← Book details Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 90

Sashe 5

Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.......“Kai ɗin banza da zanji tsoronka Sulaiman. Ka sannni kaima ai, ni na wuce maka kanwar lasa, sannan ni ƙadangaren bakin tulune a rayuwarka data abokanka ta yanda kuka rasa yanda zakuyi dani. Ƙarshen target ɗinku shine ku kasheni dai, kuma na tabbatar muku a randa kuka kasheni wlhy ko minti ɗaya bazan cika ba da ɗaukewar numfashi kuma duniya zatai muku zafin da sai kun gwammace mutuwa kamar ni, dan sai mutanen duniyar sun san suwaye ku. Idan ba tsoro kuke ji ba miyya hanaku aikatawar a tsahon shekarun nan. Miyasa kuka kasa bayan kunada kowacce irin dama? Miyasa baku aikata bane sulaiman? Ku kashenin mana? Maza ku kashenin idan kun cika ku tsagerane dan ALLAH!!”.
      Matuƙar razana Alh. Sulaiman yayi da kalaman Daddy, cikin ɓacin rai da zafafuwar zuciya ya nunashi da yatsa lips ɗinsa na rawa. “Haka kace ko?”.
          “Haka nace Sulaiman, idan kuma bakaji ba na sake maimaita maka. Kuma wlhy na baka daga nan zuwa ƙanƙanin lokaci ɗiyata ta dawo gareni inba hakaba sai na sakaka nadama irin wadda sai ka gammaci mutuwa da rayuwa. Dan duk inda kasa ƙafa ka sani ni Isma'il ƙaddararka biye nake da kai. Plan ɗinku na gaba shine sakama Yousuf cocaine a kaya yayinda da zai baro ƙasar Chaina zuwa Nigeria. Bance ku fasaba dan ALLAH, amma ku sani wannan shine mabuɗin farko na kiran mutuwarku. Ni Isma'il kallon kitse kukema rogo kawai, dan ko poisining ɗin Baba da kukayi na barku ne kawai bisa wani dalilina na tarkon dana ɗanama rayuwarku. FURAR DANƘO NAKE, A SHEKARA ANA DAMU BANI FARAU-FARAU. Mawaddat kuwa bazan sake cemaka ina take ba, in dai har ita ɗin jinina ce da kanta zata maido kanta gida bisa bigiren bijire muku. Ku muje zuwa wasan a yanzu na shirya masa....”
          Har Daddy yabar office ɗin Alh. Sulaiman da yay sumar tsaye bai iya dawowa a hayyacinsa ba. Sai da Daddyn yay banging ƙofar ne ya zabura wata zufa na feso masa a illahirin jikinsa. Bai ma san sanda ya since hular kansa ya hau fifita da ita ba jikinsa ma wata irin rawar shiga ruɗani da tashin hankali. Ji yake kamar mafarki yakeyi, shin Isma'il da ya sani ne haka wai shin ko canja shi ankayina? wagga al'amari haka kamar a mahwalki. Shiy yasan Isma'il nada zuciya kam tabbas batun yanzu ba, amma bai taɓa tabbatar da zai iya wani yunƙuri ba bayan kafiyar daya sanshi da ita kawai musamman da yaga tunda suka fara ƴar tsamar nan Daddyn nayi tamkar yana shakkarsa a koda yaushe, lallai ya yarda bakatsinan mutum abin tsorone yau. Da ƙarfi ya hankaɗa kayan saman table ɗin nasa da nuna ƙofa a kausashe ya furta “Isma'il You really are playing with fire!!!....”

       (😂Daddy ni kaina ka shayar dani mamaki, ashe jinin katsinawan dai na aiki a jininka) 

       *_CANADA_*

       Sosai hankalin Dada ya sake tashi ganin yanda Lulun tai wani masifar ɗashewa ta ƙara haske sosai, ga komai nata ya ciko musamman ƙirjinta. Dan ma zazzaɓin daya tasota gaba ya ɗan saka jikin nata girgiza ƙasa kaɗan kwana biyun nan. Tambaya bayan tambaya Dada ta shiga jeroma Dr Olivia akan mike damun jikar tata haka. Kai tsaye Dr Olivia ta sanar mata Lulu na ɗauke da ciki wata uku da kwanaki biyu. Tamkar an fasa irin ƙaton dutsen nan mai girgiza yanki da gidajen wajen gaba ɗaya haka maganar Dr Olivia taima Dada saukar aradu a tsakkiyar ka. Cikin razani da zabura ta maimaita kalmar “Ciki!”  ɗin zuciyarta na bugawa. Dr Olivia ta sake tabbatar mata da hakane. Wata muguwar ashariya Dada ta lailayo ta dire akan Smart. Tare da faɗin, “ALLAH ya tsinema wannan shegen yaro dangin talauci dangin jaraba. Yanzu nan sai da dai ya ɗirka mata ciki. Amma Mawaddat kema ƴar banzar yarinya ce. Randa na ɗakkoki da ga gidan yaron nan har tambaya naita jera miki akan yanayin dana ganki amma kikace min faɗuwa kikayi ashe-ashe miƙa masa jiki kikai ya lalube”. Sai ga hawaye suna cika idon tsohuwar nan dan ɗaurama kai masifa. Kasancewar da Hausa Dada tai maganar duk sai hankalin Dr Olivia ya tashi ta shiga tambayarta ko lafiya. Rai ɓace Dada tace mata ba komai tana zuwa. Cikin rawar jiki ta fito tana neman lambar Alh. Sulaiman ɗanta...

        *_LONDON_*

       Iya ƙoƙari yana yi wajen ganin ya ajiye matsalolinsa gefe ya fuskanci rayuwarsa ta yanzu da cigaban da ya riskeshi. Sai dai hakan ya gagara matuƙa duk da akoda yaushe yay waya da Ammah ko Abbah ko Uncle Yousuf da Coach shawara suke bashi akan ya dai ƙara daurewa. Ammah kan masa nasiha mai ratsa jiki da tabbatar masa in sha ALLAH komai zai zama labari, kuma in har Mawaddat matar da zai rayu da itace duk abinda za'ai sai ta dawo garesa. Wannan ƙwarin gwiwar da mahaifiyarsa ke bashi kan ƙara ƙarfafa masa gwiwa. Sai dai hakan bai hanashi kasancewa cikin mafarkin Lulu ba a duk sanda zai kai kwance da sunan barci. Al'amarin ma har yana neman zame masa jiki akoda yaushe a koda yaushe cikin wanka yake. Ya kasa manta dare mafi daraja da muhimmanci da ya zama wani babban jigo a cikin zamansu na kwanaki ashirin da shidda. Tunashi kansa yay murmushi ko ƙaramar dariya harma da tausayawa. Duk da ashi kansa yasan darene da bazai iya tantance komai yanda ya kamata ba illa dai yasan a shi kansa yasha wahala balle ita. Amma sambatunta ko neman agaji zai ce na wannan dare ya kasa manta komai.
         Yau ma kamar kullum cikin shiri fita wajen training ya fito daga dogon ginin estate ɗin da masaukinsa yake zaune mai hawa kusan ɗari da hamsin, a hawa na tamanin da biyar yake dan haka ya sakko ta lifter har zuwa block A, sanye yake cikin dogon wando na sport da riga mai dogon hannu itama dai irin wandon ce. Sosai ya canja gaba ɗayansa tamkar wanda dama tun farko yake rayuwa anan ɗin. Fatarsa ta sake gogewa ya sake yin haske da kwarjini da cikar kamala a cikin wata uku kacal tamkar wani baƙin bature. Yawan training da sukeyi ya sake buɗe masa halittun gaɓɓai da sake kasancewar sa tsayayyen mutum da za'a iya kallo a jarumi. Kunnensa manne yake da bluetooth yana magana a hankali kamar baya so alamar waya yake amsawa. Ba kowa bane face Ahmad da yay kiransa, duk da yanayin da yake a yanzu na sake zama shiru-shiru da rashin son magana idan Ahmad ɗin yay kiransa yakan ɗan sake suyi hira. Da ɗan gudu-gudu ya fara tafiya jefi-jefi yakan ɗagama wanda suke ɗan wucewa kamar shi a hanya hannu. Yayinda yake cigaba da magana da Ahmad ɗin. Da ga estate ɗin nasu zuwa inda suke training ɗin akwai ƴar tazara sai dai ba wata mai yawa ba sosai, amma duk da haka yakan jure tafiya a ƙafa koma cikin ɗan gudu-gudu kamar yanda yake yi a yanzu domin fara motsa jininsa kafin ya isa. Hakan na ƙara masa ƙarfi da zaburarwa a yayin da ya shiga fili sai karsashinsa ya ƙaru. Sosai sabon baturen Coach ɗin nasu ke yaba ƙwazonsa da jin cewar za'a mori yaron matuƙa idan aka ƙara tsayawa akan al'amarin sa zai zama babbar kaddara, shiyyasa akoda yaushe yake sake jan Smart a jikinsa da ƙara masa dabaru kala-kala dan Smart irin mutanen nan ne masu shiga ran mutane a komai nasu, ga shi baida hayaniya sam, yanayin da yake ciki ma ya sake maida shi miskili a yanzu duk da hakan ba halinsa bane a baya. Amma hakan bai hanashi zama abin so ga wasu ba hatta a cikin teammate ɗin nashi. Alhamdullah yana ƙoƙarin maida hankali tare da ajiye gyambon dake mamaye a zuciyarsa gefe domin fuskantar abinda yaje yi a yanzu, wannan ne karo na farko da zai tunkari babban wasa link na ƙasar da za'a fara, Yana alfahari da hakan duk da team ɗin nashi ƙarami ne. Cikin zafin nama ya iso inda sauran team mate ɗinsa suke. Babu ɓata lokaci suka shiga abinda ya tarasu, sosai yake nuna ƙwazo dake firgita al'amarin wasu a cikin abokan nashi bisa dalilai masu yawa. Na farko shi kaɗaine baƙar fata ɗan Africa a cikinsu, na biyu musulmi, na uku baƙon da har yanzu bai wuce watanni uku da kwanaki ba a cikinsu, amma yana taka leda da sunan training mai firgita zuciya. Ga yanda Coach ɗin nasu yay masifar maida hankalinsa kansa a ɗan ƙanƙanin lokaci na basu mamaki. Yau ɗin ma dai mamakin daya saba basu ya basun, dan har aka tashi babu alamun gajiyawar raunin jiki dana gaɓɓai a tattare da shi. Sai dai su a zahirine kawai suke ganin haka, shi a karan kansa can ƙasan zuciyarsa cike take da rauni. Ga wani irin faɗuwar gaba da ya tashi da ita yau tamkar wanda wani mummunan abu ke neman faruwa da shi. Amma yanayinsa na dakewa da rashin walwala yasa sam su basu fahimci komai ba.
      Cikin huttai ɗai-ɗai irin na wanda yasha kai kawo ya samu waje ya kai zaune yana kwankwaɗar ruwan dake hannunsa. Sharkaf yake da zufa tamkar wanda yay wanka. Yanda yake shan ruwan kai a sama ya bama Adams apple ɗinsa damar motsawa cikin kaikawo haɗiyar ruwan da sauri-sauri. Sai da ya shanye ruwan tas ya sauke bottle ɗin yana furzar da nannauyar numfashi. A hankali ya zame jikin kujerar ya kwantar da bayansa yana mai lumshe idanunsa da kai hannunsa saman ƙirjinsa dai-dai zuciyarsa dake cigaba da bugawa ya dafe yana karanto addu'a da fatan koma minene ke tunkarosa ALLAH ya sauƙaƙa masa shi ya kuma bashi juriyar ɗauka.....

*_NIGERIA_*
Chapter 5 · 0% Book details