Sashe 7
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin haka kunya ta rufe Bintu, kamar k’asa ta bud’e ta shige. Ta na mai yin k’asa da ido ta ce ‘’Ai idan Gimbiya ta gani ko ta ji ina kamshin turare ma su k’amshi haka Iya Dije kashi na ya bushe’’ Sai a sannan hankalin Iya Dije ya fara kwanciya, ta ce ‘’Yo ba sai ki 6oye yanda ba za ta gani ba, sai ki na sawa kad’an haka, ni dai ba zan mayar da wanga turare ba’’ Ajiyar zuci Bintu ta saki ganin babu yanda za ta yi dole ta hakura ta kar6a ta na mai godiya. Ita kuwa Iya Dije ko da ta samu ta cusawa Bintu turare sai ta sami kwanciyar hankali, dan da ba ta san yanda za ta yi ta biya da kud’in Aisar da ta ci ba.
Aisar kuwa sai da ya tabbatar ya kaiwa Malam Hamisu k’orafinsa kan rashin tarbiyar d’alibai da kuma zaman wata d’aliba a waje lokacin cin abinci ba tare da ya ambaci sunan Bintu ba. Malam Hamisu ya nuna rashin saninshi kan maganar yanayin cin abincin d’aliban, kuma ya yi masa alk’awarin d’aukar mataki. Saidai batun rashin tarbiyar d’aliban ya ce su ma hakuri su ke da su kasancewar kowani tsuntsu kukan gidansu ya ke, amma In sha Allahu za su k’ara tsauri kan lamarin.
Washagari da safe wajan taron d’alibai (Assembly), Mallam Hamisu ya ja kunnan d’alibai akan bin duka, musammam wanda ba sa halartar wajan cin abinci idan lokacin yayi, ya kuma tsawatar da hukunci mai tsanani muddin aka ga d’aya daga cikin d’aliban na aikata hakan. Da wannan Bintu ta sami saukin samin cin abinci tare da yan uwan ta d’alibai duk da kuwa sai da ta sha tuhuma gun Gimbiya akan zargin ko ita ta kai k’arar ta.
Kwanci tashi haka rayuwa ta kasancewa Bintu cikin makaranta. Gaba d’aya gudun Aisar ta ke, tun shi ma bai gane ba har ya zo ya gane ya daina nemanta. Ita kuwa Zahira hakuri ta je ta bashi tare da sa bakin Malam Hamisu ya hak’ura ya bari ta koma ajin na shi. Gimbiya Binta babu irin cusa kai da ba ta yiwa Aisar, amma sam ba ta gabansa bare ya san ta na yi, manyanta ma yan aji biyar da shida fama su ke bare ita karan kad’a miya acikin jerin ‘yan mata.
Da yammacin ranar lahadi, ana saura sati biyu su Bintu su fara jarabawa. Yanda garin yayi wasai, gajimare yayi lub-lub, ciyawa da bishin da ke cikin lambun sun yi kore shar, ga wani ni’imatacciyar iskar da ked’awa wanda sanya rassa da ganyayyakin bishiyun da ke cikin lambun rausayawa suna mai fuzar da feshin ruwa sanadiyar ruwan sama da ya sauka ya kuma tsaya mintina talatin da su ka wuce ne ya sanya Aisar da ke kwance kan kujerar hutun da ke k'ark’ashin d’aya daga cikin rumfunan lambun, in banda kukan tsuntsaye da kuma k’arar saukar sauran ruwan sama da yayi ragowa bisa kwanan rumfar lambun babu abun da ke tashi.
Sanye ya ke cikin bakar riga mai k’aramin hannu, da wando wanda ya ke shi ba gajere ba bai kuma kai masa har k’asa ba. Idanunsa lumshe tamkar mai bacci, ko da yake da zai sami bacci da hakan zai fi so dan kuwa tunanin da ya dad’e ya na damun sa yanzun ma shi ya sa shi gaba. Ba kuma tunanin kowa bane, face na Bintu, musammam yanzu da aikin binciken su ya k’are, Bintun ce ta zaunar da shi a makarantar da tuni ma ya dakatar da koyarwa, dan kuwa dai hakin su ya riga ya cimma ruwa a game da aikin su. Abin takaicin shi ne tsakanin sa da Bintu sai dai a aji, duk yanda zai yi ya ganta bayan aji ya gwada amma abu ya faskara, don kuwa dai Bintu gudun sa ta ke k’iri k’iri. Shi kan shi bai san meyasa ya kasa cire yarinyar daga ransa ba, amma dai yau idan har bai sa ta a idanunsa ba zai iya shiga damuwa. Gashi kuma yau lahadi ko makarantar bai shiga ba bare ya ganta a aji. Nan fa wata dabara ta fad’o masa, ya tsinci kansa ya na mai murmusawa.
Ajiyar zuci ya saki yayin da ya bud’e idanu a hankali jin d’igar ruwa bisa fuskarsa sanadiyar iska da ta kad’o wani reshe zuwa cikin rumfar. Tashi ya yi zaune ya na mai duba lokaci, k’arfe biyar daidai, ya aje hannu inda ya tashi cikin azama ya na mai k’ok’arin zura takalmi cikin k’afafunsa. Kai tsaye ya fice daga cikin lambun, ya bi ta farfajiyar gidan ya shige falonsa wanda zai sada sa da d’akin baccinsa. Cikin k’ank’anin lokaci ya sauya kaya izuwa farar jamfa da hula tare da farin takalmi. Ya gama fesa turaren sa mai kamshin gaske ya wuce cikin motarsa. Hankali kwance ya fito daga gidansa, sai gashi kan titin francophonie, kai tsaye ya nufi makarantar Soverign.
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣6⃣
Minti goma kacal ya kai shi makarantar, Allah ya taimake shi ya had’u da Iya Dije a bakin gate ta na shirin fita kenan. Tsaida Ita ya yi, ya nemi alfarmar ganin Bintu. Iya Dije da tun da ta ga Aisar da yamma haka, gashi ranar lahadi ta san banza ba ta kawo zomo kasuwa, ta yi kud’irin samun wani abu daga aljihun sa. Jin buk’atar ta sa sai ta yi hamdala cikin ran ta, ta na mai gyara tsayuwa ta ce ‘’ai kasan yanayin dokar makarantar ne Malam, an hana d’alibai kebewa da Malamai musammam irin wannan lokacin da ba na d’aukar darasi ba’’
Duk da maganar ta Iya Dije ta yiwa Aisar wani iri, jin ta yi amfani da kalmar ‘’ke6ewa’’ amma sai ya basar, ya na mai murmusawa ya ce ‘’ba ki fahimce ni ba Iya Dije, ba wai tsayar da ita zan yi ba, kawai dai sak'o zan bata, na ga fita ma za ki yi ko?’’ nan fa Iya Dije ta samu mafaka, ta amsa da ‘’eh wlh kasuwa zani, zan saro kaya duk da dai ba wani jarin arziki gare ni ba’’ ganin Aisar ya sanya hannu cikin aljihu jikin ta har rawa ya ke. Ilai kuwa sai gashi ya fito da kud’i CFA na gugan CFA, ba tare da ya k'irga ba ya mik’awa Iya dije ya na mai fad’in ‘’gashi ki k’ara kan jarin na ki’’
nan Iya Dije ta cafe kud’i saura kiris ta had’a da hannun Aisar, fad’i ta ke ‘’kai dai ba ka gajiya, madallah, yo ai in da yarda ai na yarda da kai, bara na kira maka Bintu Bala Mahuta, amma dan Allah kar ta dad’e ka ga dai ni fita zan yi’’
Aisar na murmushin nuna jin dad’i ya amsa da ‘’toh, ina nan kusa da ofishin malamai ina jira.’’ da azar6a6in jiki Iya Dije ta koma ciki ta na k'irga kud’in da aka ba ta.
Bintu na zaune cikin d’aki, kasancewar Gimbiya Binta ba ta nan ta je karatu, itama ta sami damar yin na ta karatun. Sanye ta ke cikin shigar su na bayin Sa’ayrasa dan ba ta isa ta sa kayan gida ba duk da dai yau d’in kowa ado ya ke yi. Sai ga Iya Dije ta shigo, kallo d’aya za ka mata ka tabbatar da farin cikin da ke tattare da ita. Ta na mai washe baki ta ce
‘’Bintu tashi maza ki biyo ni, Malamin ku ne ya ke neman ki, eh! Malam Aisar’’
jin sunan Aisar Bintu ta fidda Ido tare da fad’in ‘’Iye?’’
Iya Dije ba ta damu da yanayin tsoron da ya bayya na fuskar Bintu ba, ita dai burin ta shi ne ta kai ta ga Aisar ta samu ita ma ta fita,
ta ce; ‘’ke tashi mana, ni kasuwa zani kin ga dai yamma ta yi sosai, shida na yi ba lalle na samu shiga ba, kuma kayan abincin ku na sati zan kar6o’’
‘’Iya Dije dan Allah ki ce ba ki ganni ba’’ ta fad’a ta na yin rau-rau da idanu kamar mai shirin yin kuka.
Baki bud’e Iya Dije ta ce ‘’kun ji ni da yarinya, yo me zai mi ki da za ki sa ni yin k’arya da tsufa ta, na k’i na ce ban gan ki ba d’in’’
Bintu ta ce ‘’Iya Dije aradun Allah Gimbiya ta ce idan ta ganni da shi sai na lahira ya fi ni jin dad’i, ki min afuwa ki taimake ni’’
‘’wannan kuma ke ki ka sani, idan dai ba ke ki fad’a ma ta ba ina za ta san ma kin gan shi? Ko ta na nan ne?’’ Bintu ta girgiza kai alamar aha ah. ‘’toh maza yafa mayafin ki mu je’’ Bintu ta ce ai ba ta da mayafi. ‘’ai kuwa dai ba na tafi da ke ti6i ti6i da ke haka ba, budurwa kamar ki ki ce ba ki da mayafi? A garin na ku haka ki ke yawo?’’ Iya Dije ta tambaya ta na mai duban ta.
Kana Bintu ta amsa mata da ‘’ina da su, su na gida ne Gimbiya ta hana ni zuwa da kayan gida’’
Cike da nuna Allah wadai da halin Gimbiya Binta, Iya Dudu ta ce "wannan shi ne zancen 6ir in ji tusa, menene amfanin hana ki ado ko rufe jikin ki ? Ke tashi mu je ko aran zani ne na baki ki yafa ko ma d'auko wannan d’an hijabin nan da ku ke sawa ki yafa, ai yafi babu kaka ta wajan uba’’ .
Hakan ko Bintu ta yi, ta na magiya amma Iya Dije ba ta fasa jan ta ba su ka fito daga 6angaran d’akin kwanan d’alibai, tun suna wuce d’alibai wanda ke zaune farfajiyar wajan har ya zama tsilla tsilla kad’ai ake gani, musammam da ka baro sashin kwanan d'alibai su ka shigo farfajiyar makarantar. Ganin sun nufi ofishin malamai gaban Bintu ya fara fad’uwa.
Aisar kuwa sai da ya tabbatar ya kaiwa Malam Hamisu k’orafinsa kan rashin tarbiyar d’alibai da kuma zaman wata d’aliba a waje lokacin cin abinci ba tare da ya ambaci sunan Bintu ba. Malam Hamisu ya nuna rashin saninshi kan maganar yanayin cin abincin d’aliban, kuma ya yi masa alk’awarin d’aukar mataki. Saidai batun rashin tarbiyar d’aliban ya ce su ma hakuri su ke da su kasancewar kowani tsuntsu kukan gidansu ya ke, amma In sha Allahu za su k’ara tsauri kan lamarin.
Washagari da safe wajan taron d’alibai (Assembly), Mallam Hamisu ya ja kunnan d’alibai akan bin duka, musammam wanda ba sa halartar wajan cin abinci idan lokacin yayi, ya kuma tsawatar da hukunci mai tsanani muddin aka ga d’aya daga cikin d’aliban na aikata hakan. Da wannan Bintu ta sami saukin samin cin abinci tare da yan uwan ta d’alibai duk da kuwa sai da ta sha tuhuma gun Gimbiya akan zargin ko ita ta kai k’arar ta.
Kwanci tashi haka rayuwa ta kasancewa Bintu cikin makaranta. Gaba d’aya gudun Aisar ta ke, tun shi ma bai gane ba har ya zo ya gane ya daina nemanta. Ita kuwa Zahira hakuri ta je ta bashi tare da sa bakin Malam Hamisu ya hak’ura ya bari ta koma ajin na shi. Gimbiya Binta babu irin cusa kai da ba ta yiwa Aisar, amma sam ba ta gabansa bare ya san ta na yi, manyanta ma yan aji biyar da shida fama su ke bare ita karan kad’a miya acikin jerin ‘yan mata.
Da yammacin ranar lahadi, ana saura sati biyu su Bintu su fara jarabawa. Yanda garin yayi wasai, gajimare yayi lub-lub, ciyawa da bishin da ke cikin lambun sun yi kore shar, ga wani ni’imatacciyar iskar da ked’awa wanda sanya rassa da ganyayyakin bishiyun da ke cikin lambun rausayawa suna mai fuzar da feshin ruwa sanadiyar ruwan sama da ya sauka ya kuma tsaya mintina talatin da su ka wuce ne ya sanya Aisar da ke kwance kan kujerar hutun da ke k'ark’ashin d’aya daga cikin rumfunan lambun, in banda kukan tsuntsaye da kuma k’arar saukar sauran ruwan sama da yayi ragowa bisa kwanan rumfar lambun babu abun da ke tashi.
Sanye ya ke cikin bakar riga mai k’aramin hannu, da wando wanda ya ke shi ba gajere ba bai kuma kai masa har k’asa ba. Idanunsa lumshe tamkar mai bacci, ko da yake da zai sami bacci da hakan zai fi so dan kuwa tunanin da ya dad’e ya na damun sa yanzun ma shi ya sa shi gaba. Ba kuma tunanin kowa bane, face na Bintu, musammam yanzu da aikin binciken su ya k’are, Bintun ce ta zaunar da shi a makarantar da tuni ma ya dakatar da koyarwa, dan kuwa dai hakin su ya riga ya cimma ruwa a game da aikin su. Abin takaicin shi ne tsakanin sa da Bintu sai dai a aji, duk yanda zai yi ya ganta bayan aji ya gwada amma abu ya faskara, don kuwa dai Bintu gudun sa ta ke k’iri k’iri. Shi kan shi bai san meyasa ya kasa cire yarinyar daga ransa ba, amma dai yau idan har bai sa ta a idanunsa ba zai iya shiga damuwa. Gashi kuma yau lahadi ko makarantar bai shiga ba bare ya ganta a aji. Nan fa wata dabara ta fad’o masa, ya tsinci kansa ya na mai murmusawa.
Ajiyar zuci ya saki yayin da ya bud’e idanu a hankali jin d’igar ruwa bisa fuskarsa sanadiyar iska da ta kad’o wani reshe zuwa cikin rumfar. Tashi ya yi zaune ya na mai duba lokaci, k’arfe biyar daidai, ya aje hannu inda ya tashi cikin azama ya na mai k’ok’arin zura takalmi cikin k’afafunsa. Kai tsaye ya fice daga cikin lambun, ya bi ta farfajiyar gidan ya shige falonsa wanda zai sada sa da d’akin baccinsa. Cikin k’ank’anin lokaci ya sauya kaya izuwa farar jamfa da hula tare da farin takalmi. Ya gama fesa turaren sa mai kamshin gaske ya wuce cikin motarsa. Hankali kwance ya fito daga gidansa, sai gashi kan titin francophonie, kai tsaye ya nufi makarantar Soverign.
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣6⃣
Minti goma kacal ya kai shi makarantar, Allah ya taimake shi ya had’u da Iya Dije a bakin gate ta na shirin fita kenan. Tsaida Ita ya yi, ya nemi alfarmar ganin Bintu. Iya Dije da tun da ta ga Aisar da yamma haka, gashi ranar lahadi ta san banza ba ta kawo zomo kasuwa, ta yi kud’irin samun wani abu daga aljihun sa. Jin buk’atar ta sa sai ta yi hamdala cikin ran ta, ta na mai gyara tsayuwa ta ce ‘’ai kasan yanayin dokar makarantar ne Malam, an hana d’alibai kebewa da Malamai musammam irin wannan lokacin da ba na d’aukar darasi ba’’
Duk da maganar ta Iya Dije ta yiwa Aisar wani iri, jin ta yi amfani da kalmar ‘’ke6ewa’’ amma sai ya basar, ya na mai murmusawa ya ce ‘’ba ki fahimce ni ba Iya Dije, ba wai tsayar da ita zan yi ba, kawai dai sak'o zan bata, na ga fita ma za ki yi ko?’’ nan fa Iya Dije ta samu mafaka, ta amsa da ‘’eh wlh kasuwa zani, zan saro kaya duk da dai ba wani jarin arziki gare ni ba’’ ganin Aisar ya sanya hannu cikin aljihu jikin ta har rawa ya ke. Ilai kuwa sai gashi ya fito da kud’i CFA na gugan CFA, ba tare da ya k'irga ba ya mik’awa Iya dije ya na mai fad’in ‘’gashi ki k’ara kan jarin na ki’’
nan Iya Dije ta cafe kud’i saura kiris ta had’a da hannun Aisar, fad’i ta ke ‘’kai dai ba ka gajiya, madallah, yo ai in da yarda ai na yarda da kai, bara na kira maka Bintu Bala Mahuta, amma dan Allah kar ta dad’e ka ga dai ni fita zan yi’’
Aisar na murmushin nuna jin dad’i ya amsa da ‘’toh, ina nan kusa da ofishin malamai ina jira.’’ da azar6a6in jiki Iya Dije ta koma ciki ta na k'irga kud’in da aka ba ta.
Bintu na zaune cikin d’aki, kasancewar Gimbiya Binta ba ta nan ta je karatu, itama ta sami damar yin na ta karatun. Sanye ta ke cikin shigar su na bayin Sa’ayrasa dan ba ta isa ta sa kayan gida ba duk da dai yau d’in kowa ado ya ke yi. Sai ga Iya Dije ta shigo, kallo d’aya za ka mata ka tabbatar da farin cikin da ke tattare da ita. Ta na mai washe baki ta ce
‘’Bintu tashi maza ki biyo ni, Malamin ku ne ya ke neman ki, eh! Malam Aisar’’
jin sunan Aisar Bintu ta fidda Ido tare da fad’in ‘’Iye?’’
Iya Dije ba ta damu da yanayin tsoron da ya bayya na fuskar Bintu ba, ita dai burin ta shi ne ta kai ta ga Aisar ta samu ita ma ta fita,
ta ce; ‘’ke tashi mana, ni kasuwa zani kin ga dai yamma ta yi sosai, shida na yi ba lalle na samu shiga ba, kuma kayan abincin ku na sati zan kar6o’’
‘’Iya Dije dan Allah ki ce ba ki ganni ba’’ ta fad’a ta na yin rau-rau da idanu kamar mai shirin yin kuka.
Baki bud’e Iya Dije ta ce ‘’kun ji ni da yarinya, yo me zai mi ki da za ki sa ni yin k’arya da tsufa ta, na k’i na ce ban gan ki ba d’in’’
Bintu ta ce ‘’Iya Dije aradun Allah Gimbiya ta ce idan ta ganni da shi sai na lahira ya fi ni jin dad’i, ki min afuwa ki taimake ni’’
‘’wannan kuma ke ki ka sani, idan dai ba ke ki fad’a ma ta ba ina za ta san ma kin gan shi? Ko ta na nan ne?’’ Bintu ta girgiza kai alamar aha ah. ‘’toh maza yafa mayafin ki mu je’’ Bintu ta ce ai ba ta da mayafi. ‘’ai kuwa dai ba na tafi da ke ti6i ti6i da ke haka ba, budurwa kamar ki ki ce ba ki da mayafi? A garin na ku haka ki ke yawo?’’ Iya Dije ta tambaya ta na mai duban ta.
Kana Bintu ta amsa mata da ‘’ina da su, su na gida ne Gimbiya ta hana ni zuwa da kayan gida’’
Cike da nuna Allah wadai da halin Gimbiya Binta, Iya Dudu ta ce "wannan shi ne zancen 6ir in ji tusa, menene amfanin hana ki ado ko rufe jikin ki ? Ke tashi mu je ko aran zani ne na baki ki yafa ko ma d'auko wannan d’an hijabin nan da ku ke sawa ki yafa, ai yafi babu kaka ta wajan uba’’ .
Hakan ko Bintu ta yi, ta na magiya amma Iya Dije ba ta fasa jan ta ba su ka fito daga 6angaran d’akin kwanan d’alibai, tun suna wuce d’alibai wanda ke zaune farfajiyar wajan har ya zama tsilla tsilla kad’ai ake gani, musammam da ka baro sashin kwanan d'alibai su ka shigo farfajiyar makarantar. Ganin sun nufi ofishin malamai gaban Bintu ya fara fad’uwa.