← Book details Inayah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 65

Sashe 18

Inayah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

MTN card👇
09134848107
*16*
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
Tana Isa bedroom dinta ta kwanta ko kallon Inda wayarta take bataiba.

Bata wani qin samun bacci ba,
Sosai tayi bacci kaman yanda ta saba saidai tana farkawa damuwar dake dabaibaye cikin ranta ta dawo Mata sabuwa fil harma wani 'dacin maqoshi takeji sbd tsananin damuwa da fargabar abinda zaije yadawo,

Tanajin wani irin tsananin bacin Rai da zafin abinda Zaid din yayi Mata da har takejin bazata taba iya mantawaba Amma ta wani bangaren tana cikin tsananin fargaba da tsoron rasashi sbd girman son datake Masa.

Tayi lattin sallah Dan haka alwala tafara yowa tazo tayi sallar asuba tukuna tayi adhkar.

Tana gamawa ta koma kan gadonta tashige bargo tana son komawa bacci.

Rufe idanuwanta tayi tana sake gyara kwanciyarta Amma takasa Jin dadin kwanciyar,

Sake juyawa tayi dayan banagren tana Dan yamutsa fuska cikin yanayi na qosawa.

Jin duk batajin dadin kwanciyar yasata yaye bargon datake rufe dashi tareda tashi zaune ta kalli wayarta dake kan bedside, takuma dauke Kai tana Dan sake yamutsa fuska.

Mintuna biyu ahakan kafin ta qarasa yaye bargon tayi gefe dashi tareda ziro qafafuwanta qasa tana daukar wayarta ta kunna ko duba wayar bataiba daga kunnawan darai ta ajiyeta Nan Inda ta dauka ta miqe tsaye tareda nufar Inda tarin jerin takalmanta suke jere Kaya guda,kusan babu designer shoe brand dinda batada masu zallar tsada.

Time ta kalla taga yanzuma 6:30 tayi Dan haka tasan har yanxu dadynta Yana geam,

Riga da wandon Nike ta saka black da Triple S Balenciaga sneakers farare ta fito ta nufi gym Dinsu dake gidan Wanda saika ratsa palon daya raba palonsu Dana Abbinta zaka Isa watadaccen gym din Mai girma da tsari.

Tana Isa knocking daya tayi ta tura kofar da kusan tafi karfinta sbd qarfin kifar tashiga tana gyara qaramar Vandanar dake kanta.

Sanye yake da black Lululemon wears na exercise,
Bench press yakeyi da nannauyan qarfe a hannayensa Yana dagawa da dawowa,

Shigowarta baisa ya dakataba Kuma Bai waiwayo ya kalli Wanda ta shigoba Dan yasan babu Mai shigowa Nan din kaf idan ba 'yarsaba.,

Cikin kauna da kulawa ta qaraso gurinsa tana cewa"

Good morning Abbi"

A natse ya qarasa abinda yakeyi ya ajiye qarfen tareda tashi zaune wasu qananun zufa abinda ya Gama suna gangara kan lafiyayyar fresh fatarsa ya kalleta lokacinda take daukan ruwa tana basa takuma cewa"

Abbi ka tashi lfy?

Idonta yafara kalla baiga alamar rashin bacci atareda itaba Dan haka Kai tsaye cikin nutsuwa da kulawa yace"

Morning Inayah,
Lfy kalau alhmdllh,
Me zakiyi da gymin yanzu?
kinason ki rage keda kike amarya?
Ko Kin manta kin daina zumudin auren ne tun yanzu?" ya qarasa cikin yanayi na Wasa da 'yar tasa tilo.

'yar qaramar dariya tayi tana hawa kan leg press machine tafara ahankali tana cewa"

Abbi naji banason auren Kuma yanzu
Banason tafiya nabar gida,
Abbi kullum zanyi missing naka,
Gskia Zaid zai ajeni a Inda zanna ganinka.

Murmushi kawai yasake ahankali Yana goge qananun zufansa da wata farar towel qarama yace"

Zaki Saba ahankali musamman idan kika Zama uwa,
And kafin can ma you will be busy with your work bazaki samu lokacin tunanin kewan gidaba.

Abbi duk da hakan nasan kullum sainayi kewanka,Dan Allah Abbi kace musu anan zasu ajiyeni.

Girgiza Mata Kai yayi Yana murmushin wautarta da har take cewa ta girma yanzu idan Yana Mata fadan wani abun,

Haryanzu jinjira ce shi agabansa Dan ko wannan auren Dan kawai ta nace tanaso ne yanzu yasa zaiyi Mata Amma tabbas da saita sake wayo da girma sosai
Aqalla saita fara aiki tasan ciwon kanta Dana rayuwama Dan kuwa haryanzu Batasan komai na rayuwaba,
Babu abinda tasani daga mahaifinta sai mahaifinta tukuna sauran abubuwan.

Tare suka qarasa gymin din suka fito itace mai surutu Yana saurarenta hankali kwance daga shi har ita skin Dinsu glowing kawai suke gasa ta tsantsar hutu da wadata kasancewar shi rigarsa armless sai dogon wando,
Itama rigarta qaramin hannu me da ita sai dogon wando.

Kowannensu hanyar dakinsa ya nufa,
Wanka tafara tubewa tayo ta fito kenan wayarta tahau ringing ta qarasa tana dubawa taga Zaid ne.

Wani zafin gaske ne ya taso Mata daga qasan zuciya,
Duk lokacinda sunan zaid ya fado ranta Jin take tamkar Zata Kama da wuta sbd tsananin zafin kishi da baqin ciki.

Jefar da wayar tayi tareda nufar gaban madubu tafara shiryawarta.

Oil ta shafa tareda moisturizer kadan ta fesa su spray da body mist dinta ta nufi closet.

Sai after 9 tafito sanye cikin fitted long sleeve gown kalar blue sai qaramar scarf nade akanta.

Dakin umma yaganah take kokarin Isa Amma taji kaman muryan Abbinta a dining room Yana waya Dan haka ta juya ta nufi dining din.

Shi da umma yaganah ne zaune Dan haka itama ta qaraso tana cewa"

Tun yanzu anfara ware ni a gidan Nan.

Umma yaganah ce tayi Yar dariyar Jin Dadi ganin Inayar ta sake
Dama Allah Allah take MAJEED yafita gidan kafin ya dagosu su samu sugani idan zasu iya kashe zancen iya tsakaninsu.

Ita harga Allah babbar damuwarta irin fushi Mai tsanani da MAJEED din zaiyi idan yaji 'yarsa da duk arzikinsa da zamansa busy Bai hanasa tsayawa yana ture komaiba Dan ginarda tarbiyarta tun tana jinjira har zuwa yanzu yaji sunje gidan saurayi tasan wlh ranar ransa qarshen bacin Rai zaije,
Hakama Kuma qarin abin bacin ran da baqin cikin yaji Inayar da bakinta tana fadar hannun Zaid acikin riga Yana latsa nonuwan wata,su kansu sun San ranar sai yanda Allah dai yayi dasu daga ita umman har Inayar.

Ata wani bangaren tasan Sarai Inayah Zata iya fadar hakan gaban Abbin nata.

Dan hakan yanzu ba qaramin farin cikin ganin Inayah ta sakeba tayi har Saida kusan Abbin yagane Amma dai baice komaiba har lokacin.

Breakfast sukai suka Gama ya fice zuwa aikinsa.

Yana fita Inayah ta tattaro bacin ran da baqin cikin dataketa dawainiyar boyewa cikin ranta kaman zai kasheta.

Bata wani tsaya dogon zanceba tacewa umma yaganah Zata gidansu Neesah tadawo Dan tanason Jin komai dalla dalla daga gareta idan ba hakanba zuciyarta tashiga tunani kala kala da zasu iya hallakata.

Sanin irin tsananin zafin kishi da Allah yayiwa Inayah yasa umma yaganah barinta zuwa gidansu Neesah din.

Tana barin gida batabi ta hanyar da saita bi ta anguwarsu Zaid kafin ta Isa gidansu Neesah ba Dan Bata buqatan ganin gidan ko kadan,
Jin take ta tsana gidan da anguwar gabaki daya.

Tana Isa gidansu Neesah itama Neesar na kokarin fitowa da motarta Zata gurin Inayah din.

Komawa ciki Neesah tayi da tata motar INAYAH taqarasa shigowa da tata motar sukai parking tare suka fito kusan lokaci daya.

Kallonta Neesah keyi lokacinda ta fito mota fuskarta duk babu walwala.

Cikin kulawa tace"

Hey babes,
Yaya?
Are you okay?

Wani kallo Inayah tai Mata tana qarasa Kama hannunta data miqo Mata tana cewa"

Nai Miki Kama da wadda take okay?

Kina tunanin zan Zama daidai bayan abinda idona ya ganarmin jiyan?

Ciki suka qarasa suna magana ahankali sbd rashin walwalar Inayah.

Momy na gurin dadyn Neesah Dan hakan Kai tsaye dakin Neesah suka wucewarsu.

Zama sukai Inayah na wurgi da handbag dinta da car key dinta ta kalli Neesah dake miqo Mata bowl din Candies tace"

are you for real?
Me zanyi da candies bayan 'dacin da zuciyata take ciki.

Ajiyar zuciya Neesah tayi tana Zama cikin sautin Mai mahimmanci tace"

Maganar 'dacin Rai ko baqin ciki bashine abinda yakamata ki fuskantaba,

Zaid dai wallahi Neman mata yake,
Nasha ganinsa da Amal a yanayi marasa kyan gani,
Nayi bibiyarsa Dan tabbatarwa Kuma na tabbatar Dan haka bawai maganar kishi ake ananba
Maganace ta ki nutsu kisan wanda Zaki aura da halayensa,

Bansan yaushe ya sauya yakoma hakan ba Amma a zahirance ya dade a wannan rayuwar da Amal Dan hakan maganar sauyawarsa lokaci daya zaiyi wuya....

Kasa magana Inayah tayi ta zubawa Neesah idanuwanta dasukai jajir sbd tsananin baqin ciki da zafin zuciya.

Cikin takaici da masifa tace"

Shine Baki taba fadanba?
Da banganiba da kaina ahakan Zaki Bari ayi auren nagama haukacewa a sonsa shikuma Yana can Yana kwanciya da wata macen?

Cikin damuwa Neesah tace"

Inayah Kona fada ba ganewa zakiyiba sbd idonki ya rufe akan Zaid,
Tayaya Kai tsaye zance Miki Zaid is sleeping with another woman?
Zaki yarda ne idan nafada?

Kalman "sleeping with another woman" shine yafi komai gigita dukkaninta Dan hakan Batasan lokacinda hawayen baqin ciki Mai qarfi suka fara gangaro mataba.

Sanyi jikin Neesah yayi ta matso kusada ita cikin tausasa murya tace"

Inayah wannan shine Namiji,
Duka wannan kadan ne idan baka nutsu kasamu mijin dakakeson more rayuwan aure dashi,

Inason aure nima kinsani sosai Amma Kuma bazan iya auren Wanda nakewa so irin hakan dakikewa Zaid ba sbd disappointments na cikin irin wannan son..

Gudu hawayenta suka qara sbd ba itace ta sawa kanta son Zaid ba Allah ne ya jarabceta da irin wannan son datake Masa,
Uwa uba ga zafin kishi datakeji Kamar ta hadiye zuciyarta ta mutu.

Rarrashinta Neesah tafara yi Amma Sam takasa Jin sassauci Dan hakan ta miqe tareda daukan Jakarta da key dinta tana nufar kofa.

Binta Neesah tayi tana cewa"

Babes Ina Zaki?

Cikin qunci tace"

Zanje naji daga bakinsa meyesa zaimun hakan.

No Inayah please karki Kuma zuwa gidansa sbd kada komai ya qarasa lalacewa,
Qazantar da baka ganiba tsaftane.

Bata sauraretaba tayi gaba tana cewa"

Idan bazakiba please kibarshi a iya.

Bazan iya Bari kije ke kadaiba Kuma ai dole zanbiki,
Bani key din I will drive.

Miqa Mata key din tayi tareda budewa ta shiga kafin Neesah din tashiga mazaunin driver ta tada motar suka fice daga gidan.

Tafiya suke zuwa gidan Amma babu wadda zuciyarta Bata bugawa acikinsu,
Neesah tasan tabbas sai sun samu Amal a gidan.,

INAYAH Kuma fargaba da shakkar samun mace take agidan tareda zaid sbd wannan karon bazata iya daurewaba komai zai iya faruwa Dan kuwa zuciyarta Zata iya bugawa.

Kuma ganin Zaid da wata tamkar qarasa buga zuciyarta ne zatai.

A slow Neesah ke tafiyar itama tanata adduar Allah yasa kada su tadda Zaid a gidanma gabaki daya bare wata Amal.
#MAMUH#
#AA MAJEED
#AYSHATOUH INAYAH
#MARRIAGE
#LOVE/ROMANCE

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_
Chapter 18 · 0% Book details