← Book details Kida A Ruwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 35 OF 47

Sashe 35

Kida A Ruwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

      A hankali ƙofar corridor ɗin ta buɗe. Sai kowa ya sake nutsuwa da zubama ƙofar ido musamman Imran, Faro, shugaban prison. Yaran sojojin uku da suka rage a wajen kawunansu a ƙasa na girmamawa. Sakan goma tsakani jarumin jarumai ya bayyana, bayyanar data saka gaba ɗaya sojojin wajen harda su Imran ƙamewa a tare suka sara masa.Sai da ya lumshe idanunsa ya buɗe a kansu, sannan shima ya dunƙule hannaye duka yana ɗan miƙasu gaba alamar amsar girmamawar su. A karo na biyu, shugaban prison, Imran, Faro suka sake ƙamewa da sarawa irin ta girma da girma. A yanzu kam shima sai ya ƙame ya sara musu su ukun murmushin mai nauyi ya bayyana a fuskarsa. Kai tsaye ya saka idanunsa cikin na Faro da shima ke murmushi, ido ɗaya Faro ya kashe masa da sake yin wani salute na abokantaka da amintaka.
      Dada ya girgiza kansa yana murmusawa da yima Faro alamar (bazaka taɓa canjawa ba) da idanunsa. Sai kuma ya janyesu a slowly ya maida kan Imran da ya tsaya cak kawai yana kallon sa shima. Idanusu ne suka haɗu cikin juna, shekaru takwas na ɓacin rai, rashin adalci, fushi da raɗaɗi duk suka bayyana cikin wannan idanuwa huɗun tamka a film ɗin da aka dannama pause.
      Zak-Shadow ya sakarma Imran murmushi cikin nauyin zuciyar da ya saba ɓoyewa.
     “…Imran Abbas?”.
   Dada ya faɗa a karo na farko da wani irin salo na jini yaga jini.
      Imran ya saki murmurshi tare da matsawa kusa da shi gab, sai kawai ya rungumeshi.
         “Shagwaɓaɓɓena”.
     Dada ya faɗa cikin kunnen Imran jin saukar hawayensa akan kafaɗarsa. Share hawayen yayi sannan ya ɗago yana murmurshi.
       “Alƙawarin ALLAH ya cika. Rubutacciyar ƙaddara daga littafi na gaskiya ta taƙaita. UBANGIJI ya tabbatar mana zai jarabcemu, sai dai da jarabawar nan zai ɗaga darajojinmu a sama idan mun kasance masu haƙurin cinyeta. Ƙasarka ta jira dawowarka. Zuri'a bata manta da kai ba. Rundunar soji na kwatance da sunanka. Bararka da zuwa mai son a gina gaskiya a zartar da ita koda zata ƙona kai da kai. ALLAH ya cigaba da amintar da wannan RUHIN bisa kyakkyawan gini na gaskiya. A yau zan buɗe muryar data disashe saboda kukan kewa na faɗama duniya cewar Haysam Abdul-rasheed Shehu is back again”.
        Murmurshi Dada ya saki mai nauyi, zuciyarsa ta rikice da son fitar da abinda ke zagaye da ita na kewa tsahon shekaru, ba dan prison ba, ba don wahala ba, sai dan kalaman Imran dasuka ratsata har cikin jini da jijiya dama ƙashi. Amma da yake mazan maza ne sai suka rikiɗe da ƙarfafa kai bayyananne. Da nayin kamewa da nutsuwa ya furta,
       “Imran! You are my destiny. I am proud of you........✍️
Received at 12:27 PM
[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 34

..........“Almu na maka kiran gaggawa ne saboda ƙarin abokin aiki da zaka samu”.
    Cikin tashin hankali maigadi ya ɗago yana kallon mutumin dake zaune cikin lallausar kujerar ƙayataccen falon. Sai kuma ya sake maida kan nasa ƙasa da sauri. Zuciyarsa na bugawa da yin rawa a cikin ƙirjinsa ya furta, “Ranka ya daɗe nawa aikin baya tafiya dai-dai ne?”.
        Sai da mutumin yaja fin sakan uku kafin ya amsa cike da isa. “Aikin ka na tafiya dai-dai Almu, anzo gaɓar da shima wannan ɗin dole sai ya shiga gidan ne”.
     “Shike nan ranka ya daɗe, yanda kace haka za'ai. Ni dai ALLAH ina sake roƙon arziƙi kada a cutar min da ƴar uwa. Kaima ka sani mu marayu ne, bamu da kowa a wannan duniyar sai kammu mu biyun nan rak.”
          “Bijirema umarni na ne kawai zai iya sakawa ta cutu. Idan ka kiyaye ta kiyaye lokaci kaɗan ya rage muku ku samu freedom.”
      “Zamuyi duk abinda kake buƙata in sha ALLAHU ranka ya daɗe. Amma dan ALLAH zan iya ganinta?”.
     Wani banzan kallo daya saka maigadi sake nutsuwa mutumin ya watsa masa. Sai kuma yaja tsaki yana ɗaukar wayarsa dake gefe yay danne-danne. Kunnensa ya kai, sai dai a taƙaice ya furta, “Zaka iya fitowa”. Daga haka ya ajiye wayar. Shiru falon ya ɗauka, sai ƙarar tv dake fita ƙasa-ƙasa dana ac. Cikin abinda bai gaza mintuna biyar ba wani ya fito. A ƙalla dai bazai wuce shekara talatin da shida ba. Shima cike da tashi izzar yay ma Almu kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Sai da ya zauna a kujera sannan wancan mutumin dake kallonsa fuska da murmurshin da tun da Almu ya shigo bai gani a fuskarsa ba.
      Almu ya nuna yana gyara zama. “Wannan shine mutumin da nake gaya makan. Yana aikin gadi a gidan kusan shekara huɗu ke nan, bayan mun tsige wancan ganin bazai iya mana komai ba.”
      “Shi wannan yana yin abinda ake so kenan?”. Saurayin yay magana a karo na farko.
    “Tabbas yana yi, dan tunda ya fara aiki babu wani kuskure da zance mara daɗi. Sunansa Almu.”
      “Okay”.
  Ya faɗa a taƙaice. Mutumin bai nuna ya damu ba ya cigaba da faɗin, “Zaka shirya ne ku wuce tare? Ko zaka bishi daga baya?”.
      “Kawai mu wuce taren, ai da zafi-zafi ake dukan ƙarfe. Sai dai ya kamata nasan wane aiki zan iya samu a gidan?”.
      Yanzu kam mutumin baice komai ba, illa juyawa da yay shima ya kalla Almu. Da sauri Almu yace, “Ranka ya daɗe sai dai in munje can ɗin, amma a yanzu gaskiya a gidan nan babu wani aiki. Dama a wata biyu daya wuce ne driver ɗinsu ya samu hatsari to da an samu sai ya maye gurbinsa. Amma yanzu ma inada tunani guda, akwai mai sharar tsakar gidan kullum da bama filawoyi ruwa. Yakan zo da safe yayi ya dawo da yamma. Sunyi-sunyi ya dinga zama nan koma kwana yaƙi, acewarsa yana wasu ayyukan ne idan ya kammala da nan. To ko shi zamu tunɓuke ta hanyar maƙarƙashiya sai shi ya maye shi?”.
        “Eh wannan ma kazo da zance mai ƙyau. Amma miyasa ban san da labarin driver ba? Bayan kuma na sanar maka ko sabuwar kaza akai a wannan gidan nasan da ita. Ko cokali ya faɗi nasan da sautin ƙarar faɗuwarsa....”
     “Ka gafarceni ranka ya daɗe, na nemeka amma ban samu ba, idan baka manta ba jiya daka turo min saƙon kana son ganina na tura maka amsa da dama inada wata magana. To dama maganar kenan”.
      Maimakon amsa zancen sai cayay, “Kaje waje ka jira shi zai fito”.
      Idanun Almu cike da ƙwalla ya jinjina kai. Yayi kamar zai miƙe sai kuma ya sake komawa ya duƙa. “Ranka ya daɗe dan ALLAH ko zan iya ganin ƴar uwata ɗin?”.
         “No!”.
   Ya bashi amsa a ɗan tsawace. Da sauri maigadi ya miƙe jikinsa na rawa ya fice a falon. Idanunsa kuwa tuni sun cika da ruwan hawaye. Zuciyarsa kam raɗaɗi take masa. Tabbas badan da ƴar uwarsa da mutanen nan suke amfani wajen juyashi yanda suke so ba sun san basu isa ba. Shine fa Almu, Almu na babba ƙarfe bashi ratsa jininka. Guduma mai fasa kan tantiri.... Ƙwafa yayi yana mai cije laɓɓansa, daga haka ya samu waje a bakin baranda ya zauna......

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Received at 12:27       “Aunty Shariffa karki damu, lokaci ne zaku sani, amma shagalin biki sai Dada na nan in sha ALLAHU”.
     A take falon yay tsitt, Dan shima yayi maganar ne muryarsa na ɗan rawa. Mammah ce tai gyaran murya, dan tasan yanzu zasu fara mata koke-koke. Cikin canja hirar ta ce, “Mudai yanzu tashi ka ɗakko mana tsarabar mu nan duk ita mukai zaman jira”.
        Cikin dariya Bilal ya ce, “Kai Mammah harda ke? To kowa yay haƙuri baza'a buɗe tsarabar nan ba sai yarana sun dawo school gaskiya. Dan sune zasu buɗe ta”.
       “Yau muna ganin jalala, har sai su kafi auta sun dawo za'a bamu tsarabar?”.
       Yanda Aunty Lailah tai maganar yasa kowa fashewa da dariya........✍️
Received at 12:27[01-16, 11:37] +234 703 449 6321: 35

.......... ★PRISON★

       9:30am dai-dai motocin sojojin biyu suka fice daga cikin prison ɗin cikin tsaro mai cikakken sirri, yayin da hukuncin UBANGIJI da ƙarfin ikonsa suka tabbata a daidai wannan lokacin wani razani ya gitta a zukatan wasu mutane daga ɓangaren Ƙungiyar duhu, a ƙasan rayukansu suka dinga jin cewa abu mafi hatsari ya faru. Sai dai daga ina? Daga wane yanki? Akan mi? A dalilin mi? Duk UBANGIJI ya toshe wannan amsoshin daga garesu, koda ata hanyar yaransu dake cikin prison ɗin babu wani labari da suka samu saboda gargaɗin shugaban ƙasa......
Chapter 35 · 0% Book details