Sashe 46
Kida A Ruwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ranar Lahadi su Nimrah suka dawo gida da yamma. A kuma ranar Daddy Imran da tunda suka je gidan bai kwana ba dan Ammie ta faɗa musu yana wajen aiki yazo gidan da safe, sun nuna farin cikin ganinsa shima kuma yaji daɗin ganinsu. Dan haka suka zagayeshi da uban surutunsu yana biye musu. A ƙasan ransa kam ji yake badan yau ne tafiyar nan tasu ba daya shiryata da Nimrah a ciki. Amma lokaci ya riga ya ƙure, dan yau ne jirginsu zai tashi ƙarfe goma na dare shi da Haysam. Tunanin ya ture gefe ya cigaba da biye musu, dan sunata masa shagwaɓa wai zasuyi missing ɗinsa saboda ya sanar musu zai yi tafiya, kuma zai jima dan wata ɗaya zai yi ko sama da haka. Da yammar ma da kyar suka yarda suka bi Yaya Khalifa da zai maidasu gida. Shi Daddy Imran yace sai anyi isha'i zai shigo yayi ma Mammah sallama...
Da yamma Mu'azz yazo ɗaukar su shima, sai kawai Khalifa yay zamansa dan dama yana da uzirin aikin makaranta. Ammie ta haɗa musu kayan kwalliya da kayan ƙamshi na musamman na turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Suna da turare wuta da khumra kaloli har uku: black humra, white humra, brown humra. Akwai oil perfume da kullacham da genine da Turare kabasa kaloli uku shima. white, black, and brown. Akwai man kitso, da kayan gyaran jiki masu gyara fata da sanyata laushi da santsi kiyita glowing abinki hajjaju. Duk da kuwa Aunty Biebah ta saya musu kwanaki. Yanzu ɗin ma harda na Biebah Ammie ta bada, sannan taima Mammah gasashen nama mai ɗan karen daɗi itama a kai mata. Suka wuce Asma'u na musu tsiyar yau zatai barci mai daɗi. Lolo kuwa yana islamiyya ma suka wuce da ansha rigima duk da shima fa ya zama ɗan saurayi tunda 2years kawai Rukyn ta bashi. Gasu yanzu suna shekara sha biyar da watanni. Sai da suka fara sauke Fedoo a gidansu, sannan Bintu. Dan gobe in sha ALLAHU Monday ba batun tafiya gidan Mammah a cigaba da shargalle. Su kuma su biyu Mu'azz ya wuce da su gida cike da jin kewar ƴan uwansu da aka rabu.
Received at 3:59 P Maigadi ya buɗe musu gate, Mu'azz ya shige da motar yana samun waje yay parking. Sun fito suna gulmar ƙanin maigadi Sanda dan gayene, akwai son yin gayu sai dai irin namu na ƙauye.
Har zasu wuce ciki sabon driver ya iso wajen yana kiran sunan Nimrah. Kusan lokaci guda Nimrah, Ruky, Mu'azz suka juyo da mamaki. Nimrah da ƙirjinta yay mummunar bugawa da ƙyar ta iya daurewa ta amsa masa. Sai dai ta kasa motsawa taje inda yake sai shine ya ƙaraso. Ledar hannunsa ya miƙa mata yana faɗin, “Yaron nan daya kawo mage ranar ne yace a baki. Yace a gaishe ku ke da yar uwarki”.
Ji Nimrah take kamar jikinta na rawa. Ta dai daure ta amsa tana gyaɗa masa kai dan ta kasa magana. Shi kuma bai damu ba ya juya ya bar wajen. Sai ma Ruky ce dake ƴar dariya cikin tsokana ta ce,.........✍️
Received at 3:59 PMKIƊA A RUWA 2
44
..........“Da alama fa Sayyadi Kamal ya buɗe wuta Sisi, kwanaki a gidan Aunty Mimi books, kwana biyu da suka wuce ma haka, yau kuma mi muka samu?”.
Har Nimrah ta sakar mata ledar sai kuma ta amshe da sauri saboda tuna takardar cikin wancan saƙon. Dai-dai Mu'azz na ƙarasowa yana tambayar, “Sayyadi Kamal ɗin dai again yau ma?”.
“Ai kuwa dai Yaya Mu'azz, halan bakuyi masa maganar da kuka ce ba?”.
Ruky ta bashi amsa cike da shaƙiyanci. Sai dai kafin yay magana Nimrah tabar gurin da sauri, ga kuma su Yaya Ma'aruff sun shigo suma gidan da alama daga wani waje suke dan a ƙafa suke, sai ya zam hankalinsu Ruky ya rabu har su Yaya Ammar ɗin suka tambayesu lafiya ganin yanda Nimrah ta wuce ciki kamar da sassarfa. Cikin takaici Mu'azz ke sanar musu wai saƙo sayyadinsu na islamiyya ya aikoma Nimrah.
“Saƙon mi?”.
Yaya Ma'aruff ya tambaya.
Kallon Ruky Mu'azz yayi da faɗin, “Wlhy Uncle ban sani ba nima. Ruky ce tasan komai duk da dai ranar muna gidan Daddy ya aiko mata books nan ma”.
Hankalinsu duk suka maida akan Rukyn, sai duk taji tsoro ya kamata. Da sauri ta ce, “ALLAH ba komai fa Uncle, kawai dai ina ga litattafai ne.”
Yanda tayi yasa duk suka fahimci akwai abinda ya dace su sani bayan hakan. Dan haka Yaya Ammar ya ce, “Kinga zo nan”.
“Uncle nace fa ba komai ALLAH”.
“Nima ai bance da komai ba Ruky, canai kawai kizo naji.”
Ita tsoronta kar suji son Nimrah yake a musu faɗa, amma babu yanda ta iya ta ƙarasa inda suke. Wani lokacin Yaya Bilal ya fisu sauƙi su ukun nan har Dadan ma. Amma yau sai ga Yaya Ja'afar cikin lallashi yana tambayarta ta faɗa musu bazasu musu faɗa ba. Minene tsakanin Nimrah da Sayyadin nasu?.
“Idan kuma bazaki faɗa ba zan sanar da Yaya.”
Tasan Daddynsu ake nufi, dan haka ta shiga girgiza kai, “A'a Uncle dan ALLAH karka faɗa masa. Dama kawai shi Sayyadin yana son Ninah ne. Amma wlhy bata kulashi, kuma ka tambaya ma kaji”.
“In bata kulashi miyasa yasan gidan ku?”.
Yaya Ma'aruff ne yay magana yanzu. Da sauri Rukyn ta ce, “Randa ya kawo mage ne, sai kuma ranar sunan Baby Nawal ya kai saƙo gidan Mah-mah na books, kuma can gidan ma muka mantasu. Shekaran jiya ma a gidan Daddy haka”
Ammar zai yi magana Yaya Ja'afar ya hanashi ta hanyar riƙe masa hannu, ƙofa ya nunama Rukyn da faɗin, “Shike nan shige ciki”.
Aiko da gudu ta wuce. Koda ta shiga falo ba taga Nimrah ba sai su Aunty Biebah, sai kawai ta rungume Biebah ɗin, kafin ta saketa ta koma kan su Aunty Lailah tana tambayar ina Mammah?. Bedroom suka nuna mata inda Nimrah dama tana ciki, dan itama tana shigowa ta gansu sai ta shanye tashin hankalinta tayi kamar yanda Ruƙayya tayi sannan ta shige bedroom ɗin Mammah. Tana rungume da ita itama Rukyn ta shigo, sai kawai itama ta rungume Mammah ɗin dan kewarta suke ji mai girman gaske......
==============
Da daddare kamar yanda Daddy Imran ya faɗa yazo yay ma Mammah sallama akan zaije wani aiki. Amma zai jima dan zai iya ɗaukar wata ɗaya ma. Mammah ta jimanta sosai, amma tai masa addu'a ranta duk babu daɗi. Ganin Imran na rage mata kewa Dada sosai a zuciyarta. Shiyyasa bata cika son taga shima zaiyi nesa da su ba. Sai dai babu yanda suka iya tunda aikinsu ne.
Su kansu su Yaya Ma'aruff sunji babu daɗi, dan kamar dai Mammah ɗince Imran na ɗauke musu kewar Dada. Amma da yake su maza ne sai suka danne suka bishi da addu'a suma. Daga nan suka taɓa hira Ruky da Nimrah na jera masa tsarabar da suke so idan zai dawo harda wayoyi. Duk da dai Nimrah dauriya kawai take yi tun ɗazun hankalinta nakan saƙon Sayyidi Kamal da bata samu ta duba ba. Ƙarfe tara dai-dai Imran yabar gidan, daga nan kuma airport zai wuce dan a can zasu haɗu da Dada kawai...
Bayan wucewarsa Nimrah ta faki idonsu ta wuce ɗaki ganin hankalin Ruky ya koma wajen yima su Abees homework ita da Mu'azz. Gabanta sai faɗuwa yake, tana shiga ta maida ƙofar ta rufe harda mirza key dan jikinta ma rawa yake. A haka ta buɗe ledar ta leƙa, a mamakinta yau ma books ne kamar koyau she. Sai dai yau guda ɗaya ne kawai, hisnul muslim ne kuma ƙarami.
Received at 4:00 PMJininta na tsinkewa ta ciroshi, haka ta shiga buɗeshi zuciyarta na rawa. Kamar Ranar kuwa sai ga takarda ƙarama a ciki, ɗauka tai ta buɗe.
_Da alama baki duba saƙon ranar ba ko? To ki sani, cigaba da sakacinki na nufin yin dana sani. Duk da kuwa a cikin dana sanin kike shekaru da dama. Idan kuma bakiyi gaggawar dubawa ba zaki dawwama a dana sanin har karshen rayuwarki musamman idan kika fara cin karo da gawar wani a cikin gidank....._
Batama iya ta ƙarasa ba saboda wani yuuuu data risketa na hajijiya. Ta miƙe zambar tana nufar inda suke ajiye handbags ɗinsu. Laluben ta wadda tai amfani da ita a ranar ta shiga yi dan ko books ɗin batama cireba a ciki. Haka ta zazzageta litattafan suka zubo ƙasa. Tsabar ta rikice tama manta littafin da ka rubuta saƙon yake a ciki a ranar, dan haka dukansu ta shiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya sai ana ƙarshe taga takardar, ɗauka tai ta sake karantawa, jin book mai jan bango yasa ta ɗaukesa ta fara buɗo shafukan ƙarshe tana duba lamba harta samu wanda akace. Data buɗe shafin bataga komai ba, sai da ta maida zata rufe ta farga da memory card da aka tura ciki sosai kaɗan ake ganinsa. Tana jawo shi ta wani sauke ajiyar zuciya mai nauyi, sai da ta zuba masa ido ranta fal tambayoyin da basu da amsa. Dai-dai nan aka fara buga ƙofa dan haka ta miƙe tana tattare books ɗin da sauri ta maida a bag ɗin, memoryn ta saka a cikin bra dan dole ta nema waya yanzun nan.
Koda taje ta buɗe ƙofar sai taga Afrah ce. Da ƙyar ta daure ta ce, “My Afry ya akayi?”.
“Aunty yunwa nake ji, kuma ke nake so kimin noodles”.
Kai ta iya jinjina mata kawai ta kama hannunta suka fita......
<%><<%>><%>
Da yamma Mu'azz yazo ɗaukar su shima, sai kawai Khalifa yay zamansa dan dama yana da uzirin aikin makaranta. Ammie ta haɗa musu kayan kwalliya da kayan ƙamshi na musamman na turarrukan SHUWA INCENSE AND MORE +234 704 229 3387. Suna da turare wuta da khumra kaloli har uku: black humra, white humra, brown humra. Akwai oil perfume da kullacham da genine da Turare kabasa kaloli uku shima. white, black, and brown. Akwai man kitso, da kayan gyaran jiki masu gyara fata da sanyata laushi da santsi kiyita glowing abinki hajjaju. Duk da kuwa Aunty Biebah ta saya musu kwanaki. Yanzu ɗin ma harda na Biebah Ammie ta bada, sannan taima Mammah gasashen nama mai ɗan karen daɗi itama a kai mata. Suka wuce Asma'u na musu tsiyar yau zatai barci mai daɗi. Lolo kuwa yana islamiyya ma suka wuce da ansha rigima duk da shima fa ya zama ɗan saurayi tunda 2years kawai Rukyn ta bashi. Gasu yanzu suna shekara sha biyar da watanni. Sai da suka fara sauke Fedoo a gidansu, sannan Bintu. Dan gobe in sha ALLAHU Monday ba batun tafiya gidan Mammah a cigaba da shargalle. Su kuma su biyu Mu'azz ya wuce da su gida cike da jin kewar ƴan uwansu da aka rabu.
Received at 3:59 P Maigadi ya buɗe musu gate, Mu'azz ya shige da motar yana samun waje yay parking. Sun fito suna gulmar ƙanin maigadi Sanda dan gayene, akwai son yin gayu sai dai irin namu na ƙauye.
Har zasu wuce ciki sabon driver ya iso wajen yana kiran sunan Nimrah. Kusan lokaci guda Nimrah, Ruky, Mu'azz suka juyo da mamaki. Nimrah da ƙirjinta yay mummunar bugawa da ƙyar ta iya daurewa ta amsa masa. Sai dai ta kasa motsawa taje inda yake sai shine ya ƙaraso. Ledar hannunsa ya miƙa mata yana faɗin, “Yaron nan daya kawo mage ranar ne yace a baki. Yace a gaishe ku ke da yar uwarki”.
Ji Nimrah take kamar jikinta na rawa. Ta dai daure ta amsa tana gyaɗa masa kai dan ta kasa magana. Shi kuma bai damu ba ya juya ya bar wajen. Sai ma Ruky ce dake ƴar dariya cikin tsokana ta ce,.........✍️
Received at 3:59 PMKIƊA A RUWA 2
44
..........“Da alama fa Sayyadi Kamal ya buɗe wuta Sisi, kwanaki a gidan Aunty Mimi books, kwana biyu da suka wuce ma haka, yau kuma mi muka samu?”.
Har Nimrah ta sakar mata ledar sai kuma ta amshe da sauri saboda tuna takardar cikin wancan saƙon. Dai-dai Mu'azz na ƙarasowa yana tambayar, “Sayyadi Kamal ɗin dai again yau ma?”.
“Ai kuwa dai Yaya Mu'azz, halan bakuyi masa maganar da kuka ce ba?”.
Ruky ta bashi amsa cike da shaƙiyanci. Sai dai kafin yay magana Nimrah tabar gurin da sauri, ga kuma su Yaya Ma'aruff sun shigo suma gidan da alama daga wani waje suke dan a ƙafa suke, sai ya zam hankalinsu Ruky ya rabu har su Yaya Ammar ɗin suka tambayesu lafiya ganin yanda Nimrah ta wuce ciki kamar da sassarfa. Cikin takaici Mu'azz ke sanar musu wai saƙo sayyadinsu na islamiyya ya aikoma Nimrah.
“Saƙon mi?”.
Yaya Ma'aruff ya tambaya.
Kallon Ruky Mu'azz yayi da faɗin, “Wlhy Uncle ban sani ba nima. Ruky ce tasan komai duk da dai ranar muna gidan Daddy ya aiko mata books nan ma”.
Hankalinsu duk suka maida akan Rukyn, sai duk taji tsoro ya kamata. Da sauri ta ce, “ALLAH ba komai fa Uncle, kawai dai ina ga litattafai ne.”
Yanda tayi yasa duk suka fahimci akwai abinda ya dace su sani bayan hakan. Dan haka Yaya Ammar ya ce, “Kinga zo nan”.
“Uncle nace fa ba komai ALLAH”.
“Nima ai bance da komai ba Ruky, canai kawai kizo naji.”
Ita tsoronta kar suji son Nimrah yake a musu faɗa, amma babu yanda ta iya ta ƙarasa inda suke. Wani lokacin Yaya Bilal ya fisu sauƙi su ukun nan har Dadan ma. Amma yau sai ga Yaya Ja'afar cikin lallashi yana tambayarta ta faɗa musu bazasu musu faɗa ba. Minene tsakanin Nimrah da Sayyadin nasu?.
“Idan kuma bazaki faɗa ba zan sanar da Yaya.”
Tasan Daddynsu ake nufi, dan haka ta shiga girgiza kai, “A'a Uncle dan ALLAH karka faɗa masa. Dama kawai shi Sayyadin yana son Ninah ne. Amma wlhy bata kulashi, kuma ka tambaya ma kaji”.
“In bata kulashi miyasa yasan gidan ku?”.
Yaya Ma'aruff ne yay magana yanzu. Da sauri Rukyn ta ce, “Randa ya kawo mage ne, sai kuma ranar sunan Baby Nawal ya kai saƙo gidan Mah-mah na books, kuma can gidan ma muka mantasu. Shekaran jiya ma a gidan Daddy haka”
Ammar zai yi magana Yaya Ja'afar ya hanashi ta hanyar riƙe masa hannu, ƙofa ya nunama Rukyn da faɗin, “Shike nan shige ciki”.
Aiko da gudu ta wuce. Koda ta shiga falo ba taga Nimrah ba sai su Aunty Biebah, sai kawai ta rungume Biebah ɗin, kafin ta saketa ta koma kan su Aunty Lailah tana tambayar ina Mammah?. Bedroom suka nuna mata inda Nimrah dama tana ciki, dan itama tana shigowa ta gansu sai ta shanye tashin hankalinta tayi kamar yanda Ruƙayya tayi sannan ta shige bedroom ɗin Mammah. Tana rungume da ita itama Rukyn ta shigo, sai kawai itama ta rungume Mammah ɗin dan kewarta suke ji mai girman gaske......
==============
Da daddare kamar yanda Daddy Imran ya faɗa yazo yay ma Mammah sallama akan zaije wani aiki. Amma zai jima dan zai iya ɗaukar wata ɗaya ma. Mammah ta jimanta sosai, amma tai masa addu'a ranta duk babu daɗi. Ganin Imran na rage mata kewa Dada sosai a zuciyarta. Shiyyasa bata cika son taga shima zaiyi nesa da su ba. Sai dai babu yanda suka iya tunda aikinsu ne.
Su kansu su Yaya Ma'aruff sunji babu daɗi, dan kamar dai Mammah ɗince Imran na ɗauke musu kewar Dada. Amma da yake su maza ne sai suka danne suka bishi da addu'a suma. Daga nan suka taɓa hira Ruky da Nimrah na jera masa tsarabar da suke so idan zai dawo harda wayoyi. Duk da dai Nimrah dauriya kawai take yi tun ɗazun hankalinta nakan saƙon Sayyidi Kamal da bata samu ta duba ba. Ƙarfe tara dai-dai Imran yabar gidan, daga nan kuma airport zai wuce dan a can zasu haɗu da Dada kawai...
Bayan wucewarsa Nimrah ta faki idonsu ta wuce ɗaki ganin hankalin Ruky ya koma wajen yima su Abees homework ita da Mu'azz. Gabanta sai faɗuwa yake, tana shiga ta maida ƙofar ta rufe harda mirza key dan jikinta ma rawa yake. A haka ta buɗe ledar ta leƙa, a mamakinta yau ma books ne kamar koyau she. Sai dai yau guda ɗaya ne kawai, hisnul muslim ne kuma ƙarami.
Received at 4:00 PMJininta na tsinkewa ta ciroshi, haka ta shiga buɗeshi zuciyarta na rawa. Kamar Ranar kuwa sai ga takarda ƙarama a ciki, ɗauka tai ta buɗe.
_Da alama baki duba saƙon ranar ba ko? To ki sani, cigaba da sakacinki na nufin yin dana sani. Duk da kuwa a cikin dana sanin kike shekaru da dama. Idan kuma bakiyi gaggawar dubawa ba zaki dawwama a dana sanin har karshen rayuwarki musamman idan kika fara cin karo da gawar wani a cikin gidank....._
Batama iya ta ƙarasa ba saboda wani yuuuu data risketa na hajijiya. Ta miƙe zambar tana nufar inda suke ajiye handbags ɗinsu. Laluben ta wadda tai amfani da ita a ranar ta shiga yi dan ko books ɗin batama cireba a ciki. Haka ta zazzageta litattafan suka zubo ƙasa. Tsabar ta rikice tama manta littafin da ka rubuta saƙon yake a ciki a ranar, dan haka dukansu ta shiga buɗewa ɗaya bayan ɗaya sai ana ƙarshe taga takardar, ɗauka tai ta sake karantawa, jin book mai jan bango yasa ta ɗaukesa ta fara buɗo shafukan ƙarshe tana duba lamba harta samu wanda akace. Data buɗe shafin bataga komai ba, sai da ta maida zata rufe ta farga da memory card da aka tura ciki sosai kaɗan ake ganinsa. Tana jawo shi ta wani sauke ajiyar zuciya mai nauyi, sai da ta zuba masa ido ranta fal tambayoyin da basu da amsa. Dai-dai nan aka fara buga ƙofa dan haka ta miƙe tana tattare books ɗin da sauri ta maida a bag ɗin, memoryn ta saka a cikin bra dan dole ta nema waya yanzun nan.
Koda taje ta buɗe ƙofar sai taga Afrah ce. Da ƙyar ta daure ta ce, “My Afry ya akayi?”.
“Aunty yunwa nake ji, kuma ke nake so kimin noodles”.
Kai ta iya jinjina mata kawai ta kama hannunta suka fita......
<%><<%>><%>