Sashe 16
Gammon Rama Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ba zan tsaya ba! Ka ƙyale ni na tafi tun da ba ni da sauran amfani a rayuwarka. Dama an faɗa mini tamkar baiwa haka nake, tun da babu wata mamora a gare ni saboda ni juya ce."
Rakiya ta furta masa a fusace cikin ɗaga murya, waigawa ya yi ya ga babu mutane a ƙofar gidan nasu sai wani matashi guda ɗaya da ya zo wucewa. Malam Hasan ya sauke ajiyar zuciya, ya yi ƙasa da murya ya ce.
"Don Allah ki daina É—aga murya kada mutane su ji, ki zo ki wuce gidan Kawu yanzu a daren nan ina za ki je."
"Zan tafi duk inda ya yi daidai da rayuwata, ka rabu da ni Hasan babu inda zan je." Rakiya tana gama maganar ta cigaba da tafiya, duk yadda Malam Hasan ya so ya dakatar da ita fir ta ƙi amincewa. Don haka ya riƙo hannunta da niyyar su koma, a haukace ta fizge hannunta cikin ƙaraji ta ce.
"Ka rabu da ni, ba na son ganinka ba na ƙaunarka..."
Tass! Ya tsinke ta da mari, cike da ƙunan zuciya ta riƙe kuncinta tana kallonsa hawaye yana zuba, ta ɗauki lokaci a haka cikin sassanyar murya ta ce.
"Na gode da wannan tukwicin da ka yi mini, amma ka sani ko kashe ni za ka yi ba zan koma cikin ahalinka ba."
Ta yi yunƙurin ƙwacewa ya janyo ta, ya saka hannuwa biyu ya matse ta a jikinsa. Sunkuyar da kai ya yi har sai da suka fara jin numfashin junansu, cikin muryar nadama ya ce.
"Don Allah ki yi haƙuri, a tsakanina da ke ba na son na ji kalman ƙiyayya da kike furta mini. Yanzu ki zo mu je ki gidan Kawu."
Furzar da iska mai zafi ta yi ta girgiza masa kai ta ce.
"Ba za ni ba, ka ƙyale ni babu inda zan je."
Sai da Malam Hasan ya kai ruwa rana sannan ta amince ta bi shi suka wuce gidan Kawu Sani. Lokacin da suka ƙarasa Kawu Sani yana shirin rufe gida, yana ganinsu ya ce.
"Hasan lafiya na ganku a daren nan? Hala Kulu ce ta sake yin wani rashin mutumcin?"
Malam Hasan ya ɗan sosa kai ya ce, "Kawu maganar tana da ɗan tsayi, yanzu dai Rakiya za ta kwana a nan idan Allah Ya kaimu safiya zan dawo sai mu tattauna." Jinjina kai Kawu Sani ya yi ya ce, "Ikon Allah, Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan masifar." Suka amsa da Amin, Har Malam Hasan ya juya zai tafi Kawu ya ce. "Hasan idan ka san matsalar nan ta haɗa da su Kulu, to kana komawa ka ce gobe da sassafe ina son ganinsu ku dawo tare." Hasan ya amsa masa sannan ya tafi, bayan tafiyarsa Kawu da matarsa sun jima suna tausar Rakiya da ba ta baki, sannan suka bata makwamci ta kwanta.
Malam Hasan yana komawa gida a inda ya bar su Inna a nan ya koma ya same su, Inna tana ganinsa ta taɓe baki ta ce.
"To gantalalle, bayan ka sake ta uban me ka bi ta ka faÉ—a mata."
Shiru Malam Hasan ya yi yana jin zuciyarsa babu daÉ—i, Inna ta É—ora da cewa.
"Ai wallahi tun da har muka rabu da jaraba kun rabu kenan, na san halinka da nacin tsiya kana iya dawo da ita..."
"Inna Kawu yana son ganinku gobe idan Allah Ya kaimu."
Malam Hasan ya furta yana katse ta, riƙe baki Inna ta yi ta ce.
"Ai ƙara ta kuka kai kenan ko? To Allah Ya kaimu ai duk wacca za a yi sai dai ayi ta ta ƙare. " Malam Hasan bai tanka mata ba ya miƙe ya shiga ɗaki, da yake Zuwaira ta san ba ta shuka abin arziki ba ko magana ba ta yi masa ba, saboda yadda ya hautsine musu tsoron tanka masa take ji.
Washegari da sassafe su Inna suka dira a gidan Kawu, bayan an gaisa a nan ne ya nemi jin ba'asin abin da ya faru. Nan take Rakiya ta zayyane duk abin da ya faru, cike da jin haushi Kawu ya É—auki hularsa ya jefa wa Zuwaira ya ce. "Yanzu Zuwaira rashin mutumcin naki har ya kai haka? Rakiyan ce za ta yi miki wanki har kike zaginta?"
Inna da ta gama cika fam ta ce, "To amma ai ka ji ɗayan ɓangaren indai ba son kai za ka yi..."
"Ke dallah rufe mini baki, kin girma ga yawan shekarun amma babu hankali." Kawu ya katse Inna, Rakiya ta saki murmushin takaici ta ce.
"Kawu ni dai a wurina komai ya wuce, dama fata na ya ba ni takarda ta kuma AlhamduLillah ya sake ni jiya."
Malam Hasan yana jin haka ya yi zaraf ya ce, "Ban saki matata ba Kawu, takardar da na ba ta jiya ba ta saki ba ce ta ban haƙuri ce."
"Ni kuma gaskiya na gaji da zaman gidanka, domin mahaifiyarka da matarka sun mayar da ni baiwa ni ma kuma 'ya ce kamar kowa." Inna ta yi mamakin jin furucin Rakiya, nan Kawu da malam Hasan suka shiga ba ta haƙuri. Kafin Rakiya ta haƙura sai da ya tabbatar musu da cewar daga wannan ranar babu aikin Zuwaira da za ta sake ɗauka. Hatta wankn Inna ta daina idan ba ita ta yi niyya ba, yadda su Inna suka ga Rakiya ta fitsare idonta tana faɗar maganganu ya sa har suka ji shakkunta. Sai da Kawu ya yi musu faɗa da nasiha sannan suka wuce gida Rakiya sai harare-harare take tana shan kunu.
Tun bayan da wannan al'amarin ya faru Rakiya ta samu 'yancin kai a cikin gidan, daga Inna har Zuwaira babu mai shiga sabgarta. Ita ma harkokinta take yi cikin kwanciyar hankali, kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci ta samu nutsuwa don har kiɓa ta yi. Ita kuma Zuwaira ta cigaba da feleƙe tana laulayin cikinta, yau ta tsiro da wannan gobe ta tsiro da wannan. Da gayya take kiran Malam Hasan idan yana ɗakin Rakiya ta ce masa wani abin take son ci, ko ta fito tsakar gida ta yi ta amaye-amayen ƙarya har sai Inna ta ƙwala masa kira ya fito. Daga ƙarshe ma sai ta tsiri cewa tana gane-gane a ɗakinta, don kada Malam Hasan ya zargi ƙarya take har da rana ko safiya haka take ihu ta ce ta ga giftawar mutum ko ta ce ta ji magana ko motsi a ɗakinta. Hakan bai taɓa damun Rakiya ba, don wani lokacin da kanta take saka shi ya tafi wurin Zuwairat ya kwana da ita idan makircin nata ya motsa.
Da yake Inna tana sana'ar sayar da koko da kunu da safe, sai Rakiya ta fara sana'ar ƙosai da wainar gero kuma cikin hukuncin Ubangiji tas suke ƙarewa. Zuwaira tana ƙyalla ido da ta ga haka, sai ta tsiri aman ƙarya da safe ta ce warin suyar ƙosai da waina ne ba ta so. Shi kuma Malam Hasan ya ce ba zai dakatar da Rakiya ba, kuma da ta yi wa Inna ƙorafi sai ta ga ba ta ɗauki wani hukunci ba. Da ta ga makirci ba zai kai ta ba, sai ta zari bin gidajen malamai da bokaye.
"Malam na yi yawo gidan malamai da dama, amma kusan duka kuɗina suke ci babu wata biyan buƙata a kan kishiyata. Don haka aka kwatanto mini wurinka, na ce zan gwada nan na gani."
Zuwaira ta furta wa mutumin, wanda ya fi kama da riƙaƙƙen ɗan bori. Daga shi sai wani ganye a ƙugunsa, wuyansa, hannuwansa da tsintsiyar ƙafarsa duka sanye yake da wuri. Kansa cike yake da wani irin ƙazamin gashi marar tsafta, kallo ɗaya mai ƙyanƙyami zai yi masa ya ji zuciyarsa tana tashi musamman idan warin jikinsa ya daki hancin mutum.
"Ni ba irin jabun malaman da kike zuwa wurinsu ba ne, kuma zan ci ki gyara ni ba malami ba ne. Ni boka ne taɓaɓɓe, ke ma kuma taɓaɓɓiya ce. Ki sa a ranki buƙatarki ta gama biya, saboda kin zo ne a kan kishiyarki. Me kike son ki yi mata, nakasa ta kike so ayi ko kuwa kashe ta zan yi. Domin ni ina kashewa, haukatawa kuma ina nakasawa amma da ikon Allah."
Bokan ya furta mata yana zuba mitsitsin idanunsa a kanta, tsuru Zuwaira ta yi ta shiga zare ido jin bokan ya ninka ta rashin imani. Jiki yana rawa ta ce.
"Ni kawai so nake.a datse alaƙarta da mijinmu, wallahi ba na son wani abu ya cigaba da shiga tsakaninsu. Amma ina son a ɓullo ta sigar da wani ba zai zarge ni ba, idan na ga wannan ya ci zan dawo ayi mini wani daban."
"Idan na lura ke ƙaramar sheɗaniya ce, har yanzu da sauran imani a zuciyarki. Amma tun da kika zo wurina dole mu halaka gabaɗaya, zan yi miki yadda kike so kuma babu wanda zai zarge ki. Ungo riƙe wannan."
Ya ƙarasa furucin yana miƙa mata wani garin magani da aka dama shi da ruwan sihiri a cikin farar leda.
"Ki tabbatar wannan maganin ya taɓa jikinta, amfaninsa a kan mutum ɗaya ne. Indai ya taɓa mutum ɗaya kowaye, to ko ya sake taɓa wani ya riga da ya tashi daga aiki. Ki yaye don kada a samu matsala, idan kika shafa mata shi duk bayan magriba Aljani Furzum zai dinga saka ta nannauyan bacci, ba shi zai ƙyale ta ba sai gari ya waye. Kuma duk tashin da za a yi mata ba za ta tashi ba, garin maganin mun haɗa shi ne da ruwan wankan gawa da kuma iccan kabari." Hannun Zuwaira yana rawa ta miƙa hannu ta karɓa sannan ta ce.
"Godiya nake boka Lado. Nawa ne abin da zan biya?"
Rakiya ta furta masa a fusace cikin ɗaga murya, waigawa ya yi ya ga babu mutane a ƙofar gidan nasu sai wani matashi guda ɗaya da ya zo wucewa. Malam Hasan ya sauke ajiyar zuciya, ya yi ƙasa da murya ya ce.
"Don Allah ki daina É—aga murya kada mutane su ji, ki zo ki wuce gidan Kawu yanzu a daren nan ina za ki je."
"Zan tafi duk inda ya yi daidai da rayuwata, ka rabu da ni Hasan babu inda zan je." Rakiya tana gama maganar ta cigaba da tafiya, duk yadda Malam Hasan ya so ya dakatar da ita fir ta ƙi amincewa. Don haka ya riƙo hannunta da niyyar su koma, a haukace ta fizge hannunta cikin ƙaraji ta ce.
"Ka rabu da ni, ba na son ganinka ba na ƙaunarka..."
Tass! Ya tsinke ta da mari, cike da ƙunan zuciya ta riƙe kuncinta tana kallonsa hawaye yana zuba, ta ɗauki lokaci a haka cikin sassanyar murya ta ce.
"Na gode da wannan tukwicin da ka yi mini, amma ka sani ko kashe ni za ka yi ba zan koma cikin ahalinka ba."
Ta yi yunƙurin ƙwacewa ya janyo ta, ya saka hannuwa biyu ya matse ta a jikinsa. Sunkuyar da kai ya yi har sai da suka fara jin numfashin junansu, cikin muryar nadama ya ce.
"Don Allah ki yi haƙuri, a tsakanina da ke ba na son na ji kalman ƙiyayya da kike furta mini. Yanzu ki zo mu je ki gidan Kawu."
Furzar da iska mai zafi ta yi ta girgiza masa kai ta ce.
"Ba za ni ba, ka ƙyale ni babu inda zan je."
Sai da Malam Hasan ya kai ruwa rana sannan ta amince ta bi shi suka wuce gidan Kawu Sani. Lokacin da suka ƙarasa Kawu Sani yana shirin rufe gida, yana ganinsu ya ce.
"Hasan lafiya na ganku a daren nan? Hala Kulu ce ta sake yin wani rashin mutumcin?"
Malam Hasan ya ɗan sosa kai ya ce, "Kawu maganar tana da ɗan tsayi, yanzu dai Rakiya za ta kwana a nan idan Allah Ya kaimu safiya zan dawo sai mu tattauna." Jinjina kai Kawu Sani ya yi ya ce, "Ikon Allah, Allah Ya kawo mana ƙarshen wannan masifar." Suka amsa da Amin, Har Malam Hasan ya juya zai tafi Kawu ya ce. "Hasan idan ka san matsalar nan ta haɗa da su Kulu, to kana komawa ka ce gobe da sassafe ina son ganinsu ku dawo tare." Hasan ya amsa masa sannan ya tafi, bayan tafiyarsa Kawu da matarsa sun jima suna tausar Rakiya da ba ta baki, sannan suka bata makwamci ta kwanta.
Malam Hasan yana komawa gida a inda ya bar su Inna a nan ya koma ya same su, Inna tana ganinsa ta taɓe baki ta ce.
"To gantalalle, bayan ka sake ta uban me ka bi ta ka faÉ—a mata."
Shiru Malam Hasan ya yi yana jin zuciyarsa babu daÉ—i, Inna ta É—ora da cewa.
"Ai wallahi tun da har muka rabu da jaraba kun rabu kenan, na san halinka da nacin tsiya kana iya dawo da ita..."
"Inna Kawu yana son ganinku gobe idan Allah Ya kaimu."
Malam Hasan ya furta yana katse ta, riƙe baki Inna ta yi ta ce.
"Ai ƙara ta kuka kai kenan ko? To Allah Ya kaimu ai duk wacca za a yi sai dai ayi ta ta ƙare. " Malam Hasan bai tanka mata ba ya miƙe ya shiga ɗaki, da yake Zuwaira ta san ba ta shuka abin arziki ba ko magana ba ta yi masa ba, saboda yadda ya hautsine musu tsoron tanka masa take ji.
Washegari da sassafe su Inna suka dira a gidan Kawu, bayan an gaisa a nan ne ya nemi jin ba'asin abin da ya faru. Nan take Rakiya ta zayyane duk abin da ya faru, cike da jin haushi Kawu ya É—auki hularsa ya jefa wa Zuwaira ya ce. "Yanzu Zuwaira rashin mutumcin naki har ya kai haka? Rakiyan ce za ta yi miki wanki har kike zaginta?"
Inna da ta gama cika fam ta ce, "To amma ai ka ji ɗayan ɓangaren indai ba son kai za ka yi..."
"Ke dallah rufe mini baki, kin girma ga yawan shekarun amma babu hankali." Kawu ya katse Inna, Rakiya ta saki murmushin takaici ta ce.
"Kawu ni dai a wurina komai ya wuce, dama fata na ya ba ni takarda ta kuma AlhamduLillah ya sake ni jiya."
Malam Hasan yana jin haka ya yi zaraf ya ce, "Ban saki matata ba Kawu, takardar da na ba ta jiya ba ta saki ba ce ta ban haƙuri ce."
"Ni kuma gaskiya na gaji da zaman gidanka, domin mahaifiyarka da matarka sun mayar da ni baiwa ni ma kuma 'ya ce kamar kowa." Inna ta yi mamakin jin furucin Rakiya, nan Kawu da malam Hasan suka shiga ba ta haƙuri. Kafin Rakiya ta haƙura sai da ya tabbatar musu da cewar daga wannan ranar babu aikin Zuwaira da za ta sake ɗauka. Hatta wankn Inna ta daina idan ba ita ta yi niyya ba, yadda su Inna suka ga Rakiya ta fitsare idonta tana faɗar maganganu ya sa har suka ji shakkunta. Sai da Kawu ya yi musu faɗa da nasiha sannan suka wuce gida Rakiya sai harare-harare take tana shan kunu.
Tun bayan da wannan al'amarin ya faru Rakiya ta samu 'yancin kai a cikin gidan, daga Inna har Zuwaira babu mai shiga sabgarta. Ita ma harkokinta take yi cikin kwanciyar hankali, kallo ɗaya za ka yi mata ka fahimci ta samu nutsuwa don har kiɓa ta yi. Ita kuma Zuwaira ta cigaba da feleƙe tana laulayin cikinta, yau ta tsiro da wannan gobe ta tsiro da wannan. Da gayya take kiran Malam Hasan idan yana ɗakin Rakiya ta ce masa wani abin take son ci, ko ta fito tsakar gida ta yi ta amaye-amayen ƙarya har sai Inna ta ƙwala masa kira ya fito. Daga ƙarshe ma sai ta tsiri cewa tana gane-gane a ɗakinta, don kada Malam Hasan ya zargi ƙarya take har da rana ko safiya haka take ihu ta ce ta ga giftawar mutum ko ta ce ta ji magana ko motsi a ɗakinta. Hakan bai taɓa damun Rakiya ba, don wani lokacin da kanta take saka shi ya tafi wurin Zuwairat ya kwana da ita idan makircin nata ya motsa.
Da yake Inna tana sana'ar sayar da koko da kunu da safe, sai Rakiya ta fara sana'ar ƙosai da wainar gero kuma cikin hukuncin Ubangiji tas suke ƙarewa. Zuwaira tana ƙyalla ido da ta ga haka, sai ta tsiri aman ƙarya da safe ta ce warin suyar ƙosai da waina ne ba ta so. Shi kuma Malam Hasan ya ce ba zai dakatar da Rakiya ba, kuma da ta yi wa Inna ƙorafi sai ta ga ba ta ɗauki wani hukunci ba. Da ta ga makirci ba zai kai ta ba, sai ta zari bin gidajen malamai da bokaye.
"Malam na yi yawo gidan malamai da dama, amma kusan duka kuɗina suke ci babu wata biyan buƙata a kan kishiyata. Don haka aka kwatanto mini wurinka, na ce zan gwada nan na gani."
Zuwaira ta furta wa mutumin, wanda ya fi kama da riƙaƙƙen ɗan bori. Daga shi sai wani ganye a ƙugunsa, wuyansa, hannuwansa da tsintsiyar ƙafarsa duka sanye yake da wuri. Kansa cike yake da wani irin ƙazamin gashi marar tsafta, kallo ɗaya mai ƙyanƙyami zai yi masa ya ji zuciyarsa tana tashi musamman idan warin jikinsa ya daki hancin mutum.
"Ni ba irin jabun malaman da kike zuwa wurinsu ba ne, kuma zan ci ki gyara ni ba malami ba ne. Ni boka ne taɓaɓɓe, ke ma kuma taɓaɓɓiya ce. Ki sa a ranki buƙatarki ta gama biya, saboda kin zo ne a kan kishiyarki. Me kike son ki yi mata, nakasa ta kike so ayi ko kuwa kashe ta zan yi. Domin ni ina kashewa, haukatawa kuma ina nakasawa amma da ikon Allah."
Bokan ya furta mata yana zuba mitsitsin idanunsa a kanta, tsuru Zuwaira ta yi ta shiga zare ido jin bokan ya ninka ta rashin imani. Jiki yana rawa ta ce.
"Ni kawai so nake.a datse alaƙarta da mijinmu, wallahi ba na son wani abu ya cigaba da shiga tsakaninsu. Amma ina son a ɓullo ta sigar da wani ba zai zarge ni ba, idan na ga wannan ya ci zan dawo ayi mini wani daban."
"Idan na lura ke ƙaramar sheɗaniya ce, har yanzu da sauran imani a zuciyarki. Amma tun da kika zo wurina dole mu halaka gabaɗaya, zan yi miki yadda kike so kuma babu wanda zai zarge ki. Ungo riƙe wannan."
Ya ƙarasa furucin yana miƙa mata wani garin magani da aka dama shi da ruwan sihiri a cikin farar leda.
"Ki tabbatar wannan maganin ya taɓa jikinta, amfaninsa a kan mutum ɗaya ne. Indai ya taɓa mutum ɗaya kowaye, to ko ya sake taɓa wani ya riga da ya tashi daga aiki. Ki yaye don kada a samu matsala, idan kika shafa mata shi duk bayan magriba Aljani Furzum zai dinga saka ta nannauyan bacci, ba shi zai ƙyale ta ba sai gari ya waye. Kuma duk tashin da za a yi mata ba za ta tashi ba, garin maganin mun haɗa shi ne da ruwan wankan gawa da kuma iccan kabari." Hannun Zuwaira yana rawa ta miƙa hannu ta karɓa sannan ta ce.
"Godiya nake boka Lado. Nawa ne abin da zan biya?"