← Book details Inayah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 65

Sashe 41

Inayah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hadiza ki warwarewa hajiya komai sbd kawarda zargi da Kuma damuwar qaddarorin dasuka gifta abaya data rabu da 'danta akan hakan.

Dagowa Hadiza tayi jiki a sanyaye ta kalli hajiyar cikeda kunyar Zama mugun sanadin daya kawo abubuwa da dama.

Kan su Yaya Umar da Yaya kabiru ta maida kallonta sbd kusan suma sune sanadin komai.

Inayah data tsaya bakin kofar dakin umma yaganah sbd tanason taji yanda tazo hannun Abbinta da kunnenta batareda wani ya fada Mata ya rage Mata wani abun....

SHEKARUN BAYA....
#MAMUH##
#LOVE/ROMANCE/LOADING

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

Shedar biya👇
07040727902

MTN card👇
09134848107
[11/3, 10:28 AM] +234 704 465 9560: *_38_*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Tana fitowa gidansu rungume da jaririyar tata dake lafe kirjinta tana bacci taji qafafuwanta na Neman sanyi Amma sukasa riqeta sbd wani irin nauyi da kirjinta kemata tareda radadi a maqoshi..

Sake rungume jaririyarta tayi da kyau ahankali kafin ta dago ta kalli hanya da idanuwanta dasuka qafe sukai jajir sbd kuka tuni ya qafe daga Idanuwanta.

Ahankali ta daga qafafunta tafara tafiya tareda kauke kanta qasa sbd Yan anguwa wainda suka lura da ita suke kallonta da ma'anoni da maganganun zunde da zagi.

Bakowane yasan tadwo daga Lagos dinba da ciki saidai sukaji haihuwar tareda rasuwar mahaifiyarta shiyasa kusan duk Wanda ya bude Baki tir da Allah wadai yake furtawa gareta da jaririyar 'yarta.

Ahankali take takawar sbd rashin qarfin jiki dakuma qarin data samu agun haihuwa gakuma rashin abinci ko abinsha Dan haka batada wani babban kuzarin takawa da sauri harta fice daga layin batareda ta waiwayo ba Dan tanajin idanuwan mutane akanta Wanda tasan mummunan fatar rashin ganin me kyau suke Mata a duniyar da Zata shiga.

Kasa hawa titi tayi sbd Batasan Inda ta dosaba,
Batasan gurin waye Zata ba a wannan mummunan halin datake ciki,

Batada uwa Bata uba batada miji waye gareta Mai tsaya mata?

Samun kanta tayi da zaunawa bakin wata bishiya sbd kwakwalwarta datake neman Dena aiki.

Jaririyarta tafara kuka Wanda na tsananin zafin ranar dake dukansu ne

Yaye zanin datake dunqule aciki tayi ta Dan kalli fuskarta taga yanda fuskar tayi jajir take sbd azabar Rana
Sai alokacin taji zuciyarta data daskare tana narkewa da tausayin kanta dana jaririyar Dan haka batada zabi daya wuce ta tunkari gidansu salisu ko ummansa Zata karbesu tunda jikartace su taimaketa ta zauna gurinsu ta Rena Ayshatouh idan ko shekara tayi saita barta takoma gidansu idanma sbd itane su Yaya Umar suka koreta daga gida.

'yar qaramar jakar kayanta ta bude tafara duba kudin datake dasu.,

Dari uku da ashirin tagani take jikinta yakuma mutuwa saidai halinda zuciyarta take ciki Batajin akwai abinda zai fisa daci.,

Miqewa tayi ta qarasa bakin titi Anata kallonta sbd Jin yanda jaririya ke kuka sosai a jikinta Dan haka Bata tsaya juran napep ba ta tsayarda Mai mashin ta hau suka tafi.

Gabanta tsananta faduwa da shiga qunci yakeyi sbd hajiyar salisu ma batasan yaya zata karbesuba...

Mai mashin na ajiyeta kofar gidan ta Ciro dari da hamsin ta miqa Masa ta juya ta shige qaramar kofar gidan tana sake qamqame yarta jikinta.

Tun kafin ta qaraso ciki Yara suka fara Isa gurin hajiyar suka sanar Mata Hadiza tazo.

Dan shiru hajiyar tayi kafin ta kalli yaran ta korasu waje ta dawo da hankalinta kansu balaraba dake gidan ta sallamesu suka wuce inda zasu ta kofar baya batareda sun tsaya Gaisawa da Hadizan ba Dan dama a sama sama suke da ita tun salisu nada Rai bare yanzu da basuda alaqa da ita.

Da wata irin dasasshiyar sallama ta shigo hankali sbd muryarta ko fita batayi.

Da mamaki hajiya ta kalleta idanuwanta na sauka kan jaririyar dake hannun Hadizan.

Idanuwan Hadizan zuwa fuskarta ta kalla dakyau take tagane jegone tareda Hadizan Dan haka ta tattaro hankalinta da mamaki a bayyane kan fuskarta tace"

Hadiza¿
Kece nake gani?
Lafiya da Rana tsaka haka?
Ba zaman karban gaisuwar Aishatu akeba.

Kasa magana Hadiza tayi sbd jirin dake dibanta Dan haka a sukwane ta qaraso ta durqusa gaban hajiyar tareda sunkuyar dakai idanuwanta na sake rinewa.

Sake Shiga firgici hajiya tayi tana qin nuna taga jariri atareda hadizanba tasake cewa"

Hadiza nace lfy kuwa?
Kiyi mgana kikai shiru kina bani tsoro...

Dagowa Hadizan tayi tana kallon hajiyar sbd tasan bazatace bataga abinda ke hannuntaba
Idanma Bata ganiba bazatace batajin kukan da Ayshatouh ke tsalawaba.

Sunkuyar dakai tayi tareda bude jaririyar dakyau agaban hajiyar muryarta na a disashe da tsananin damuwa da qunci Mai daci tace"

Hajiya haihuwa nayi su Yaya Umar sukace nabar gida,
Bansan Inda zaniba sbd ko Abokai banda shine nataho Nan....

Dauke wuta hajiyar tayi daga zaune tana kallon Hadizan Baki sake ko fuskar jaririyar taqi kalla.

Qofa tafara kalla ta leqa tsakar gida taga ba kowa tadawo da sauri ta kalli Hadizan cikin tsananin mamaki, firgici da takaici Kai tsaye tace"

Me Zan Miki anan hadiza?
Haihuwafa kikace kinyi?
Haihuwa ba aure fa?
Wace qaddarace wannan takaiki ga wannan mummunan sakamakon? Shine Kuma Zaki zomun Nan?

Ko kunyar 'danki dake gidan Nan bakijiba kika kwaso jiki da jaririn shege kizomun anan?

To Kinga Hadiza tun kafin Raina ya baci Kuma tum kafin wani yaji tashi ki fice,

Mune mukafi kowa hauka a duniya ne dazamu Baki gurin zaman renon barna......

Rawa hannuwan Hadiza suka fara hankalinta yasake mummunan tashi tana kallon hajiya da idanuwanta jajir tace"

Dan Allah hajiya ki yarda Dani ki fahimceni
Kima kaini a dubani idan ana dubawa wallahi tallahi banyi kowace irin barnaba nasamu cikin Nan,
Wallahi cikin salisu ne......

Wata irin mummunan zabura hajiyar tayi tana kallon Hadiza a gigice sbd mamaki da baqin cikin zancenta Dan ta Gama raina Mata hankali kokuwa dai mahaukaciya ta dauketa?
Amma dai Bari ta tabbatar...kallonta tayi a Rikice tace wane salisun Hadiza?

Muryarta Bata fita sosai sbd shaqewar maqoshi tace"

Salisu baban Abdul....

Kasa magana hajiyar tayi ta rufe idonta daya fara sauyawa sbd tsananin bacin Rai da masifar Rainin da Hadiza tazo dashi Dan haka Bata buqatan ma Jin komai ta nuna Mata hanya tace"

Fice Hadiza kibar gabana Dan Allah.

Dagowa Hadiza tayi ta kalli hajiyar sai alokacin hawaye suka ciko jajayen idanuwanta suka fara gangarowa.

Magana takeson yi Amma zuciyarta tayi nauyi bazata iyaba sai wani irin quntataccen kuka Mai ciwo daya zuwar Mata.

Ganin ba tashi zataiba kada wani yashigo yagantama kokuma yaji haukar datake fada yasa hajiyar Kama hannayenta ta miqar tsaye tareda janta takaita har waje ta Kuma gargadeta akan sake zuwa da wata jaririyar gidan da sunan salisu abakinta.

Kuka sosai Hadiza keyi tanajin wani irin azababben ciwo a zuciyarta,
Jin takeyi kaman zuciyarta zata mutu,

Ganin mutanen dake wucewa sunfara Mata kallon mahaukaciya yasata Jan jiki tabar kofar gidan.

Tafiya kawai takeyi sbd Batasan Inda zataba,

Jin jaririyar tayi baccin wuya itama yasata tsayawa ta goyata taci gaba da tafiya.

Tafiya Mai nisa tayi wadda batamasan tayiba har Saida yamma tayi sosai ta nema bakin wani gidan abinci ta zauna tareda sauke jaririyarta ta saka cikin hijabinta tafara Bata nono.

Kasa Shan nono 'yar tayi sbd tuni ciwon zazzabin wahala ya rufeta sbd ba qaramar Rana sukashaba.

Fara jijjigata tayi tana sake cusa Mata nonon Amma Bata amsaba Dan haka ta maidata ta goya.

Shagon dake gefen gidan abincin ta qarasa ta siyo ruwan roba na sauran canjinta dasuka rage Takoma Inda ta baro ta zauna tasake saukoda 'yar ta bude ruwan ta ringa zubawa a murfin robar tana Bata.

Ruwan ma batasha saidai wasu sun shiga cikinta kadan...

Kuka jaririyar keyi sosai Wanda ya qarasa gigita Hadiza..
Batasan ya zataiba sbd kanta zazzabi da ciwone Mai qarfi a jikinta.

Gabanta radadi yake Mata sbd qarin haihuwa da rashin ruwan zafin gasa gurin ga doguwar tafiya cikin azabar Rana Dan haka itama take a gigice.

Kukan 'yar yasa Dole tabar gurin ganin hankalin jama'a yafara yawa kanta.

Cikin wasu mabarata dake gaba kadan bakin wasu super market taje ta zauna tana sake fama da Yar dake kuka har lokacin.

Nanma bata tsiraba sbd anfara Mata kallon zargi da 'yar
Silalewa tayi tabar gurin kafin ayi Mata dukan Satan 'ya takama hanya taci gaba da tafiya gashi duhun dare yafara Dan har anfito sallar magriba.

Tafiya Mai Dan tsayi takuma Yi taji bazata iyaba sbd radadi da azabar da tsakiyar cinyiyinta ke Mata,

Azabar datakeji tafi Mata naqudar haihuwar datayi sbd gurin ya goge sosai sbd tafiya Dan haka tasamu wasu shaguna da Yan gudun hijira suke ta zauna daga can gefe itama.

Ruwan robar data siyawa yarta itama taciro daqyar ta iya karban kadan ta shimfida zaninta agurin ta kwanta tana fidda numfashi daqyar jikinta na rawar sanyi.

Babu Wanda ya lura da ita sbd suma kowa ta kansa yakeyi Bata wani ba dan kowa agurin abin tausayine.

Yarta na dungule cikin jikinta itama tayi bacci.

Hadiza Batasan inda kanta yakeba sbd kusan suma tayi saida sanyin asuba da kukan yarta ya dawo da ita
Ta bude idanuwanta daqyar tana Neman tashi Amma takasa.

Daga kwancen ta sake rungume jaririyarta ta Ciro nono tasaka Mata a Baki.

Ana Gama sallar asuba duka mabarata da Yan gudun hijira dake gurin suka fara watsewa sbd baa barin Zama gurin da daddare kawai suke zuwa su kwanta da gari ya waye kowa yatafi gurin bara.

Daqyar ta iya daddafawa ta tashi tabar gurin
Tafiya kadan tayi tasamu guri ta zauna sbd bazata iyaba.

Anan gurin ta Rana ta fito ta sameta
Mutanen dake wucewa suka fara Bata sadaka sbd sun dauka Bata takeyi

Dayake tana buqatan taimakon ana bata haka ta ringa karba har Allah yasa ta hada 400 ta tashi daqyar ta siya ruwan zafi gurin me shayi ta Sha na hamsin ta siya wasu na hamsin din ta wankewa 'yarta jiki ta gogeta ta maida Mata kayanta da daudarsu da komai.

Har yamma tana garari a hanya Dan haka tasake komawa gidansu salisu
Hajiyarsa Bata tausayawa mataba tayi Mata korar wulaqanci harda munanan kalamai akan 'yarta Dan haka ta sake komawa Inda ta kwana jiya anan ta Kuma kwanciya.
Chapter 41 · 0% Book details