Sashe 60
Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read
A ɓangaren Lulu tun fitar Smart itama ta fice a gidan. Asibiti ta nufa saboda maganar Smart dake cimata rai akan shi baya saɓa saiti. Haka kawai take jin tsoro a ranta, ita yanzu ta samu ciki kuma ai taga bonu. Yaushe ma yaronta yay ƙwarin hakan. Bawai bata son yara ba, amma dai tafi son ko zata sake haihuwa sai AA ya kai irin 5years haka. Yanzu kam tana ina zata fara haɗama kanta cakwakiyar nan, ga business ga rainon AA, ga fitinar ubansa, ga rainon ciki da hidimar ƙungiya dana aikinta. Ta samu ganin likita, babu wani kwana-kwana tace planning zatayi, amma su fara tabbatar da babu wani abu a jikinta, duk da dai a ganinta haɗuwa uku bai zama lallai a samu wani abu ba, to amma idan tai la'akari da farkon haɗuwar aka samu cikin AA sai hankalinta ya sake tashi taji ta kasa yarda da kanta. Doctor dai ta mata dukkan abinda ya dace sannan ta bata magani, acewarta a iya bincikensu mahaifarta fresh take babu komai. Amma ga magani tasha koda ma an samu akasi marar zata sake wankuwa fass. Daga haka suka saka mata abu a jiki ta dawo gida tana jin hankalinta a kwance. Ta iske har lokacin Smart bai dawo gidan ba. Dan haka ta ƙirƙiri aiki dan zama waje ɗaya ya isheta. Tsaff ta gyara gidan tare da musu girkin Nigeria yau. Tana kammalawa tai wanka, kayanta da ya rage ɗaya tak ta saka ta dawo falo ta zauna dan AA tunda suka dawo barci yake abinsa. Ta shagala a kallo ya shigo gidan da sallama hannunsa ɗauke da kaya. Bata motsa da ga inda take ba ta dai zuba masa ido, shiko nashi idanun na kallon gidan ne da yanda aka gyara shi, aka canja zaman abubuwa da yawa. Gyaran mace dabanne. Ya ayyana a zuciyarsa yana ajiye kayan hannunsa a hankali. Kusa da ita ya kai zaune cikin yanayin gajiya ya ke faɗin, “Madam ya gidan?”.
Baki ta tura da faɗin, “Ni ALLAH idan baka daina cemin Madam ɗin nan ba zamuyi faɗa ko kaima na saka maka suna. Sai kace wata tsohuwa?”.
“Oh da yarinya kike ɗaukar kanki, ai kin tsufa tunda gaki da AA. Nan da shekara ashirin zaki ga anzo fara miki gaisuwar uwar miji”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi, ta ce, “Kai kuma Baban miji ko”.
Murmushi yayi yana ɗan girgiza kansa. Sai kuma ya lunshe ido ya sake buɗewa a kanta. “Ina boss ɗin gidanne naji shiru?”.
“Barci yake, shiyyasa nake hutawa ta ai.”
“Ai yanzu ga baban shi ya dawo hutu ya ƙare”. Yay maganar yana kissing kuncinta da kwantar da kansa a kafaɗarta. A hankali ta sauke numfashi da lumshe idanunta itama. Dan zuwa yanzu duk yanda taso cigaba da riƙe kanta salonsa na barazanar tonata ne. Ƙarfin hali ne kawai da taurin kai irin nata. A hankali ta ce, “Yaya wasan?”.
“Alhamdullah bakin ƙi zuwa kallo ba”.
“To ni Wlhy ban iya kallon ƙwallo bane”.
“Sai ki fara koyo ai”.
“Zan ƙoƙarta in shan ALLAH kodan kai. Ni yanzu ma maganar da nake son maka shine jibi fa ya kamata mu koma”.
Batare da ya buɗe idonsa da ga rufen da suke ba ya ce, “Ina kenan?”.
A shagwaɓe ta ce, “Nigeria mana”.
“Uhhyim yin me?”.
Idanu ta zuba masa da mamaki, “Ya zakace yin me bayan kasan ayyuka na baro na taho nan, kuma ni da shirin sati ɗaya na taho ko kwana goma. Wlhy inada abubuwa masu yawa acan”.
Kaɗan ya buɗe idanunsa yana kallonta, tsahon mintina kamar bazaiyi magana ba sai kuma ya firzar da numfashi. Cikin deep voice ɗin nan nashi da babu wasa a cikin fitar sauti ta ya ce, “Mawaddat! Ke yanzu idan ance miki ki ƙara tafiya kibar mijinki sai ki tafi? Kiyi lissafi shekarar aurenmu ɗaya da wattani takwas kenan fa. Amma bamu taɓa zaman cikakken wata guda ba har yanzu. Idan ke baƙya jin damuwa da hakan ni gaskiya ina ji. Sannan haƙurina ya ƙare ina buƙatarku a kusa dani yanzu. Shekarunmu tafiya suke bakwai komawa baya ba, ko sai ƙarfina ya ƙare sannan zaki fiskanceni a gaɓar da bazan iya komai a gareki ba. Na waiga ma na ganku a kusa da ni farin ciki nake ji. A yanda nai wasa a fili yau kowa yasan ina cikin farin ciki mara misali, aure ibada ne fa bawai son zuciya ba ko ra'ayin kanka a yanda kaso tafiyar da shi. Dan haka maganar komawa na soke shi, ba yau ba, ba gobe ba babu ma rana kawai at all. Dan haka karma ki sake mun maganar data shafi hakan ranmu zai ɓaci ne kawai”. Ya miƙe fuska a tsuke ya bar falon zuwa bedroom........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣5️⃣
Baki ta tura da faɗin, “Ni ALLAH idan baka daina cemin Madam ɗin nan ba zamuyi faɗa ko kaima na saka maka suna. Sai kace wata tsohuwa?”.
“Oh da yarinya kike ɗaukar kanki, ai kin tsufa tunda gaki da AA. Nan da shekara ashirin zaki ga anzo fara miki gaisuwar uwar miji”.
Dariya ta ƙyalƙyale da shi, ta ce, “Kai kuma Baban miji ko”.
Murmushi yayi yana ɗan girgiza kansa. Sai kuma ya lunshe ido ya sake buɗewa a kanta. “Ina boss ɗin gidanne naji shiru?”.
“Barci yake, shiyyasa nake hutawa ta ai.”
“Ai yanzu ga baban shi ya dawo hutu ya ƙare”. Yay maganar yana kissing kuncinta da kwantar da kansa a kafaɗarta. A hankali ta sauke numfashi da lumshe idanunta itama. Dan zuwa yanzu duk yanda taso cigaba da riƙe kanta salonsa na barazanar tonata ne. Ƙarfin hali ne kawai da taurin kai irin nata. A hankali ta ce, “Yaya wasan?”.
“Alhamdullah bakin ƙi zuwa kallo ba”.
“To ni Wlhy ban iya kallon ƙwallo bane”.
“Sai ki fara koyo ai”.
“Zan ƙoƙarta in shan ALLAH kodan kai. Ni yanzu ma maganar da nake son maka shine jibi fa ya kamata mu koma”.
Batare da ya buɗe idonsa da ga rufen da suke ba ya ce, “Ina kenan?”.
A shagwaɓe ta ce, “Nigeria mana”.
“Uhhyim yin me?”.
Idanu ta zuba masa da mamaki, “Ya zakace yin me bayan kasan ayyuka na baro na taho nan, kuma ni da shirin sati ɗaya na taho ko kwana goma. Wlhy inada abubuwa masu yawa acan”.
Kaɗan ya buɗe idanunsa yana kallonta, tsahon mintina kamar bazaiyi magana ba sai kuma ya firzar da numfashi. Cikin deep voice ɗin nan nashi da babu wasa a cikin fitar sauti ta ya ce, “Mawaddat! Ke yanzu idan ance miki ki ƙara tafiya kibar mijinki sai ki tafi? Kiyi lissafi shekarar aurenmu ɗaya da wattani takwas kenan fa. Amma bamu taɓa zaman cikakken wata guda ba har yanzu. Idan ke baƙya jin damuwa da hakan ni gaskiya ina ji. Sannan haƙurina ya ƙare ina buƙatarku a kusa dani yanzu. Shekarunmu tafiya suke bakwai komawa baya ba, ko sai ƙarfina ya ƙare sannan zaki fiskanceni a gaɓar da bazan iya komai a gareki ba. Na waiga ma na ganku a kusa da ni farin ciki nake ji. A yanda nai wasa a fili yau kowa yasan ina cikin farin ciki mara misali, aure ibada ne fa bawai son zuciya ba ko ra'ayin kanka a yanda kaso tafiyar da shi. Dan haka maganar komawa na soke shi, ba yau ba, ba gobe ba babu ma rana kawai at all. Dan haka karma ki sake mun maganar data shafi hakan ranmu zai ɓaci ne kawai”. Ya miƙe fuska a tsuke ya bar falon zuwa bedroom........✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣5️⃣