Sashe 4
Hira Da Matattu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*** *** ***
Sharifah ce ke tukawa, ta tsaya sannan ta fito daga cikin wata tsaleliyar motar. Daidai lokacin Nana Ahmad da Maryam Alqali su ma sun fito daga cikin motar Nana. Sai kawai aka yi kicibus da su da Sharifah. Ko ba su fada ba ta gane sun razana.
Maryam Alqali da yake 'yar karama ce sai ta labe a bayan Nana Ahmad ita ce barkekiya, Nana ta hau muzurai ita ba abin ta taka da gudu ba dan lokaci ya kure, su na daf da juna. Duk da an fada musu yanzu an tabbatar Sharifah mutum ce amma basu gama yarda ba.
Sharifah ta dube su sai ta yi murmushi ta ce " Su Nana manyan mata."
Ta wuce ta bar su anan a jikin mota su na makerketa. Nana ta fusata ta figo Maryam daga bayanta inda ta labe.
Ta ce " munafukar Allah sai ki labe a bayana saboda ke 'yar karama ce, ni kadai ake kullata gashi nan ta ga baqina har da wani habaici take yi min. Muddin ka ga Fatalwa tana habaici akwai magana kenan nan gaba. Innalilahi wa inna ilaihi rajuun. Shikenan na ga ta kaina."
Maryam ta yi dariya ta ce "ance ba fatalwa ba ce ba fa mutum ce an tabbatar da hakan."
Haushi ya sake rufe Nana ta ce " ai kin tabbatar da mutum din ce amma kika gudu kika buya a bayana. Ni da yake barkekiya ce babu in da zan labe ni ake gani ga shi nan ta kullace ni."
Su ka hau kan bene ofishin lauyoyi, Nana ta zo wajen babban yayanta Bar. Inuwa Ahmad ta rako Maryam zasu tattauna akan wani case da Maryam Alqali take so ta shigar.
Anan aka sake yin arangama da Sharifah tana zaune a reception itama tana jiran layi ya zo kanta za ta ga lauyanta Bar.Inuwa Ahmad yayan Nana Ahmad ba tare da kowannensu ya sani ba. Ashe waje daya su ka zo an sake cakuduwa.
Nan ma suka yi turus suka ji kamar su koma amma ba hali saboda Sharifah ta tsare su da idanuwan nan na ta masha Allah manya-manya. Ga kujerun da za su iya zama dole sai a kusa da Sharifah ne. Da alama yana ganawa da wasu mutane a cikin ofishin, dan haka dole su jira.
Kallon da Sharifah take yi mu su ya wuce na mutane dan ba ta ko qiftawa. Sun kasa gane dalilin wannan tsare su da idanuwan da ta ke yi.
Maryam ta sake daka tsalle ta koma ta maqale a bayan Nana, dan tafi ta tsawo da qiba da fadi, Idan ta labe a bayanta baa hango ta ko kadan, takaici ya kara kama Nana. Ta shiga zulumin shin ta je su gaisa da Sharifah ko itama ta share ta su kalli juma kawai.
Su na tsaye basu zauna ba duk da tayin da sakataren yake ta yi musu akan su zo su zauna amma suka ki zama. Su sun san dalilin da ya hana su zama, tsoron Sharifah ne.
Ana cikin wannan hali ne sai mutanen cikin ofishin suka fito, Sharifah ta tashi ta shiga sannan su Nana suka samu damar zama. Nana da Maryam sai fada ake yi saboda labewar da take yi a bayanta, Nana ta ce ta daina yi ma ta haka. Maryam ta sha aradu muddin ta ga abin buya wallahi sai ta buya a bayanta kuwa.
Sharifah ta dade a cikin ofishin Barista, su na ta tattaunawa da shi da alama case dinta babba ne. Ta fi awa guda sannan ta fito, har Nana ta shiga fargabar ko dai Sharifah ta bace tare da yayanta, ta ji kamar ta je ta leqa ta gani.
[3/1, 12:30 PM] Jamila Umar Tanko: 3
Sharifah ta fito daga ofis bayan ta gama, ta same su a zaune, ta kalle su suka kalle ta sannan ta fita. Su Nana ba su ji dadin wannan abinda ya faru ba, ya kamata ace sun yi ma ta magana duk da itama ba ta yi mu su magana ba ai amma tana da dalili tunda sun dauke ta fatalwa zata ji tsoron ta yi mu su magana don kada su baje da gudu. Sai dai sun rasa abinda za su zaba shin ita ce ko fatalwa ce?
Su ka shiga ofishin Barista da sauri bayan sun yi ma sa sallama, ko gaisawa basu yi ba Nana ta shiga jero masa tambayoyi.
" Yaya ka san wannan matar ashe, wacce ta fita yanzu?"
Ya ce "kwarai kuwa mun dade tare nine lauyanta duk da sai daga baya ta dawo wajena bayan ta gama shan wahala da wasu lauyoyin."
Nana da Maryam su ka hada ido sannan suka sami waje suka zauna. Nanah ta sake cewa "Yaya ka ce kun dade tare ko?"
Ya harare ta ya ce " ina ruwanki da mutanen da su ke aiki tare da ni ne? Menene matsalarki? Kin santa ne?"
Nanah ta gyara zama ta ce "akan me ake yin shari'a da ita? Ita ta kai kara ko ita aka kai kara?"
Wannan karon sai ya qi ba ta amsa, ransa ya baci har sai da fuskarsa ta nuna.
Ya ce "ku fadi abinda yake tafe da ku kawai,babu ruwanki da case din wasu."
Maryam ta gaishe shi sannan ta fara bayani. Shi kuma ya na sauraronta.
Su na fitowa Samha suka kira a waya, su ka shaida ma ta sun hadu da Sharifah a ofishin lauya amma sun kasa yi ma ta magana kuma har ta gane su na jin tsorona har yanzu.
Samha ta nuna bata ji dadi ba, basu kyauta ba. Sharifah a halin yanzu soyayya take bukata da kulawa, saboda ta rasa kusan kowa na ta, ta rasa komai.
Duk da ba ta kammala ba ta labarinta ba amma alamu sun nuna haka, kowa ya guje ta saboda an ganta da wahalar yara. Game da shari'ar ce ma baa san ko da wa suke yi ba. Shin Shariqah take nemowa hakkinta ne bayan ta rasu ko wani zalumci aka yi ma ta daban?
Nanah ta na dorawa Maryam laifi, Maryam na dorawa Nanah laifin cewa ita ce ta fara razana. Su ka yiwa Samha alqawari zasu sami lokaci su zo gidanta sai ta jagorance su zuwa gidan Sharifah su ba ta hakuri.
*** ***. ***
Samha na zaune sai ta ga kiran wayar Mamarta ya shigo wayarta, bayan ta amsa sun gaisa kamar yadda su ka saba.
Kwatsam sai Mama ta ce " Samha! Yanzu na ji wa'azi a radio yadda kika san da mu ake, game da Sharifah. Malam ya ce babu fatalwa a duniya, babu wanda ya mutu ya taba dawowa duniya. Mun yiwa yarinyar nan mummunan zato."
Samha ta ji dadi da jin kalaman da suka fito daga bakin Mama. Alhamdulullah.
Mama ta dora da cewa "idan kin sami lokaci ko ki je gidanta ko ta zo gidanki ki saurare ta ki ji meye matsalarta in sha Allah za mu taimaka ma ta idan bai fi karfinmu ba. Mahaifiyarsu mutuniyar kirki ce bana manta alkhairan da su ka yi mana a lokacin aurenki. Lokacin da komai ya cabe min, ba mu da kudi su ne masu kudi babu abinda ba su dafa sun kawo gidan nan ba kowa ya ci ya sha ya koshi a taron biki. Bayan haka kuma kayan dakinkin ma su suka siya mana abubuwa da yawa."
Samha ta gyada kai ta ce "kwarai kuwa Mama ban taba manta alkhairan bayin Allah nan ba. Mamarsu da su kansu, wallahi Mama ban taba mantawa da yiwa iyayen Sharifa addu'a ba har lokacin da ba ma tare, mun yi zumunci a baya sosai dan ba zan manta lokacin da Babansu yake zuwa mata visiting a sakandire ba, dukka kawayenta sai ya raba mana kudi da littattafai. In sha Allah zan sami lokaci in je gidanta, dan na san a yanzu dai ba zata zo gidana ba, dan tana da zuciya mun yi mata laifi akan abubuwan da mu ka yi zatonta da su. Ba ta ji dadi ba sam."
Su na kashe waya sai Samha ta ji hawaye yana ta sirnano ma ta na tausayin Sharifah.
Aliyu ya shigo ya iske ta na kuka, ya razana a tunaninsa ko mutuwa ma aka yi. Dakyar dai ta iya bashi labarin abinda ya faru tsakaninta da Mama, da labarin da su Nana suka ba ta cewa sun ga Sharifah a wajen lauya. Tabbas Sharifa tana buqatar kulawa, tana bukatar wani da zai tsaya a gefenta ya na karfafa ma ta guiwa ko da baa taimake ta da kudi ba.
Tambayar da Aliyu ya yi ita ce "ina mijinta yake yanzu ko basa tare?"
Samha ta ce "tare da kai fa ta ba mu labari, ba mu ji karshen labarin ba amma kamar da alama basa tare dan tana ta ambaton rashin kirkinsa. Ba ta taba jin dadin zama da shi ba."
Aliyu ya tambaye ta "menene abin yi yanzu?"
Ta ce su Nana sun ce zasu sami dama su zo ta jagorance su zuwa gida Sharifah dan su ba ta hakuri. Ba su saka rana ba dai amma zasu zo.
Ya ce duk ranar da suka zo ya bata izini ta je koda ba ya gari. Samha ta ji dadi ta yi godiya sosai.
Ta shiga tunano irin abincin da Sharifah ta fi so idan zasu je sai ta dafa ma ta ta kai ma ta. Dan ta san ita da yaran za su ji dadi a kalla zasu ga an kula su.
Sharifah ce ke tukawa, ta tsaya sannan ta fito daga cikin wata tsaleliyar motar. Daidai lokacin Nana Ahmad da Maryam Alqali su ma sun fito daga cikin motar Nana. Sai kawai aka yi kicibus da su da Sharifah. Ko ba su fada ba ta gane sun razana.
Maryam Alqali da yake 'yar karama ce sai ta labe a bayan Nana Ahmad ita ce barkekiya, Nana ta hau muzurai ita ba abin ta taka da gudu ba dan lokaci ya kure, su na daf da juna. Duk da an fada musu yanzu an tabbatar Sharifah mutum ce amma basu gama yarda ba.
Sharifah ta dube su sai ta yi murmushi ta ce " Su Nana manyan mata."
Ta wuce ta bar su anan a jikin mota su na makerketa. Nana ta fusata ta figo Maryam daga bayanta inda ta labe.
Ta ce " munafukar Allah sai ki labe a bayana saboda ke 'yar karama ce, ni kadai ake kullata gashi nan ta ga baqina har da wani habaici take yi min. Muddin ka ga Fatalwa tana habaici akwai magana kenan nan gaba. Innalilahi wa inna ilaihi rajuun. Shikenan na ga ta kaina."
Maryam ta yi dariya ta ce "ance ba fatalwa ba ce ba fa mutum ce an tabbatar da hakan."
Haushi ya sake rufe Nana ta ce " ai kin tabbatar da mutum din ce amma kika gudu kika buya a bayana. Ni da yake barkekiya ce babu in da zan labe ni ake gani ga shi nan ta kullace ni."
Su ka hau kan bene ofishin lauyoyi, Nana ta zo wajen babban yayanta Bar. Inuwa Ahmad ta rako Maryam zasu tattauna akan wani case da Maryam Alqali take so ta shigar.
Anan aka sake yin arangama da Sharifah tana zaune a reception itama tana jiran layi ya zo kanta za ta ga lauyanta Bar.Inuwa Ahmad yayan Nana Ahmad ba tare da kowannensu ya sani ba. Ashe waje daya su ka zo an sake cakuduwa.
Nan ma suka yi turus suka ji kamar su koma amma ba hali saboda Sharifah ta tsare su da idanuwan nan na ta masha Allah manya-manya. Ga kujerun da za su iya zama dole sai a kusa da Sharifah ne. Da alama yana ganawa da wasu mutane a cikin ofishin, dan haka dole su jira.
Kallon da Sharifah take yi mu su ya wuce na mutane dan ba ta ko qiftawa. Sun kasa gane dalilin wannan tsare su da idanuwan da ta ke yi.
Maryam ta sake daka tsalle ta koma ta maqale a bayan Nana, dan tafi ta tsawo da qiba da fadi, Idan ta labe a bayanta baa hango ta ko kadan, takaici ya kara kama Nana. Ta shiga zulumin shin ta je su gaisa da Sharifah ko itama ta share ta su kalli juma kawai.
Su na tsaye basu zauna ba duk da tayin da sakataren yake ta yi musu akan su zo su zauna amma suka ki zama. Su sun san dalilin da ya hana su zama, tsoron Sharifah ne.
Ana cikin wannan hali ne sai mutanen cikin ofishin suka fito, Sharifah ta tashi ta shiga sannan su Nana suka samu damar zama. Nana da Maryam sai fada ake yi saboda labewar da take yi a bayanta, Nana ta ce ta daina yi ma ta haka. Maryam ta sha aradu muddin ta ga abin buya wallahi sai ta buya a bayanta kuwa.
Sharifah ta dade a cikin ofishin Barista, su na ta tattaunawa da shi da alama case dinta babba ne. Ta fi awa guda sannan ta fito, har Nana ta shiga fargabar ko dai Sharifah ta bace tare da yayanta, ta ji kamar ta je ta leqa ta gani.
[3/1, 12:30 PM] Jamila Umar Tanko: 3
Sharifah ta fito daga ofis bayan ta gama, ta same su a zaune, ta kalle su suka kalle ta sannan ta fita. Su Nana ba su ji dadin wannan abinda ya faru ba, ya kamata ace sun yi ma ta magana duk da itama ba ta yi mu su magana ba ai amma tana da dalili tunda sun dauke ta fatalwa zata ji tsoron ta yi mu su magana don kada su baje da gudu. Sai dai sun rasa abinda za su zaba shin ita ce ko fatalwa ce?
Su ka shiga ofishin Barista da sauri bayan sun yi ma sa sallama, ko gaisawa basu yi ba Nana ta shiga jero masa tambayoyi.
" Yaya ka san wannan matar ashe, wacce ta fita yanzu?"
Ya ce "kwarai kuwa mun dade tare nine lauyanta duk da sai daga baya ta dawo wajena bayan ta gama shan wahala da wasu lauyoyin."
Nana da Maryam su ka hada ido sannan suka sami waje suka zauna. Nanah ta sake cewa "Yaya ka ce kun dade tare ko?"
Ya harare ta ya ce " ina ruwanki da mutanen da su ke aiki tare da ni ne? Menene matsalarki? Kin santa ne?"
Nanah ta gyara zama ta ce "akan me ake yin shari'a da ita? Ita ta kai kara ko ita aka kai kara?"
Wannan karon sai ya qi ba ta amsa, ransa ya baci har sai da fuskarsa ta nuna.
Ya ce "ku fadi abinda yake tafe da ku kawai,babu ruwanki da case din wasu."
Maryam ta gaishe shi sannan ta fara bayani. Shi kuma ya na sauraronta.
Su na fitowa Samha suka kira a waya, su ka shaida ma ta sun hadu da Sharifah a ofishin lauya amma sun kasa yi ma ta magana kuma har ta gane su na jin tsorona har yanzu.
Samha ta nuna bata ji dadi ba, basu kyauta ba. Sharifah a halin yanzu soyayya take bukata da kulawa, saboda ta rasa kusan kowa na ta, ta rasa komai.
Duk da ba ta kammala ba ta labarinta ba amma alamu sun nuna haka, kowa ya guje ta saboda an ganta da wahalar yara. Game da shari'ar ce ma baa san ko da wa suke yi ba. Shin Shariqah take nemowa hakkinta ne bayan ta rasu ko wani zalumci aka yi ma ta daban?
Nanah ta na dorawa Maryam laifi, Maryam na dorawa Nanah laifin cewa ita ce ta fara razana. Su ka yiwa Samha alqawari zasu sami lokaci su zo gidanta sai ta jagorance su zuwa gidan Sharifah su ba ta hakuri.
*** ***. ***
Samha na zaune sai ta ga kiran wayar Mamarta ya shigo wayarta, bayan ta amsa sun gaisa kamar yadda su ka saba.
Kwatsam sai Mama ta ce " Samha! Yanzu na ji wa'azi a radio yadda kika san da mu ake, game da Sharifah. Malam ya ce babu fatalwa a duniya, babu wanda ya mutu ya taba dawowa duniya. Mun yiwa yarinyar nan mummunan zato."
Samha ta ji dadi da jin kalaman da suka fito daga bakin Mama. Alhamdulullah.
Mama ta dora da cewa "idan kin sami lokaci ko ki je gidanta ko ta zo gidanki ki saurare ta ki ji meye matsalarta in sha Allah za mu taimaka ma ta idan bai fi karfinmu ba. Mahaifiyarsu mutuniyar kirki ce bana manta alkhairan da su ka yi mana a lokacin aurenki. Lokacin da komai ya cabe min, ba mu da kudi su ne masu kudi babu abinda ba su dafa sun kawo gidan nan ba kowa ya ci ya sha ya koshi a taron biki. Bayan haka kuma kayan dakinkin ma su suka siya mana abubuwa da yawa."
Samha ta gyada kai ta ce "kwarai kuwa Mama ban taba manta alkhairan bayin Allah nan ba. Mamarsu da su kansu, wallahi Mama ban taba mantawa da yiwa iyayen Sharifa addu'a ba har lokacin da ba ma tare, mun yi zumunci a baya sosai dan ba zan manta lokacin da Babansu yake zuwa mata visiting a sakandire ba, dukka kawayenta sai ya raba mana kudi da littattafai. In sha Allah zan sami lokaci in je gidanta, dan na san a yanzu dai ba zata zo gidana ba, dan tana da zuciya mun yi mata laifi akan abubuwan da mu ka yi zatonta da su. Ba ta ji dadi ba sam."
Su na kashe waya sai Samha ta ji hawaye yana ta sirnano ma ta na tausayin Sharifah.
Aliyu ya shigo ya iske ta na kuka, ya razana a tunaninsa ko mutuwa ma aka yi. Dakyar dai ta iya bashi labarin abinda ya faru tsakaninta da Mama, da labarin da su Nana suka ba ta cewa sun ga Sharifah a wajen lauya. Tabbas Sharifa tana buqatar kulawa, tana bukatar wani da zai tsaya a gefenta ya na karfafa ma ta guiwa ko da baa taimake ta da kudi ba.
Tambayar da Aliyu ya yi ita ce "ina mijinta yake yanzu ko basa tare?"
Samha ta ce "tare da kai fa ta ba mu labari, ba mu ji karshen labarin ba amma kamar da alama basa tare dan tana ta ambaton rashin kirkinsa. Ba ta taba jin dadin zama da shi ba."
Aliyu ya tambaye ta "menene abin yi yanzu?"
Ta ce su Nana sun ce zasu sami dama su zo ta jagorance su zuwa gida Sharifah dan su ba ta hakuri. Ba su saka rana ba dai amma zasu zo.
Ya ce duk ranar da suka zo ya bata izini ta je koda ba ya gari. Samha ta ji dadi ta yi godiya sosai.
Ta shiga tunano irin abincin da Sharifah ta fi so idan zasu je sai ta dafa ma ta ta kai ma ta. Dan ta san ita da yaran za su ji dadi a kalla zasu ga an kula su.