Sashe 29
Kida A Ruwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read
A kwanakin farko na kawo television ɗin ɗakinsa bai maida hankali akan zaman kallonta ba, dan lissafinsa nakan haɗa kalaman vistor ɗinsa da musu fashin baƙi a farashin mutane masu hangen nesa da basu raina bincike irinsa. Abu uku kawai da aka turke tvn da ita ne ya fara tasirin jan hankalinsa gareta dole. Sun saka mata security ta yanda bata kasuwa, bai iya rage volum, bai canja tasha daga ukun nan kacal duk da kuwa akwai remote. Duk da basu sakata da ƙara mai takura ba kasancewar sa mutum mara san damuwa da hayaniya sai da ta fakurashi a kwanakin farkon. Sai daga baya daya fahimci an kawota ne garesa dan tai masa irin wannan takurar ai sai ya dake ya ajiye komai gefe har a kwana na huɗu ya maida hankali a kallon fashin baƙin masana akan taron campaign ɗin da aka rufe, a bazata yaci karo da na Janar Yusuf Shu'aibu Tafida ne a gaba. Duk da bawai akan Janar ɗin masu fashin baƙin ke tattaunawar ba, suna tattaunawa ne akan mabiyan ɗan takara, inda daga ƙarshe suke faɗin alƙaluma na sake nuna tsohon Janar dake gaba wajen tara masoya a duk jahar da yaje. Wannan shine karo na farko daya fara bama tvn hankalinsa, daga ranar kuma ya cigaba da bibiyar komai daki-daki, har hakan ya bashi damar fara tantance kowace fuska dake tare da Janar Yusuf dama sauran ƴan takara tun daga na shugaban ƙasa har zuwa shugabannin jihohi. A haka aka gangaro har ranar zaɓe, duk yanda abubuwan ke gudana nan ma yana biye, sai ta kai har ƙirga ƙuri'u ya bibiya. Sai dai a yau da aka tashi da jiran faɗar sakamako ya yini da ciwon kai saboda matsawa kansa da ayyukan ƙwaƙwalwa da yay a cikin satin nan gaba ɗaya. Dan haka bai wani maida hankali ba sosai ga television ɗin, bayan ma ya idar da sallar isha'i yay zaman fara karatun Alkur'ani ne, kasancewar tvn ba kasuwa take ba, ba rage ƙara take ba a bazata bayanin shigaban hukumar zaɓe ya shiga cikin kunnensa.
Cak harshensa ya tsaya dai-dai da bugun zuciya na sakanni, kafin ya iya ɗago manyan idanunsa zuwa kan tvn ya saukesu akan fuskar ɗan jaridar dake maimaita kalmar.........✍️
Received at 4:21 PM
reacted[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2
29
..........“Wow! Congratulations, Her Excellency General Yusuf Tafida.”
Dada bai motsa ba. Bai yi murmushi ba. Bai yi mamaki ba.
Sai dai zuciyarsa ta furta abu guda ɗaya dai-dai da lumshewar idanunsa a hankali (Wata rana gaskiya za ta dawo da kanta. In dai har zuciya bata manta da UBANGIJI da masu gaskiyar ba) sai kuma a hankali ya ajiye Alkur'anin ya zame zuwa sujuda. Ya jima kafin ya ɗago ya sake ɗaga hannu yana ambaton, “Subahanal-lah! Allahu-akbar!”. Akan tausasan laɓɓansa
Bai ce ya damu da samuwar shugabancin Janar Tafida domin ya fita anan ba, amma tabbas ya damu da addu'ar ƙasar nan tasamu mai kishin ƙasa kamar Janar da yakema ƙyaƙyƙyawan fata akowane motsinsa, ta samu shugaba mafi alkairi, yana ji kuma a ransa ogansa kuma yaya koma uba shine zaɓin ALLAHn da suke fata da roƙa in sha ALLAHU. Sake juyawa yay yana kallon tvn a karo na biyu, dan duk da sanarwar dare ce wasu wajajen har al'umma sun fara bikin murna, sauke numfashi mai nauyi yayi, zuciyarsa tana ƙonewa irin ƙonawar da MAZAN FAMA kawai ke iya fuskanta a lokacin da suke iya hango HASKEN MASU GASKIYA......
÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷
★ONE WEEK LATER★
Cak harshensa ya tsaya dai-dai da bugun zuciya na sakanni, kafin ya iya ɗago manyan idanunsa zuwa kan tvn ya saukesu akan fuskar ɗan jaridar dake maimaita kalmar.........✍️
Received at 4:21 PM
reacted[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: KIƊA A RUWA 2
29
..........“Wow! Congratulations, Her Excellency General Yusuf Tafida.”
Dada bai motsa ba. Bai yi murmushi ba. Bai yi mamaki ba.
Sai dai zuciyarsa ta furta abu guda ɗaya dai-dai da lumshewar idanunsa a hankali (Wata rana gaskiya za ta dawo da kanta. In dai har zuciya bata manta da UBANGIJI da masu gaskiyar ba) sai kuma a hankali ya ajiye Alkur'anin ya zame zuwa sujuda. Ya jima kafin ya ɗago ya sake ɗaga hannu yana ambaton, “Subahanal-lah! Allahu-akbar!”. Akan tausasan laɓɓansa
Bai ce ya damu da samuwar shugabancin Janar Tafida domin ya fita anan ba, amma tabbas ya damu da addu'ar ƙasar nan tasamu mai kishin ƙasa kamar Janar da yakema ƙyaƙyƙyawan fata akowane motsinsa, ta samu shugaba mafi alkairi, yana ji kuma a ransa ogansa kuma yaya koma uba shine zaɓin ALLAHn da suke fata da roƙa in sha ALLAHU. Sake juyawa yay yana kallon tvn a karo na biyu, dan duk da sanarwar dare ce wasu wajajen har al'umma sun fara bikin murna, sauke numfashi mai nauyi yayi, zuciyarsa tana ƙonewa irin ƙonawar da MAZAN FAMA kawai ke iya fuskanta a lokacin da suke iya hango HASKEN MASU GASKIYA......
÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷
★ONE WEEK LATER★