Sashe 87
Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har washe gari gidan nan cike yake da mutane. To su Xoxo anga hinkafar banza anƙi tafiya🥱. Huguma da Rano da Mamu kam harda rantsuwar su sai Lulu tai arba'in zasu wuce, yo anga gida ginin gilashi🤣. Nace kunji abin kunya Zafafa dai sai an nuna hali a ko'ina😏🚶, alhalin hinkafar nan fa dai kowa nada a gidansa, gilashi kuwa kowa akwai a windown gidansa. Amma dai bari mu bincika o'e da o'e kodai-kodai 🥱. (I love you Zafafa's😘😘😘❤️💞🙏).
Shatara ta arziƙi kam dai Lulu ta sameshi a wannan haihuwar. Dan Nadiya da Ummita da amaryar Baba Garko da Maryam amarya sune tsaye akan duk wani gift data samu. Tun a wajen hotuna bata sake saka mijinta a ido ba sai a daren na washe gari ya fidda kunya dai ya shigo har ɗakinta. Su Ummita dake baje suna buɗe gifts suka suka fara rige-rigen fita. Idanu Lulu dake da ga kwance AA na gefenta zaune yana fitinar a bashi Baby ta ɗago a hankali ta sauke a kansa. Shima ita yake kallo da yaransa guda uku dake gabanta reras. Lallausan murmushi ya sakar mata yana mai lumshe ƙyawawan idanun nan nasa da take kira na maciji tare da ɗaga kafafunsa a sannu-sannu ya cigaba da nufota cikin takun ƙasaita da kasala tamkar mai irga steps ɗin nashi. Dai-dai yana isowa ta yunƙura zata tashi zaune ya girgiza mata kansa yana mai kaiwa zaune a bakin gadon da kama kafaɗunta ya maidata ya kwantar yana kaɗa mata kansa. Bata da zaɓin daya wuce komawar ta kwanta. Baice da ita komai ba sai hankalinsa da ya maida kan AA. Cike da kulawa ya ce, “Waya saka Baban Ammah kuka ne?”.
Cikin shagwaɓa AA ya nuna Lulu, dan har yanzu shi maganar tasa sai a hankali ce. Dan ma ɗan zamansu a Nigeria ɗin nan ya fara samun bakinsa kasancewar gidan Abba gidan yarane. Balle shi da ko yaushe yana hannun yaran gidan kowa ji yake da shi saboda ƙyautatawar iyayensa. Kaɗan Smart ya ɗan waro idanu waje da faɗin, “Kai-kai Maah-maah ce”. Kai AA ya ɗaga masa yana wani sake ƙwaɓe fuska.. “Ayya Kakan Papa yi shirunka ƙyale Maah-maah kaji ko. Bazamu saya mata kayan daɗinmu ba ai ko?”. Nan ma AA ya ɗaga kansa dan yana jin magana sarai abinsa. Gyara masa zama Smart yayi tare da ɗaukar Hafsat dake a kusa da shi ya ɗauramasa a saman cinya, sai dai bai sakar masa ba tana a hamnunsa. A take yaron ya hau dariya yana nuna Aysha wai itama a ɗaura masa. Haka Smart ya biye masa itama ya ɗaura masan. Ita dai Lulu na kallonsu kawai, dan a yanzu tana sake fahimtar irin so da ƙaunar da mijin nata kema yara ta dabance. Sai da yaran suka ɗan jima a cinyar yaron sannan ya saukesu ya kwantar da su yace ya kwanta kusa da su ya musu wasa.
“Ni dai kada ya tsokale min idanun yara gaskiya. Har yanzu ban gama dawowa a hayyacina ba fa”. Lulu ta faɗa cikin shagwaɓa harda wani ɗan tura baki. Dariya ta bashi ma shi, dan haka ya juyo yana kallonta gira a ɗage ya ce, “Oh really?!”.
“Kai ne shaida ai, tunda kai kafi kowa shan kuka”.
Kansa ya kauda gefe yana murmushi da faɗin, “Oh ni Aliyu. Na shiga tara kuma da gorin yarinyar nan. Ke da baƙya raye a lokacin ya akai kika san haka?”.
Murmushi ta saki mai bayyana haƙwara. Ta ce, “Likimo nayi fa duk ina jinka. Dan na sake tabbatar da wanene mijina. Ashe ragone shi a kan lamurana”.
Yanzu kam dole dariyarsa ta fita da sauti. Ya zuba mata mayun idanun nan nasa yana sakar mata wani murmushi mai sanyi da fasa zuciya. A can ƙasan maƙoshi yana mai dimtse hannunta cikin nashi da ƙyau ya ce, “Kin san kuwa matsayin da Mawaddat Jiƙamshi ke da a zuciyar Aliyu! Wannan sirrin ALLAH ne kawai yasanshi Baby luv. Kin fa gama mamaye ko'ina da ina baki ragema wata koda ƙanƙanin fili ba. Har tsoro nake ji kada wataran ƙaunarki ta fasa zuciyar ɗan bawan ALLAHn nan ma”.
Tuni ƙwalla sun cika mata idanu, zaune ta tashi tana mai juya kwanciyarta zuwa jikinsa. A tare suka saki ajiyar zuciya da lumshe idanunsu suka buɗe duk a lokaci ɗaya. Akan yaranta ta fara sauke nata kafin ta juyo gareshi hawayen da suka taru mata na sakkowa a hankali bisa ƙyaƙyƙyawar fuskar ta. Da sauri ya wara idanunsa zaiyi magana sai ta sakar masa murmushi da girgiza masa kan alamar kada yace komai.
“Aliyu!”.
“Uhyim Mawaddatan'warahmah!”.
“Kai ɗan aljanna ne da izinin ALLAH”.
“Tare ai zamu shige in sha ALLAHU”.
“Da'ace wani ɗan adam nada damar buɗema ɗan uwansa nan dana buɗe tawa ka ga matsayin ka a ciki” tai maganar tana ɗaura hannunsa a saitin zuciyarta. Idanunsa da sukai rauni sosai ya lumshe da sake buɗewa a kanta. “Kin mallaki Aliyu Hydar da komansa Mawaddatan'warahmah. Na jima da sanin kema kin mallaka masa zuciyarki. Sai dai ban san miyyasa kika zaɓi ɓoyewa ba baby luv. Salonki na azabtar dani matuƙa”. Dariya ta ƙyalƙyale masa da ita tana ƙoƙarin tashi ya hanata. Sai ma sake matseta da yay cikin jikin nasa har sai da tai ƴar ƙara da faɗin, “Wash ciwona”. Da sauri ya saketa a rikice, ta ko kwashe masa da dariya tana masa gwalo. Sai ya ƙwaɓe fuska cike da shagwaɓa ya ce “Zan rama ne ai”.
“Sai dai wani karon wannan kam nayi winning”.
“Ba komai, ai da kai da kaya duk mallakar wiyane.” yay maganar yana mai lakace mata hanci. Ita kuma taja kumatunsa da faɗin, “Yaushe Aliyu ya fara ɓoyewa Mawaddat sirrikansa?” ta ƙare faɗa tana kallon ɗakin. Ya fahimci mi take nufi. Dan haka ya saki ɗan murmushi da kallon ɗakin shima. “Aliyu bai taɓa ɓoyema Mawaddat sirrinsa ba. Ya mata hakanne kawai domin supricing ɗinta, kuma Alhmdllh burinsa ya cika, wannan shine gidan Mawaddatan'warahmah da Aliyu da zuri'ar da zasu tara in sha ALLAH.”
Hawayene masu ɗumi suka gangaro a idanun Lulu dake kallonsa ko ƙyafta idanu batayi. Kallonta yay da sauri. Zai yi magana ta ɗaura yatsarta akan lips ɗinsa ta ce, “Shiii!!. Lokacin Mawaddat ne”.
Yanda tai maganar cikin raɗa sosai ya sashi sakin murmushi.....✍️
😁😁😁😁To nima bari na ɗan murmusa
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣5️⃣
________
*_INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRAJI'UN 😭😭😭_*
_ALLAH yayima *MARUBUCIYA FAREEDA ADO GACHI* rasuwa. Ya rabbi ka gafarta mata ka yafe mata kura-kuranta. Ayyukanta na alkairi su zama fansata domin rahamarka ya *UBANGIJI. MARUBUCIYA* ce data taka rawar gani a harkar rubutu da alƙalami da duniyar rubutu bazasu manta da ita ba. Tana cikin tawagar manyan marubutan nan na *MACE MUTU* a littafinsu mai suna *HANNU DA YAWA.....* da wasu ire-iren su. Ta rubuta littatafai ita kaɗai kamar haka._
*MEKE NAN?*
*RAYUWAR MATA*
*ƳAN UBA*
*NI KO SHI*
*RA'AYINA NE*
*TUBALIN TOKA*
*_ALLAH kai mata RAHMA damu baki ɗaya. 🙏🙏_*
*_MADUBINA A HARKAR RUBUTU TA TAFI 😭😭😭🙏_*
_____________
.......A bazata ya ji saukar lips ɗinta akan nasa. Daburcewa ya nema yi kasancewar anfa jima ba'a haɗu ba. Dama ɗan Ammah a wuya yake. Sai da ta gama rikita masa lissafi da salon da bai taɓa sanin ta iya ba sannan ta nema janye jikinta. Shi kuma a sannan yace bai san zancen ba. Dan ta riga ta ɓallo MAZAN FAMA. Murya a sarƙe yana ruƙota ya furta “Please Mawaddatan'warahmah”.
Murmushin mugunta ta sakin masa tana kai bakinta a saitin kunnesa ta furta, “Jego muke fa”.
“Bayan kin gama jigata ni”.
“Yada karaya haka MAZAN FAMA”.
“Ki ɗauka kawai na zama rago ko MATAN FAMA”.
Dariya Lulu ta kwashe da shi. Kamar zai saki kuka ya ce, “Ki kasheni ki huta kawai”.
“Idan na kashe Aliyu dawa za'a ganni a filin yaƙin ƙasa da ƙasar kuma ni Mawaddat”.
Harara ya ɗan sakar mata yana kaiwa kwance dan gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi. Yaransa ya zubama ido kawai dan AA ma yayi barci a kusa da twins.. Mintsini ta kai masa, yay shiru, ta sake ya sake mata shiru, ta sake kai hannu a karo na uku ya damƙe hannun tare da birkiceta. Rikitata ya shiga yi tare birkita mata lissafi da zazzafan salonsa. Sai ga Lulu na roƙonsa harda kukanta akan ya rufa mata asiri yau fa kwananta tara da haihuwa. toshe kunnuwansa yay kamar baya jinta, sai da ya tabbatar ta tsorata matuƙa sannan ya harareta yana komawa gefe. Sai kuma ya koma yimata dariya ganin yanda ta gama fita a hayyacinta da tsoro. ƙaramar ƙwafa yay da faɗin “Gobe ma ki sake takalata zaki sha mamaki dan sai kinga ƙarshen tsokala.”
Baki ta tura masa tana harararsa, da sauri ya kai mata cafka, ta dire da gudu daga gadon. Dariya ya kwashe da ita harda hawaye itako tana harararsa baki a sama.....
Duk shagalin da aka sha sai da aka kaima Umma labari, hawaye kawai take zirararwa. Ga shi dai Aliyu yakai inda ta jima tana yaƙin, yayinda ita take kwance sai an kwantar an tayar. Miji ya saketa ƴaƴan nata ma sai wanda ya ga ALLAH yake tausaya mata. Gashi su dukansu sun koma ƙarƙashin alfarmar maƙiyin nata. Kallon Ammah kawai na ɗaga mata hankali. Dan daka ganta kasan Alhmdllh komai ya zauna dole a kirata uwar sarkin gida. Suna da matsayin data jima farautar samu. Huwaila harda nuna mata video ɗin gidan Smart. Nan ma saita ɓarke da kuka. Babu kunya Huwaila ta sanya dariya tana faɗin, “Su Umma dai ana kwancen ma baza'ai dana baƙin ciki da cigaban wasu ba”. Tana gama faɗa ta miƙe da cikinta tirƙai-tirƙai da ke saka jinin Umma sake hawa a duk sanda ta kalli Huwailar tayi wucewarta yayarta na mata faɗa bata ko saurareta ba.....
★★★
Shatara ta arziƙi kam dai Lulu ta sameshi a wannan haihuwar. Dan Nadiya da Ummita da amaryar Baba Garko da Maryam amarya sune tsaye akan duk wani gift data samu. Tun a wajen hotuna bata sake saka mijinta a ido ba sai a daren na washe gari ya fidda kunya dai ya shigo har ɗakinta. Su Ummita dake baje suna buɗe gifts suka suka fara rige-rigen fita. Idanu Lulu dake da ga kwance AA na gefenta zaune yana fitinar a bashi Baby ta ɗago a hankali ta sauke a kansa. Shima ita yake kallo da yaransa guda uku dake gabanta reras. Lallausan murmushi ya sakar mata yana mai lumshe ƙyawawan idanun nan nasa da take kira na maciji tare da ɗaga kafafunsa a sannu-sannu ya cigaba da nufota cikin takun ƙasaita da kasala tamkar mai irga steps ɗin nashi. Dai-dai yana isowa ta yunƙura zata tashi zaune ya girgiza mata kansa yana mai kaiwa zaune a bakin gadon da kama kafaɗunta ya maidata ya kwantar yana kaɗa mata kansa. Bata da zaɓin daya wuce komawar ta kwanta. Baice da ita komai ba sai hankalinsa da ya maida kan AA. Cike da kulawa ya ce, “Waya saka Baban Ammah kuka ne?”.
Cikin shagwaɓa AA ya nuna Lulu, dan har yanzu shi maganar tasa sai a hankali ce. Dan ma ɗan zamansu a Nigeria ɗin nan ya fara samun bakinsa kasancewar gidan Abba gidan yarane. Balle shi da ko yaushe yana hannun yaran gidan kowa ji yake da shi saboda ƙyautatawar iyayensa. Kaɗan Smart ya ɗan waro idanu waje da faɗin, “Kai-kai Maah-maah ce”. Kai AA ya ɗaga masa yana wani sake ƙwaɓe fuska.. “Ayya Kakan Papa yi shirunka ƙyale Maah-maah kaji ko. Bazamu saya mata kayan daɗinmu ba ai ko?”. Nan ma AA ya ɗaga kansa dan yana jin magana sarai abinsa. Gyara masa zama Smart yayi tare da ɗaukar Hafsat dake a kusa da shi ya ɗauramasa a saman cinya, sai dai bai sakar masa ba tana a hamnunsa. A take yaron ya hau dariya yana nuna Aysha wai itama a ɗaura masa. Haka Smart ya biye masa itama ya ɗaura masan. Ita dai Lulu na kallonsu kawai, dan a yanzu tana sake fahimtar irin so da ƙaunar da mijin nata kema yara ta dabance. Sai da yaran suka ɗan jima a cinyar yaron sannan ya saukesu ya kwantar da su yace ya kwanta kusa da su ya musu wasa.
“Ni dai kada ya tsokale min idanun yara gaskiya. Har yanzu ban gama dawowa a hayyacina ba fa”. Lulu ta faɗa cikin shagwaɓa harda wani ɗan tura baki. Dariya ta bashi ma shi, dan haka ya juyo yana kallonta gira a ɗage ya ce, “Oh really?!”.
“Kai ne shaida ai, tunda kai kafi kowa shan kuka”.
Kansa ya kauda gefe yana murmushi da faɗin, “Oh ni Aliyu. Na shiga tara kuma da gorin yarinyar nan. Ke da baƙya raye a lokacin ya akai kika san haka?”.
Murmushi ta saki mai bayyana haƙwara. Ta ce, “Likimo nayi fa duk ina jinka. Dan na sake tabbatar da wanene mijina. Ashe ragone shi a kan lamurana”.
Yanzu kam dole dariyarsa ta fita da sauti. Ya zuba mata mayun idanun nan nasa yana sakar mata wani murmushi mai sanyi da fasa zuciya. A can ƙasan maƙoshi yana mai dimtse hannunta cikin nashi da ƙyau ya ce, “Kin san kuwa matsayin da Mawaddat Jiƙamshi ke da a zuciyar Aliyu! Wannan sirrin ALLAH ne kawai yasanshi Baby luv. Kin fa gama mamaye ko'ina da ina baki ragema wata koda ƙanƙanin fili ba. Har tsoro nake ji kada wataran ƙaunarki ta fasa zuciyar ɗan bawan ALLAHn nan ma”.
Tuni ƙwalla sun cika mata idanu, zaune ta tashi tana mai juya kwanciyarta zuwa jikinsa. A tare suka saki ajiyar zuciya da lumshe idanunsu suka buɗe duk a lokaci ɗaya. Akan yaranta ta fara sauke nata kafin ta juyo gareshi hawayen da suka taru mata na sakkowa a hankali bisa ƙyaƙyƙyawar fuskar ta. Da sauri ya wara idanunsa zaiyi magana sai ta sakar masa murmushi da girgiza masa kan alamar kada yace komai.
“Aliyu!”.
“Uhyim Mawaddatan'warahmah!”.
“Kai ɗan aljanna ne da izinin ALLAH”.
“Tare ai zamu shige in sha ALLAHU”.
“Da'ace wani ɗan adam nada damar buɗema ɗan uwansa nan dana buɗe tawa ka ga matsayin ka a ciki” tai maganar tana ɗaura hannunsa a saitin zuciyarta. Idanunsa da sukai rauni sosai ya lumshe da sake buɗewa a kanta. “Kin mallaki Aliyu Hydar da komansa Mawaddatan'warahmah. Na jima da sanin kema kin mallaka masa zuciyarki. Sai dai ban san miyyasa kika zaɓi ɓoyewa ba baby luv. Salonki na azabtar dani matuƙa”. Dariya ta ƙyalƙyale masa da ita tana ƙoƙarin tashi ya hanata. Sai ma sake matseta da yay cikin jikin nasa har sai da tai ƴar ƙara da faɗin, “Wash ciwona”. Da sauri ya saketa a rikice, ta ko kwashe masa da dariya tana masa gwalo. Sai ya ƙwaɓe fuska cike da shagwaɓa ya ce “Zan rama ne ai”.
“Sai dai wani karon wannan kam nayi winning”.
“Ba komai, ai da kai da kaya duk mallakar wiyane.” yay maganar yana mai lakace mata hanci. Ita kuma taja kumatunsa da faɗin, “Yaushe Aliyu ya fara ɓoyewa Mawaddat sirrikansa?” ta ƙare faɗa tana kallon ɗakin. Ya fahimci mi take nufi. Dan haka ya saki ɗan murmushi da kallon ɗakin shima. “Aliyu bai taɓa ɓoyema Mawaddat sirrinsa ba. Ya mata hakanne kawai domin supricing ɗinta, kuma Alhmdllh burinsa ya cika, wannan shine gidan Mawaddatan'warahmah da Aliyu da zuri'ar da zasu tara in sha ALLAH.”
Hawayene masu ɗumi suka gangaro a idanun Lulu dake kallonsa ko ƙyafta idanu batayi. Kallonta yay da sauri. Zai yi magana ta ɗaura yatsarta akan lips ɗinsa ta ce, “Shiii!!. Lokacin Mawaddat ne”.
Yanda tai maganar cikin raɗa sosai ya sashi sakin murmushi.....✍️
😁😁😁😁To nima bari na ɗan murmusa
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 6️⃣5️⃣
________
*_INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIRAJI'UN 😭😭😭_*
_ALLAH yayima *MARUBUCIYA FAREEDA ADO GACHI* rasuwa. Ya rabbi ka gafarta mata ka yafe mata kura-kuranta. Ayyukanta na alkairi su zama fansata domin rahamarka ya *UBANGIJI. MARUBUCIYA* ce data taka rawar gani a harkar rubutu da alƙalami da duniyar rubutu bazasu manta da ita ba. Tana cikin tawagar manyan marubutan nan na *MACE MUTU* a littafinsu mai suna *HANNU DA YAWA.....* da wasu ire-iren su. Ta rubuta littatafai ita kaɗai kamar haka._
*MEKE NAN?*
*RAYUWAR MATA*
*ƳAN UBA*
*NI KO SHI*
*RA'AYINA NE*
*TUBALIN TOKA*
*_ALLAH kai mata RAHMA damu baki ɗaya. 🙏🙏_*
*_MADUBINA A HARKAR RUBUTU TA TAFI 😭😭😭🙏_*
_____________
.......A bazata ya ji saukar lips ɗinta akan nasa. Daburcewa ya nema yi kasancewar anfa jima ba'a haɗu ba. Dama ɗan Ammah a wuya yake. Sai da ta gama rikita masa lissafi da salon da bai taɓa sanin ta iya ba sannan ta nema janye jikinta. Shi kuma a sannan yace bai san zancen ba. Dan ta riga ta ɓallo MAZAN FAMA. Murya a sarƙe yana ruƙota ya furta “Please Mawaddatan'warahmah”.
Murmushin mugunta ta sakin masa tana kai bakinta a saitin kunnesa ta furta, “Jego muke fa”.
“Bayan kin gama jigata ni”.
“Yada karaya haka MAZAN FAMA”.
“Ki ɗauka kawai na zama rago ko MATAN FAMA”.
Dariya Lulu ta kwashe da shi. Kamar zai saki kuka ya ce, “Ki kasheni ki huta kawai”.
“Idan na kashe Aliyu dawa za'a ganni a filin yaƙin ƙasa da ƙasar kuma ni Mawaddat”.
Harara ya ɗan sakar mata yana kaiwa kwance dan gaba ɗaya jikinsa babu wani ƙarfi. Yaransa ya zubama ido kawai dan AA ma yayi barci a kusa da twins.. Mintsini ta kai masa, yay shiru, ta sake ya sake mata shiru, ta sake kai hannu a karo na uku ya damƙe hannun tare da birkiceta. Rikitata ya shiga yi tare birkita mata lissafi da zazzafan salonsa. Sai ga Lulu na roƙonsa harda kukanta akan ya rufa mata asiri yau fa kwananta tara da haihuwa. toshe kunnuwansa yay kamar baya jinta, sai da ya tabbatar ta tsorata matuƙa sannan ya harareta yana komawa gefe. Sai kuma ya koma yimata dariya ganin yanda ta gama fita a hayyacinta da tsoro. ƙaramar ƙwafa yay da faɗin “Gobe ma ki sake takalata zaki sha mamaki dan sai kinga ƙarshen tsokala.”
Baki ta tura masa tana harararsa, da sauri ya kai mata cafka, ta dire da gudu daga gadon. Dariya ya kwashe da ita harda hawaye itako tana harararsa baki a sama.....
Duk shagalin da aka sha sai da aka kaima Umma labari, hawaye kawai take zirararwa. Ga shi dai Aliyu yakai inda ta jima tana yaƙin, yayinda ita take kwance sai an kwantar an tayar. Miji ya saketa ƴaƴan nata ma sai wanda ya ga ALLAH yake tausaya mata. Gashi su dukansu sun koma ƙarƙashin alfarmar maƙiyin nata. Kallon Ammah kawai na ɗaga mata hankali. Dan daka ganta kasan Alhmdllh komai ya zauna dole a kirata uwar sarkin gida. Suna da matsayin data jima farautar samu. Huwaila harda nuna mata video ɗin gidan Smart. Nan ma saita ɓarke da kuka. Babu kunya Huwaila ta sanya dariya tana faɗin, “Su Umma dai ana kwancen ma baza'ai dana baƙin ciki da cigaban wasu ba”. Tana gama faɗa ta miƙe da cikinta tirƙai-tirƙai da ke saka jinin Umma sake hawa a duk sanda ta kalli Huwailar tayi wucewarta yayarta na mata faɗa bata ko saurareta ba.....
★★★