← Book details Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 90

Sashe 33

Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

    Duk da zuciyarta a dagule take da wannan tafiya ta mijinta da kishiyarta da tafi tsana fiye da kowa a rayuwarta ta wani fannin hakan ya taimaketa, dan ta samu damar aiwatar da mugayen nufinta akan wanda suke wa taƙamar da tinƙaho. Saboda tayi alƙawarin kofa komanta zai ƙare ita sai taga bayan Smart da uwarsa. A haka ma dan bata san ainahin abinda ya kaisu UK ɗin ba kenan. Hankalin aunty amarya ya tashi da ganin kai-kawon da Umma ke yi, dan haka kawai zuciyarta ke ayyana mata kai-kawon bana banza bane ba. Su dukansu sun jima suna zargin Umma akan shige-shigen gidajen malamai. Dan a wasu lokutan sukan kasa gane kan mijin nasu ta koma sai ita kaɗai ce madubin dubawarsa. Sai sun dage da addu'a abin yay sauƙi kafin ta sake masa sabon aike. Wannan dalilin yasa a yanzu ɗin ma Aunty Amarya ta shiga damuwa. Sai dai ta rasa dawa zatayi maganar dan Mama ita ba gane kanta ake ba wasu lokutan sai a hankali ce. Ga shi su Maryam basa nan. Ganin abin nata cigaba da alamomi masu yawa ta ɗaga waya tai kiran aunty Bilkisu akan tazo dan ALLAH idan ta samu lokaci. Da sauri Aunty Bilkisu ta tabbatar mata da gatanan zuwa.
          Da yamma ko sai gata, sai dai ta nuna kamar daga wani waje take ta biyo gaishesu. Sama-sama Mama da Umma suka amsa mata gaisuwarta, dan suna cike da takaici da kishin tafiyar Abba da Ammah. Aunty Bilkisu bata nuna ta damu ba ta shiga ɗakin aunty Amarya abinta. Tsakanin aunty Bilkisu da aunty Amarya suna abune kamar ƙawaye, duk da aunty Bilkisun ta girmeta kaɗan, bayan sun gaisa babu ɓata lokaci suka shiga tattauna abinda ya tara su. Sosai hankalin Aunty Bilkisu ya tashi da bayanin aunty Amarya, duk sai ta rikice. Cikin kwantar da hankali aunty amarya ta ce, “Bilkisu dan ALLAH karki ruɗa kanki, mu nutsu muyi tunanin abinda ya dace, dan kinga dai bawai tabbas garemu ba zargi ne”.
        “Aunty wannan ai ya wuce zargi tunda har kinji tana ambatar sunan Hydar ɗin da matarsa. Wlhy nikam al'amarin Umma ya fara bani tsoro a gidan nan. Ko kin san kwanan nan sai da taje ta kaima kishiyata gulmar Ammah da har ta kaimu da yin faɗa. Alhaji ne ya tausheni da kar nazo gida na faɗa kamar zaimin kuka. Kuma ya tabbatar min da ai ta daɗe tana kai musu gwabsona dana Ammah kawai dai yanzu ne ALLAH ya tona asirinta. Akan wannan rigimar yanzu haka uwargidana na gidansu ya mata saki ɗaya”.
            “Innalillahi. Itako Umman Hannatu mi take son zama ne? Wlhy al'amarin ta na bani mamaki”.
      “Dolene abinta yake bada mamaki ai Aunty, ki duba fa yanda ta tada hankalinta a gidan nan tunda taji Hydar na ƙasar waje. Ni wlhy zuciyata ma har ta fara zarginta akan matsalar da yayta samun nan a baya. Kawai dai dan Ammah tace kar nayi magana ne”.
          “Eh ai tabakin Yayar gara a barta, ita da kanta halinta zai tsangwameta kowa ya shaida. Amma yanzu idan akaji a bakin wani a cikinmu za'a ɗauka sharrin kishi ne kawai. Kin san kuma Yaya ita komai nata a nutse ne bata son gaggawa. Shiyyasa yanzu ma kikaga na nemoki dan kota dawo bana son na fara mata maganar, duk da nasan zata fahimce ni”.
       “Hakane Aunty, yanzu to yaya zamuyi?”.
      “Addu'a zamu dage da ita, mu kuma saka a cigaba dama Aliyu shima har sanda su Yaya zasu dawo miji nata shawaran”.
    Aunty Bilkisu ta gamsu da shawaran aunty Amaryan, dan haka suka cigaba da tattaunawa. Bata bar gidan ba sai bayan sallar magrib........✍️

_Network kaje dan kanka. Na barka da ƙarfen da ake maƙalaka ehe🥱🥱🚴_.

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣6️⃣

.......Kamar yanda Daddy ya faɗi zasu tattauna da Smart tun a waya ya cika alkawari, dan washe gari tunda safe ya baro Abba da Uncle Yousuf ya sami Smart a gidan su Usman dan nan ya kawoshi. Sun gaisa cikin mutunta juna kafin su fara tattaunawa. A nutse Daddy ya fara ma Smart bayanin mafarin komai tsakaninsa da Sulaiman har zuwa yau da suke tare. Matuƙar girgiza Smart ya shiga, tare da jinjina ƙarfin halin Daddy da sake ganin kimarsa. Ya jure ɗaci da damuwa saboda kawai karya rama sharri da alkairi, saboda kare mutunci da lafiyar ahalinsa. Cikin zubda hawaye Daddy ya katse Smart da faɗin, “Abu ɗaya ne ke cimun zuciya a yanzu Aliyu shine cutar da matarka da nayi, kwarai da gaske na zalunci rayuwar Mawaddat dan rashin ilimin addini babbar naƙasu a rayuwar ɗan adam. Gara ace mutum bai san komai a limin boko ba dan wannan iya kar alfaharinka da shi shine duniya. Inajin kunyarta ta yanda a duk sanda na tunata nakanji hawaye na zubarmin tunda ba haka naima sauran ƴan uwanta ba. Wlhy alokacin idanuna ne suka rufe da iya tunanin kuɓutar da ita da ga sharrin Sulaiman ne kawai shiyyasa. Iya ƙoƙari Yousuf kuma yayi na ganin ta samu ilimin har malami ya nema mata a can Germany amma tsoron karda a haɗa baki da Malamin a cuta mata yasa na hana hakan. Ashe na manta UBANGIJI shine mai ikon tsarewa da killace bawa da ga sharrin masu makirci da ƙulle-ƙulle ba wai wayo ba. Domin nayi gudun gara na faɗa gidan zago. Dan ALLAH ka tayani bata haƙuri da neman gafararta, ka tayani gina mata sabuwar rayuwa, ka tayani horas da ita sababbin ɗabi'u, ka tayani ɗorata a hanyar tsira Aliyu kafin ɗan sauran lokacin da ya rage min ya ƙure mana ni da ita. Dan nasan da wahala na tsallake da ga tarkon Sulaiman saboda shu'umi ne na gaske. A yanzu haka ya ƙullaci mahaifinka akan maganar kotun nan, amma Alhamdullah babu abinda ya isa masa dan duk inda ya saka ƙafa na saka ƴan sandan farin kaya biye da shi, bama shi ba hatta ƙannenka dake gida dana ma'auri al'amarinsu na ƙarƙashin kulawar hukuma a duk sanda zasu bar gida. Kayi haƙuri kaima Aliyu na sakaka a rigimar da baku san mafarinta ba, shiyyasa raina fansa akan ganin wani abu bai cutar da ku ba a dalilina. Amma dan ALLAH ku yafe min duk laifina ne, da ace nayi nazari kafin na biyema Sulaiman tun farko maybe da duk bamu kai a irin wannan matakin ba.....”
          “Daddy jarabawace kawai, bawa kuma bai isa tsallake ƙaddararsa ba. Ba kamana laifin komai ba sai alkairi a rayuwa. Babu abinda zan iya cemaka sai godiya da cigaba da maka addu'a har ƙarshen numfashina. Ba laifinka bane Mutumin nan hatsabibin ne na gaske. Na fahimci hakan tun a haɗuwata da shi ta farko. Dan haka na zauna na karancesa yanda ya kamata, sai dai rashin sanin abinda ke a tsakaninku yasa ban taɓa wani yunƙuri ba. Amma tabbas na jima da lura da duk inda nake ana biye da ni, hakama ƙannena, na shiga tashin hankali saboda a tunanina Sulaiman ne, sai daga baya na fahimci ƴan sanda ne, sai dai babu irin bibiyar da ban musu ba sunƙi gayamin wanda ya sakasu, sai nai tunanin ma ko Uncle Yousuf ne ko Coach a lokacin, shiyyasa na zaɓi musu shiru a ganina wataran ai zan sani. Kamar yanda na faɗa maka ina son ka bar wannan case ɗin a hannuna yanzu, sannan ina son na bada shawara....”
       Cike da kulawa Daddy ya ce, “Ina jinka Aliyu, ka faɗi komi ke'a ranka kai tsaye tsakaninmu babu wani ɓoye-ɓoye”.
     Kai Smart ya jinjina tare da furzar da iska mai nauyi. “Wato Daddy irin su Sulaiman da hatsabibancinsu yaƙin sunƙuru yake buƙata a farkon fara wasa. Kamar yanda ka ɗauki masa salon shekarun da suka gabata na nuna baka san mi yake ciki ba wannan salon zamu cigaba a yanzu har zuwa wani mataki. Domin idan har akace za'ai masa fito-na-fito a shirye yake da wannan tun ba yanzu ba. Jirace yake da kai kace kule yace cass. Sannan mahaifinsa da kai hallacin shanye komai daminsa zai iya samun bugawar zuciya wlhy in har yaji kasuwancin da yake yi da kuma ketama autarsu mutunci da yayi. Ko kuma shi da kansa ya shirya hanyar halakasu idan yaga zaka cimma burin tona masa asiri. Kaga anyi gudun gara kenan an faɗa gidan zagon dai. Dan haka mu ajiye batun fito-na-fito ɗin nan mu lallaɓa Baba Garko ya sakar masa ɗansa, ka cigaba da nuna masa kana shakkar tasa, sauran yaƙin ka bar mana zamu ƙarasashi ni da Mawaddat da Uncle Yousuf in sha ALLAHU”.
      Idanu kawai Daddy ya zubama Smart, yama rasa abin faɗa akan wannan yaro. Lallai farar haihuwa tayi, dan shikam dole ya kira wannan yaro da farar haihuwa ga iyayensa. Smart ne da yaga kallon da Daddyn ke masa yay ƙasa da kansa yana murmushi kawai....

__________★
Chapter 33 · 0% Book details