa da yawan mazan unguwar firfitowa kama daga matasa har dama maginta ko ina ka bi cikin unguwar maza zaka gani wasu bisa bencina wasu bisa tabarmi kowa da abinda yake, can gefen kwata bakin wani kanti bencin su Muktar ne shida abokan sa da suke zaune gefen teburin da Ibrahim ke saida kaza soyayyiya, kilishi, da dambun nama.
Nasir da ya ƙara so wurin ɗauke da katuwar baƙar leda ne ya zauna ƙarshen bencin tare da faɗin "wash! Allah yau na gaji da yawa" Salisu ne ya ɗan leƙo kai "kai dai walllahi ka cika ragon ta in ba haka maine abin gajiya a wannan ƴar ledar da ka ɗauko?"
Hararar sa Nasir ya yi "ai gwamma ni da baki kawai na ce na gaji kai na tabbatar sai dai kama faɗi wanwar"
Muktar ne yasa dariya "kai dai Nasiru baka mutunci mai ka maida Salisun ne?"
Nasir bai bashi amsa ba ya hau fito da atamfofi cikin leda yana faɗin " Haja ce na kawo muku dukan mu nasan kayan aure muke haɗawa"
Ibrahim da ke gaban glass ɗin da kayan sana'ar suke yana zubawa matashin saurayin da ya zo siyan dambun nama da doya ne ya yi caraf ya ce inason jar can zatawa Fiddausi na kyau" ya faɗa yana ninke takardar da ya zuba doya.
Salisu ne ya zuro hannu zai ɗauka Nasir ya yi caraf ya ce "koda bashi bani baka, kuɗi hannu nake bawa marasa sana'a"
" Kut.. wai mai kuka maida ni ne?" Salisu ya faɗa a fusace.
Ibrahim da ya komo ya zauna ne ya ɗauki jar da yace yana so yana ƙara ɗaga ta cikin hasken street light "anma atamfar nan ta yi kyau, bama zan sa a lefe ba gobe zan kai mata, in haɗa mata da kwanukan da tayo min cin cin" ɗan juyowa ya yi ya kalli Salisu mutumina kabi shawarar Muntari ka kama sana'a walllahi"
Banza Salisun ya masa tare da ci gaba da ƙoƙarin kama tasha a radiyon sa.
Nasir ne ya taɓo Muktar da tunda aka fara batun kayan baice komai kan su ba yace " ya mutumina banga kafa ɗauka ba?" Murmushi Muktar ya yi abin ai na masu ƴan mata ne.
Nasir ne ya ɗago wata golden ɗin atamfa ya ɗora kan cinyar Muktar wannan ko fara ko baƙa zata mata kyau ina faɗa ma, kama daina wayancewa ni namiji ne nasan duk nunƙufurcin mutun dole akwai wadda yake ɗan tayawa"
Kallon atamfar da ke cinyar sa ya yi, bai ankara ba zuciyar sa ta fara zayyano masa Hafsa cikin atamfar cikin sauri ya mayarwa da Nasir kan cinyar sa, " aiko kai namijin ƙarya ne tunda dai bakasan da irin mu ba wanda sam soyayya bata gaban su"
Dariya Nasir yasa tare da mayar masa atamfar " ka rantse da Allah babu wadda kake so"
Shiru Muktar ya yi tare da shan kunu, Salisu ne ya zuro kai "ka rantse mana" ya faɗa yana tsare Muktar da idanu.
Tsuke fuska Muktar ya kumayi lokacin guda zuciyar sa na ayyano masa Hafsa yanzu da ya yi tunani mai zurfi ya fahinci bawai iya burgeshi yarinyar kawai take ba, har da ɓurɓushin so duda shiɗin baisan ya son yake ba.
" Sabida mai zan rantse, abinda na sani shine dai kawai ba wanda nake so"
"Wai kana nufin wannan tsuke fuskar zai sa in ƙyale ka," Salisu ya faɗa tamkar da shi aka fara musun tun asali.
"To karma ka kyale ni mana" Muktar ya faɗa, nefa da yaran da ke ɗan wasa tsakanin hanya suka faɗa suna tsalle ya bawa Muktar damar miƙewa bayin Allah sai da safen ku dama zafi ya fito dani"
Nasir ne ya yi saurin miƙewa ya danƙa masa atamfar kaban kuɗin ƙarshen wata," numfashi ya furzar tare da kallon atamfar kamar zai maido masa da ita sai kuma ya juya ya yi gida.
Wutar nefan da aka kawo ta haske tsakar gidan su Inna na zaune tana kwaɓin fanke Juwairiyya na Feraye kabewa yasan ta abincin safen gobe ce yayin da Hajara ke rubutu ya yi sallama kusan dukkanin su suka amsa.
Hajara ta ɗago ne ta ce "lah yaya mai ka siyo?"
Hajara ta tambaya cewa ya yi "Idon matambayi," Juwairiyya tasa dariya inda Hajara ta yi ƙas da kai tana zumɓura baki. Gefen Inna ya aje ledar tare da faɗin "Nasiru ke siyar wa na ɗaukan miki wannan in kalar bata miki ba sai ince ya kawo ki zaɓa"
Da rawar jiki Inna ta buɗe "kai masha Allah, ai ta yi sosai gabaki ɗaya suka faɗa, albarka Inna ta hau sa masa tamkar ya siya mata duniyar nan yayin da shi kuma yake ta faman murumushi da faɗin "Amin"
Ɗakinn sa ya shige yana sauraron Addu'oin da Innar ke masa idanun sa bisa fanka da ke kaɗawa baima san sa'adda bacci ya yi gaba da shi ba.
*****
Tunanin yadda zata iya koyan electricity and magnetism ɗinnan ne duk ya cika mata rai, mafita ɗaya ta faɗo mata shine Uncle Muktar, inda tasan course ɗinnan zata faɗi ɗin da gaske, da tuni tun suna hutu da take zuwa da zaman hira da suke lokacin break da tuni tasa ya fara koya mata, sai dai yanzu babu dama tunda sun koma makaranta, next week zasu fara lectures gobe ko jibi take son siyi handing over da malamar da zata rike ajin da take.
Sam ta rasa mai yake mata daɗi, karatu da BUK ɗin duk tabi ta tsane su, dama ba son Agric ɗin nan take ba, tsaki taja ita dama art take tasan ba za'a bata Agric ba.
Yunwa da ta fara tambayar ta yasa ta miƙewa ta kunna fitilar ɗakin ta dan tunda ta shigo ta yi sallah take kan daddumar bata ko motsa ba tun bayan sakon da ta turawa Aunty Halima, ranta sam babu daɗi ta daure ta fito falon fatan ta kar ta haɗu da kowa har zuwa gobe ta samu ta koma gidan Gwaggo.
Hango ta da Khalil ya yi wanda yake ta fama wasa shida ƙanwar sa khairi ne ya rugo da gudu yana tsalle yana faɗin "Aunty Hafsa shine kika tafi kika barni ko, yau she kika dawo?"
Jin Khalil ya anbaci Hafsan ya sa Abba juyowa " Hajiya Hansatu ashe kina gida?" Daurewa Hafsan ta yi ta ƙaraso.
"Abba sannu da gida" ta faɗa kallon ta yi damuwar da ta bayyana a fuskar ta yasa shi shima damuwa kafin ya ce wani abu Momy ta fara faɗa.
A kusa da ita wata ta yi ihun murna sannan ta kara wayarta a kunne tace, “baby carryover ta biyu kawai. Alhamdulillah.” Mamaki ya cika Hafsah. Lallai rayuwa wata irin aba ce me mahanga daban daban. Mintina kadan da sula wuce wata ta suma amma ga wata kuma ita murna ma takeyi bata fado da yawa ba. Maimakon ta duba sai ta tsaya nazarin yadda yanayin tunanin mutum ke da tasiri da yadda rayuwa zata zo mishi. In ya dauke ta da sauki, tazo mishi da sauki. In ya dauka da zafi, sai komai yafi karfin sa.
So take ta karfafawa kanta gwiwa kafin ta duba. Nan ta shiga duba reg number din Bilkisu. Ganin babu carryover yasa tayi ajiyar zuciya sannan ta duba GPA din Bilkisun. 3.8. Hankalinta ya kwanta sosai sannan ta duba nata.
Ko da idonta ya sauka akan nata, bata yarda daidai ta gani ba. Ta sake dubawa tana tabbatarwa da cewa carryover din electricity take gani. Take wani gumi ya rufe goshinta. Yatsanta yana rawa ta sauke shi daga notice board din sannan ta sulale daga cikin jama’ar tana jin jiri jiri.
Tafiya take yi cike da heartbreak din faduwa course dinnan tare da kara jin tsanar course din tana shigar ta. Ta rasa menene matsalar. Ta rasa ya zatayi. A gefe guda kuma tunanin yadda zata fadawa Abba take yi tunda yasan an saka musu result din. Hankalinta gaba daya ya tashi don ji take har wani sanyi yana shiga jikinta.
Da kyar ta samu ta karasa motar sannan sula soma tafiya. So take wani ya rarrashe ta. So take wani yace mata that’s not the end. So take wani yace mata its okay to fail. So take tayi magana da wani…
“Ka kaini gida da sauri…” ta fadawa dreban.
Duk da a lokacin ba Bilkisu take so ta gayawa ba, ba ta da zabi sai na kiranta tunda tana jiranta itama taji sakamakon ta.
Tana danna kiran kamar Bilkisun na jira ta dauki wayar. Hafsah ta runtse idonta hawaye na zuba sannan ta samu courage din yin magana. “Result yayi kyau besty. Kina da 3.8 kuma babu carryover…” ihun murna Bilkisu ta tsala sannan cike da farin ciki tace.
“Besty dan Allah wait, bari na gayawa Tariq…”
Hafsah ta sauke wayar sannan ta jinginar da kanta a kan window. Har suka isa gida bata daina tunani ba. Cike da damuwa ta karasa cikin gidan ba tare da tayiwa kowa magana ba. Ko da ta shiga dakinta ma rufo kofar tayi sannan ta kwanta a gefen gadonta ta fara rusa kuka. Sai da tayi me isarta sannan ta tashi ta wanke fuskarta, tayi sallah.
Bayan ta idar ne ta samu nutsuwa sannan ta tuna ma ashe a gidan Goggo take ba gidan su ba. Ko ya akayi ma dreban ya kawota gida ita ba zata iya tunawa ba.
Wayarta ta janyo tayiwa Halimah text tana gaya mata a gida zata kwana.
Har yanzu zuciyarta take ji tayi mata nauyin da sai tayi magana da wani zata samu sauki. A wannan lokacin kuma mutum daya ne ya zo ranta.
Uncle Mukhtar…
************
Ban iskar da aka samu kwana biyu ba tare da anyi ruwa ba yasanya garin yin zafi, wannan yasa da yawan mazan unguwar firfitowa kama daga matasa har dama maginta ko ina ka bi cikin unguwar maza zaka gani wasu bisa bencina wasu bisa tabarmi kowa da abinda yake, can gefen kwata bakin wani kanti bencin su Muktar ne shida abokan sa da suke zaune gefen teburin da Ibrahim ke saida kaza soyayyiya, kilishi, da dambun nama.
Nasir da ya ƙara so wurin ɗauke da katuwar baƙar leda ne ya zauna ƙarshen bencin tare da faɗin "wash! Allah yau na gaji da yawa" Salisu ne ya ɗan leƙo kai "kai dai walllahi ka cika ragon ta in ba haka maine abin gajiya a wannan ƴar ledar da ka ɗauko?"
Hararar sa Nasir ya yi "ai gwamma ni da baki kawai na ce na gaji kai na tabbatar sai dai kama faɗi wanwar"
Muktar ne yasa dariya "kai dai Nasiru baka mutunci mai ka maida Salisun ne?"
Nasir bai bashi amsa ba ya hau fito da atamfofi cikin leda yana faɗin " Haja ce na kawo muku dukan mu nasan kayan aure muke haɗawa"
Ibrahim da ke gaban glass ɗin da kayan sana'ar suke yana zubawa matashin saurayin da ya zo siyan dambun nama da doya ne ya yi caraf ya ce inason jar can zatawa Fiddausi na kyau" ya faɗa yana ninke takardar da ya zuba doya.
Salisu ne ya zuro hannu zai ɗauka Nasir ya yi caraf ya ce "koda bashi bani baka, kuɗi hannu nake bawa marasa sana'a"
" Kut.. wai mai kuka maida ni ne?" Salisu ya faɗa a fusace.
Ibrahim da ya komo ya zauna ne ya ɗauki jar da yace yana so yana ƙara ɗaga ta cikin hasken street light "anma atamfar nan ta yi kyau, bama zan sa a lefe ba gobe zan kai mata, in haɗa mata da kwanukan da tayo min cin cin" ɗan juyowa ya yi ya kalli Salisu mutumina kabi shawarar Muntari ka kama sana'a walllahi"
Banza Salisun ya masa tare da ci gaba da ƙoƙarin kama tasha a radiyon sa.
Nasir ne ya taɓo Muktar da tunda aka fara batun kayan baice komai kan su ba yace " ya mutumina banga kafa ɗauka ba?" Murmushi Muktar ya yi abin ai na masu ƴan mata ne.
Nasir ne ya ɗago wata golden ɗin atamfa ya ɗora kan cinyar Muktar wannan ko fara ko baƙa zata mata kyau ina faɗa ma, kama daina wayancewa ni namiji ne nasan duk nunƙufurcin mutun dole akwai wadda yake ɗan tayawa"
Kallon atamfar da ke cinyar sa ya yi, bai ankara ba zuciyar sa ta fara zayyano masa Hafsa cikin atamfar cikin sauri ya mayarwa da Nasir kan cinyar sa, " aiko kai namijin ƙarya ne tunda dai bakasan da irin mu ba wanda sam soyayya bata gaban su"
Dariya Nasir yasa tare da mayar masa atamfar " ka rantse da Allah babu wadda kake so"
Shiru Muktar ya yi tare da shan kunu, Salisu ne ya zuro kai "ka rantse mana" ya faɗa yana tsare Muktar da idanu.
Tsuke fuska Muktar ya kumayi lokacin guda zuciyar sa na ayyano masa Hafsa yanzu da ya yi tunani mai zurfi ya fahinci bawai iya burgeshi yarinyar kawai take ba, har da ɓurɓushin so duda shiɗin baisan ya son yake ba.
" Sabida mai zan rantse, abinda na sani shine dai kawai ba wanda nake so"
"Wai kana nufin wannan tsuke fuskar zai sa in ƙyale ka," Salisu ya faɗa tamkar da shi aka fara musun tun asali.
"To karma ka kyale ni mana" Muktar ya faɗa, nefa da yaran da ke ɗan wasa tsakanin hanya suka faɗa suna tsalle ya bawa Muktar damar miƙewa bayin Allah sai da safen ku dama zafi ya fito dani"
Nasir ne ya yi saurin miƙewa ya danƙa masa atamfar kaban kuɗin ƙarshen wata," numfashi ya furzar tare da kallon atamfar kamar zai maido masa da ita sai kuma ya juya ya yi gida.
Wutar nefan da aka kawo ta haske tsakar gidan su Inna na zaune tana kwaɓin fanke Juwairiyya na Feraye kabewa yasan ta abincin safen gobe ce yayin da Hajara ke rubutu ya yi sallama kusan dukkanin su suka amsa.
Hajara ta ɗago ne ta ce "lah yaya mai ka siyo?"
Hajara ta tambaya cewa ya yi "Idon matambayi," Juwairiyya tasa dariya inda Hajara ta yi ƙas da kai tana zumɓura baki. Gefen Inna ya aje ledar tare da faɗin "Nasiru ke siyar wa na ɗaukan miki wannan in kalar bata miki ba sai ince ya kawo ki zaɓa"
Da rawar jiki Inna ta buɗe "kai masha Allah, ai ta yi sosai gabaki ɗaya suka faɗa, albarka Inna ta hau sa masa tamkar ya siya mata duniyar nan yayin da shi kuma yake ta faman murumushi da faɗin "Amin"
Ɗakinn sa ya shige yana sauraron Addu'oin da Innar ke masa idanun sa bisa fanka da ke kaɗawa baima san sa'adda bacci ya yi gaba da shi ba.
*****
Tunanin yadda zata iya koyan electricity and magnetism ɗinnan ne duk ya cika mata rai, mafita ɗaya ta faɗo mata shine Uncle Muktar, inda tasan course ɗinnan zata faɗi ɗin da gaske, da tuni tun suna hutu da take zuwa da zaman hira da suke lokacin break da tuni tasa ya fara koya mata, sai dai yanzu babu dama tunda sun koma makaranta, next week zasu fara lectures gobe ko jibi take son siyi handing over da malamar da zata rike ajin da take.
Sam ta rasa mai yake mata daɗi, karatu da BUK ɗin duk tabi ta tsane su, dama ba son Agric ɗin nan take ba, tsaki taja ita dama art take tasan ba za'a bata Agric ba.
Yunwa da ta fara tambayar ta yasa ta miƙewa ta kunna fitilar ɗakin ta dan tunda ta shigo ta yi sallah take kan daddumar bata ko motsa ba tun bayan sakon da ta turawa Aunty Halima, ranta sam babu daɗi ta daure ta fito falon fatan ta kar ta haɗu da kowa har zuwa gobe ta samu ta koma gidan Gwaggo.
Hango ta da Khalil ya yi wanda yake ta fama wasa shida ƙanwar sa khairi ne ya rugo da gudu yana tsalle yana faɗin "Aunty Hafsa shine kika tafi kika barni ko, yau she kika dawo?"
Jin Khalil ya anbaci Hafsan ya sa Abba juyowa " Hajiya Hansatu ashe kina gida?" Daurewa Hafsan ta yi ta ƙaraso.
"Abba sannu da gida" ta faɗa kallon ta yi damuwar da ta bayyana a fuskar ta yasa shi shima damuwa kafin ya ce wani abu Momy ta fara faɗa.