Sashe 37
Furar Danko Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Washe gari suka tashi Lulu nata rakin ciwon kai. Sai da Ammah tai mata addu'oi a ruwa tasha aka kama mata kan sannan. Lokacin da su Smart suka iso ya lafa mata. Tana cikin rubutu a littafinta Smart ya shigo da sallama su Ahmad biye da shi. Sai da ta saka mayafi yace su shigo. Sun gaisa da tambayar juna gajiyar taro Ahmad ya ɗan tsatstsokaneta sannan suka fito suka barsu. Smart da tun shigowarsa hankalinsa ke akan book ɗin da takema rubutu sanda ya shigo ta ɓoye. Suna fita ya kai hannu bayanta zai ɗauki littafin tai saurin buge masa hannu tana ɓata fuska. Idanun nan nasa ya kafeta da su babu walwala sam tare da shi. Duk sai taji ta daburce saboda mugun kwarijin ya mata da cika waje. Shima babu wasa a tattare da shi murya a dake ya furta, “Kinada wani abun ɓoyewa ne da kike ganin saninsa a gareni illa ne?”.
Fuska ta tsuke cikin cuna baki batare data amsa masa ba. Shima sai ya sake dakewa da koma mata Smart ɗin nan mai ɗaukar kai da manna mata hauka sanda yana drivern ta. A kausashe ya furta, “In ma baki son na sani kin makaro. Domin ɗayan littafin ai yana gareni. Banyi niyyar karantawa bane kawai dan nafi son jin komai daga bakinki ba'a rubuce ba.” Da sauri ta ɗago tana kallonsa, ya ɗauke kansa gefe kamar bai ganta ba. Sai kawai taji hawaye sun cika mata ido. Cikin rawar murya ta ce, “Da gaske kakeyi?”.
“Na miki kama da ɗan wasan kwaikwayo ne da zan miki ƙarya?. Mawaddat ɓoye-ɓoyen nan bazai kaiki ko'ina ba face cigaba da dasa miki damuwar da zata iya maidaki ga abinda kika baro. Mi kike ɓoyewa? Miye baki son a sani? A zatona ko zaki iya cigaba da binnewa kowa abinda kike kallo a sirrinki ni zan kasance ba'a cikinsu ba saboda kasancewata mafi ƙololuwar SIRINKI a yanzu. Amma bazan cigaba da takura miki son sani ba ki cigaba da riƙon abunki in dai nine bazan sake tambayarki ba”. Ya ƙare maganar kamar cikin ƴar fusata zai juya yabar ɗakin. Hannunsa ta riƙo da sauri, hakanne ya sashi tsayawa cak sai dai bai juyo ba, ya dai lumshe idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Itama batare data tashi ba cikin shashshekar kukan da ke sukar masa zuciya a hankali ta furta, “Aliyu ban san miyasa kake son ji ba? Babu wani abin sha'awa ko birgewa a son jin abinda ya shuɗe da ga tarihin rayuwata. Babu wani abin alfahari ko ƙayatarwa face baƙin ciki da takaici a cikin jiyana. Taya zan faɗa maka na taɓa kashe mutum da hannayen nan nawa ne?, kuma wlhy ban taɓa jin nadamar aikatawar ba har yau har gobe da ma ƙarshen numfashi na. Aliyu ban san taya kake son na faɗa maka na rasa Nanny na data raineni tamkar uwa ba a dalilin kisan da nayi ba, ta amshi laifin daba nata ba, ta rasa ranta a dalili na, Aliyu alhakinta bazai barni na rayu cikin salama ba...” ta sake sakin kuka mai tsuma zuciya.
Sosai shima yake haɗiyar zuciya, maƙogwaronsa sai faman kai kawo yake a cikin wuyansa. Idanun maza sun masifar kaɗawa. Da ƙyar ya iya controlling temper ɗinsa tare da firzar da numfashi mai nauyi ya juyo a hankali gareta. Har lokacin hannunta a cikin nasa ya zauna a kusa da ita. Jikinsa ya jawota ya rungume, hakan sai ya bata damar sake sakin kuka tana ƙanƙamesa kamar mai gudun a rabasu. Bai hanata ba, sai tambaya da ya jeho mata kai tsaye. “Taya akai kika aikata kisan kai? Dan nasan kinada dalili mai ƙarfi Mawaddat, bakiyi kalar masu aikata irin wannan laifin bisa son zuciya ba. Please faɗamin miya faru a shekarun baya a tsakaninki da Nanny ɗinki?”.
Cikin haɗiyar zuciya da shashshekar kuka ta furta, “Johanna itace Nanny na dana buɗa ido na gani a tare da ni tamkar uwa mahaifiya. Duk da dai kafin a kaini gareta na ɗan rayu a Nigeria hannun mahaifina da matarsa, sai dai babu abinda zan iya tunawa a wannan rayuwar saboda ƙarancin shekaru na. Nanny na da nake kira da Mah-mah Ta raineni ne tamkar zinariya, tana bani dukkan gata da uwa ke bama ƴaƴa duk da kasancewarta kafira. Bata taɓa cewa nabi addininta ba balle akai gata tilasta ni. Duk da na kasance mai tsiwa da rashin ji komai nai a gareta abin farin ciki ne, sai taga zan kauce da yawa ne take saurin gyara min duk da bata kasance muslma ba. Daddy na yawan zuwa gareni, dan haka nake ɗauka shi da ita duk iyayena ne, sai da na fara ɗan wayo na fara damuwa akan ƙin kwana da Daddyna keyi a gidanmu idan yazo Germany, ya yarda ya yini da ni a gida koma ya ɗaukeni mu fita yawo amma dare nayi zai wuce masaukinsa. Nakan masa ƙorafin hakan amma sai yay murmushi kawai. Itama idan na tambayeta miyasa Daddyna baya kwana tare da mu kamar sauran abokaina da iyayensu takance min aiki ne ke hanashi hakan.........✍️
NEXT PAGE PLEASE 🚴🚴🚴🚴
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣9️⃣
Fuska ta tsuke cikin cuna baki batare data amsa masa ba. Shima sai ya sake dakewa da koma mata Smart ɗin nan mai ɗaukar kai da manna mata hauka sanda yana drivern ta. A kausashe ya furta, “In ma baki son na sani kin makaro. Domin ɗayan littafin ai yana gareni. Banyi niyyar karantawa bane kawai dan nafi son jin komai daga bakinki ba'a rubuce ba.” Da sauri ta ɗago tana kallonsa, ya ɗauke kansa gefe kamar bai ganta ba. Sai kawai taji hawaye sun cika mata ido. Cikin rawar murya ta ce, “Da gaske kakeyi?”.
“Na miki kama da ɗan wasan kwaikwayo ne da zan miki ƙarya?. Mawaddat ɓoye-ɓoyen nan bazai kaiki ko'ina ba face cigaba da dasa miki damuwar da zata iya maidaki ga abinda kika baro. Mi kike ɓoyewa? Miye baki son a sani? A zatona ko zaki iya cigaba da binnewa kowa abinda kike kallo a sirrinki ni zan kasance ba'a cikinsu ba saboda kasancewata mafi ƙololuwar SIRINKI a yanzu. Amma bazan cigaba da takura miki son sani ba ki cigaba da riƙon abunki in dai nine bazan sake tambayarki ba”. Ya ƙare maganar kamar cikin ƴar fusata zai juya yabar ɗakin. Hannunsa ta riƙo da sauri, hakanne ya sashi tsayawa cak sai dai bai juyo ba, ya dai lumshe idanunsa da suka kaɗa sukai jajur. Itama batare data tashi ba cikin shashshekar kukan da ke sukar masa zuciya a hankali ta furta, “Aliyu ban san miyasa kake son ji ba? Babu wani abin sha'awa ko birgewa a son jin abinda ya shuɗe da ga tarihin rayuwata. Babu wani abin alfahari ko ƙayatarwa face baƙin ciki da takaici a cikin jiyana. Taya zan faɗa maka na taɓa kashe mutum da hannayen nan nawa ne?, kuma wlhy ban taɓa jin nadamar aikatawar ba har yau har gobe da ma ƙarshen numfashi na. Aliyu ban san taya kake son na faɗa maka na rasa Nanny na data raineni tamkar uwa ba a dalilin kisan da nayi ba, ta amshi laifin daba nata ba, ta rasa ranta a dalili na, Aliyu alhakinta bazai barni na rayu cikin salama ba...” ta sake sakin kuka mai tsuma zuciya.
Sosai shima yake haɗiyar zuciya, maƙogwaronsa sai faman kai kawo yake a cikin wuyansa. Idanun maza sun masifar kaɗawa. Da ƙyar ya iya controlling temper ɗinsa tare da firzar da numfashi mai nauyi ya juyo a hankali gareta. Har lokacin hannunta a cikin nasa ya zauna a kusa da ita. Jikinsa ya jawota ya rungume, hakan sai ya bata damar sake sakin kuka tana ƙanƙamesa kamar mai gudun a rabasu. Bai hanata ba, sai tambaya da ya jeho mata kai tsaye. “Taya akai kika aikata kisan kai? Dan nasan kinada dalili mai ƙarfi Mawaddat, bakiyi kalar masu aikata irin wannan laifin bisa son zuciya ba. Please faɗamin miya faru a shekarun baya a tsakaninki da Nanny ɗinki?”.
Cikin haɗiyar zuciya da shashshekar kuka ta furta, “Johanna itace Nanny na dana buɗa ido na gani a tare da ni tamkar uwa mahaifiya. Duk da dai kafin a kaini gareta na ɗan rayu a Nigeria hannun mahaifina da matarsa, sai dai babu abinda zan iya tunawa a wannan rayuwar saboda ƙarancin shekaru na. Nanny na da nake kira da Mah-mah Ta raineni ne tamkar zinariya, tana bani dukkan gata da uwa ke bama ƴaƴa duk da kasancewarta kafira. Bata taɓa cewa nabi addininta ba balle akai gata tilasta ni. Duk da na kasance mai tsiwa da rashin ji komai nai a gareta abin farin ciki ne, sai taga zan kauce da yawa ne take saurin gyara min duk da bata kasance muslma ba. Daddy na yawan zuwa gareni, dan haka nake ɗauka shi da ita duk iyayena ne, sai da na fara ɗan wayo na fara damuwa akan ƙin kwana da Daddyna keyi a gidanmu idan yazo Germany, ya yarda ya yini da ni a gida koma ya ɗaukeni mu fita yawo amma dare nayi zai wuce masaukinsa. Nakan masa ƙorafin hakan amma sai yay murmushi kawai. Itama idan na tambayeta miyasa Daddyna baya kwana tare da mu kamar sauran abokaina da iyayensu takance min aiki ne ke hanashi hakan.........✍️
NEXT PAGE PLEASE 🚴🚴🚴🚴
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣9️⃣