Sashe 3
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shekarar Bintu goma sha biyar da haihu,mahaifin ta babban bawan wazirin Sa’ayrasa ne,kasancewar haka tare da alfarmar mahaifiyar ta da take babbar baiwar matar sarki mai rasuwa ya sa da za a kai Gimbiya Binta makarantar kwana aka zab’e ta cikin bayi domin kula da ita,dan ko a cikin ‘ya’yan bayi babu wanda ya san fada da al’adun ciki kamar Bintu. Ta wannan hanya aka rab’uka ta cikin makarantar su Gimbiya Binta musammam dan hidimar ta. Amma fa a wahalce ta ke samin ilimi,kai ba ma ilimi ba komai na Bintu cike ya ke da wahala. Wanka ne kawai ba ta yiwa Gimbiya Binta,amma komai na ta ita ce. Wanki da guga da a k’aidar makarantar akwai mai yi musu amma ita Gimbiya Binta sam ba ta yarda sai dai Bintu ta mata,hatta jakar makarantar ta ma Bintu ke gyarawa ta aukar mata. Idan jinga aka ba su sai dai ta yi na ta ta kuma yi na Gimbiya Binta, sai dai idan malamin da ya san rubutun su ne shi ne sai ta jira idan Bintu ta gama ta kwafa. Rubutu kuwa idan an mu su a allo sai dai ta kwafi na Gimbiya Binta,idan sun dawo aki ta kwafi na ta.
Batun wajan kwana kuwa aki aya su ke,duk da gadaje biyu ne a akin ba ta isa ta kwanta a gado Gimbiya Binta na gado ba, ah ah sai dai ta sami yar tabarma ta rab’ike daga can gefe a k’asa. Tun masu kula da akin kwanan na magana har sun hakura sun yi shiru dan sun ga tsakanin baiwa da uwar gijiyar ta sai Allah. Bintu ba ta isa ta riga ta bacci ba,kuma dole ta riga ta tashi ta ha a mata ruwan wanka. Wajan cin abunci ba ta isa ta zauna cikin yan uwan ta alibai ta ci abunci ba,sai dai ta jira Gimbiya ta gama,ta raka ta aki ko aji sannan ta dawo ta ci na ta. Kuma a duk in da su ke sai ta tabbatar kowa ya san Bintu iyar bayi ce, shi ya sa ma ta hana ta sa kaya in dai ba shigar bayin Sa’ayyarasa ba idan ranar sa kayan su na gida yayi.
Allah ya yiwa Bintu wani abu wai shi tsayi da diri,dan kuwa jikin ta ya girmi shekarun ta. A shekarun ta tana da zubin cikakkiyar budurwa idan ba fuskar ta aka kalla ba ba wanda ba ya b'oye shekarun na ta.
Bintu baka ce,irn bakin nan na wayayyun matan nan da ba sa shafa man da zai sake mu su kala. Doguwar fuska gare ta,amma ba mai tsayi sosai ba,ta na da manyan idanu ga hanci har baka,sai wushirya da ke mata kyau duk sanda ta dara ko ta bu e hakora. Ta na da suma matuka,ko ta aure kan ta da kallabi yawan sumar be b’oyuwa.
Daga ita har Gimbiya Binta aji uku suke. Ba ta da buri da ya wuce su kai aji shi da su gama makarantar ko ta huta da jarabar Gimbiya,dan kuwa ko k’awaye Bintu ba da shi a makarantar.
Aisar Gaddafi Nur
Aisar saurayi ne mai kimanin shekara talatin a duniya. Aisar ya da e cikin aikin sa da ya ke matuk’ar so tun kan mahaifin sa ya zama shugaban kasan jamhuriyyar Nijar. Aiki ne wanda ake mu su lakani da mutan b’oye,wato masu bincike da kula da kasa amma ta k’ark’ashin k’asa. Tin hawan mahaifin sa kujerar shugaban k’asa ya na ji ya na gani dole aka dakatar shi saboda yanayin aikin na su na sirri ne hatta sunan da ya ke amfani da shi cikin aikin da ban ya ke da sunan sa na yanka,ba zai yiyu a ha a da siyasa ba dan ba mamaki ma wata rana aiki ya bi ta kan gidan na su. Amma shi ba haka ya so ba. Hakan ya sa sam Aisar ba ya san shiga sabgar gidan gwamnati ko abun da ya shafi harkar siyasar baban shi. Ko zama gidan shugaban k’asan ma be cika yi ba,in ka gan shi ciki toh wajan iyayen sa ya je gaidawa ya tafi,in da Allah ya taimaka ba shi ka ai ba ne ya na da yayye ba laifi, dan ba kowa ba ne ma ya san shi a matsayin an shugaban kasa. Hakan be sa kungiyar Aisar janye dakatar da shi da su ka yi ba,har ma ya fidda rai ya hakura har sai baban shi ya sauka kwatsam ya ji kiran aiki na wani bincike da ya bi ta kan wani kamfani da ke kusa da makarantar su Bintu. Yayi murna kwarai duk da kuwa aikin ba nasa ba ne,shi kawai taimako zai yi shi ya sa sai dai ya rab’uke daga gefe har sai lokacin taimakon yayi. Kungiyar ta su ce ta ba shi izinin neman koyarwa a nan makarantar ta sovereign girls secondry school,su ka kuma ce ya je da sunan sa na ainihi tun da hawan baban sa mulki an fara ya awa cewa ya na kungiyar,kasancewar shi cikin makarantar shi zai ba su damar yin basaja,yanda wancan kamfanin ba za su yi zargin su ake bi ba har su gama binciken su.
2/01/2000
Zaune su ke cikin aji. Kamar yanda ta saba kujerar ta na bayan na Gimbiya Binta. Ta doka uban tagumi in ban da k'ugin yunwa babu abun da cikin ta ya ke dan kuwa raban ta da abunci tin na dare da ke yau sun makara, hakan be sa Gimbiya ta aga mata k’afa ba ta bari ta ci abunci lokacin da ta ke cin abunci,kafin ta gama kuma aka shiga aji. Ta na ji ta na gani sai hakura ta yi.
Duka duka ba su kai talatin ba cikin ajin amma gaba aya sun ciki ajin da surutu. Hirar abubuwa masu tsada da k’asashen da su ka tab’a zuwa kowa ya ke. Ita kuwa Bintu da hirar ta su ko hankali ba ya bata sai hamma ta ke,ta kalli agogon bangon ajin,awa aya ya rage a fita gajeran hutu dan cin abunci. Malamin da ya kamata ya shigo kuma ya ki shigowa, sai kawai ta kifa kan ta bisa teburi.
Shirun da ta ji anyi ya tabbatar mata da Malam ya shigo aji. Ta yi sauri ta ago kan ta sai gashi kowa ya tashi tsaye ita ka ai ce zaune,baki bu e ganin wanda ya ke tsaye gaban ajin. Kamar yanda ta gan shi jiya yau ma bak’ak’en kaya ne sanye jikin sa,idanun sa rufe da bakin glass. Da kyar ta sa mu ta ja jikin ta ta tashi.
Gaishe su yayi cikin harshen turanci nan da nan su ma su gaishe shi. Ya umarce su da su zauna. Da zaman su da jin wani abu ya sauko mata lokaci guda ne,ta yi kasake ta na tunanin wannan wani irin saban lamari ne? Can dai ta yi tunanin dan wannan abun da ya saba zubo mata lokaci lokaci ne.
Malam ya gabatar da kan sa a matsayin saban malamin su na fannin zaman lafiya da sulhu [peace and conflict resolution" ta re da fa a ma su sunan sa wato Aisar Gaddafi Nur. Ko da jin sunan aji aka fara kus kus, daga fa in
"Gaddafi Nur shugaban kasa?’’
sai mai fa in
"haba da ma ni na ga yayi min kama da wanda na sani,ashe dan shugaban kasa ne’’
wata kuma
"toh me zai yi da koyarwa kuma?ba mamaki su nan ne ya zo aya dan kuwa an shugaban kasa ya fi karfin koyarwa’’
Ita dai Bintu ta saki baki ta na kallan sa,shi ko lura da ita be yi ba. Gashi ta na fama da wani saban lamari da ke zubo mata har ta na ji ta an fara jikewa. Tun ta na gane abun da ya ke fa a har ta zo ta dena dan kuwa ta fita hayyacin ta. Har fitar sa be lura da ita ba,ita kuwa gaba aya hankalin ta a tashe ya ke ganin abun da ya b’ata ba kayan makarantar ta ba hatta in da ta ke zaune.
Aisar na fita jiniya ta yi k’ara,lokacin fita hutun karamin lokaci yayi,dalibai su ka fara fita domin cin abunci da sauran su. Amma tashi ya gagari Bintu. Jaka Gimbiya Binta ta cilla mata yanda ta saba,wato ta auka ta biyo bayan ta. Murya na rawa Bintu ta furta
"dan darajar Allah Gimbiya ki yi min rai ki gafarce ni,na tuba’’
cike da mamaki ta juyo ta na duba ta,yan aji tuni kowa ya watse daga ita sai kawayen ta biyu masu masifar girman kai,Ruqayya da Zahira.
Zahirar ce ta ce
"kun ga shashashar banza,me ki ka yi da za ki hau magiya kamar iyar marok’a?’’
Ruqayya ta amsa da
"to menene banbamcin iyar bayi da ta marok’a?’’
Cike da nuna b’acin rai Gimbiya Binta ta ce ‘’jakar tawa ce ba za ki sami damar auka ba ko kuwa tashin ne ya gagare ki?’’
Bintu na kuka ta ce
"Allah shi taimake ki,wani abu ne kamar jini ya zubo min.......’’
‘’JINI!’’
Ruqayya da Zahira su ka ha a baki yayin da su ka ja gefe cikin nuna kyamkya mi. A wulakance Gimbiya ta ce
"duk sanda jinin ya dena zubo mi ki kya tashi,dan Allah ku zo mu tafi ko na dai na ganin wannan k’azantar’’
Zahira ce ta auki jakar na ta su ka tafi su ka barni. Tini duk wata yunwa ta dena jin ta,ta aura kan ta bisa taburi ta na hawaye,ta rasa in da za ta sa kan ta.
Ba ta jima a haka ba ta ji wani sanyayyen kamshi ya bakonci hancin ta,a hankali ta ago. Hannun sa ruk'e da bakin gilashin sa,fuskar sa auke da alamar tambaya, ya ce
‘’wannan fuskar ina na san ta ne?’’
Bintu ta yi saurin kau da kai gefe ta na mai adduar Allah kar ya tuna. Ai kuwa dai adduar ta ba ta karb’u ba jin ya ce
"Sa’ayyarsa,tabbas. Dama ke daliba ce a makarantar nan?me ya same ki ki ke kuka?ko dama ke kullum cikin tashin hankali ki ke? na wucewa na hango ki kai kife kan tebur bayan yan uwan ki dalibai suna can suna cin abunci’’
Batun wajan kwana kuwa aki aya su ke,duk da gadaje biyu ne a akin ba ta isa ta kwanta a gado Gimbiya Binta na gado ba, ah ah sai dai ta sami yar tabarma ta rab’ike daga can gefe a k’asa. Tun masu kula da akin kwanan na magana har sun hakura sun yi shiru dan sun ga tsakanin baiwa da uwar gijiyar ta sai Allah. Bintu ba ta isa ta riga ta bacci ba,kuma dole ta riga ta tashi ta ha a mata ruwan wanka. Wajan cin abunci ba ta isa ta zauna cikin yan uwan ta alibai ta ci abunci ba,sai dai ta jira Gimbiya ta gama,ta raka ta aki ko aji sannan ta dawo ta ci na ta. Kuma a duk in da su ke sai ta tabbatar kowa ya san Bintu iyar bayi ce, shi ya sa ma ta hana ta sa kaya in dai ba shigar bayin Sa’ayyarasa ba idan ranar sa kayan su na gida yayi.
Allah ya yiwa Bintu wani abu wai shi tsayi da diri,dan kuwa jikin ta ya girmi shekarun ta. A shekarun ta tana da zubin cikakkiyar budurwa idan ba fuskar ta aka kalla ba ba wanda ba ya b'oye shekarun na ta.
Bintu baka ce,irn bakin nan na wayayyun matan nan da ba sa shafa man da zai sake mu su kala. Doguwar fuska gare ta,amma ba mai tsayi sosai ba,ta na da manyan idanu ga hanci har baka,sai wushirya da ke mata kyau duk sanda ta dara ko ta bu e hakora. Ta na da suma matuka,ko ta aure kan ta da kallabi yawan sumar be b’oyuwa.
Daga ita har Gimbiya Binta aji uku suke. Ba ta da buri da ya wuce su kai aji shi da su gama makarantar ko ta huta da jarabar Gimbiya,dan kuwa ko k’awaye Bintu ba da shi a makarantar.
Aisar Gaddafi Nur
Aisar saurayi ne mai kimanin shekara talatin a duniya. Aisar ya da e cikin aikin sa da ya ke matuk’ar so tun kan mahaifin sa ya zama shugaban kasan jamhuriyyar Nijar. Aiki ne wanda ake mu su lakani da mutan b’oye,wato masu bincike da kula da kasa amma ta k’ark’ashin k’asa. Tin hawan mahaifin sa kujerar shugaban k’asa ya na ji ya na gani dole aka dakatar shi saboda yanayin aikin na su na sirri ne hatta sunan da ya ke amfani da shi cikin aikin da ban ya ke da sunan sa na yanka,ba zai yiyu a ha a da siyasa ba dan ba mamaki ma wata rana aiki ya bi ta kan gidan na su. Amma shi ba haka ya so ba. Hakan ya sa sam Aisar ba ya san shiga sabgar gidan gwamnati ko abun da ya shafi harkar siyasar baban shi. Ko zama gidan shugaban k’asan ma be cika yi ba,in ka gan shi ciki toh wajan iyayen sa ya je gaidawa ya tafi,in da Allah ya taimaka ba shi ka ai ba ne ya na da yayye ba laifi, dan ba kowa ba ne ma ya san shi a matsayin an shugaban kasa. Hakan be sa kungiyar Aisar janye dakatar da shi da su ka yi ba,har ma ya fidda rai ya hakura har sai baban shi ya sauka kwatsam ya ji kiran aiki na wani bincike da ya bi ta kan wani kamfani da ke kusa da makarantar su Bintu. Yayi murna kwarai duk da kuwa aikin ba nasa ba ne,shi kawai taimako zai yi shi ya sa sai dai ya rab’uke daga gefe har sai lokacin taimakon yayi. Kungiyar ta su ce ta ba shi izinin neman koyarwa a nan makarantar ta sovereign girls secondry school,su ka kuma ce ya je da sunan sa na ainihi tun da hawan baban sa mulki an fara ya awa cewa ya na kungiyar,kasancewar shi cikin makarantar shi zai ba su damar yin basaja,yanda wancan kamfanin ba za su yi zargin su ake bi ba har su gama binciken su.
2/01/2000
Zaune su ke cikin aji. Kamar yanda ta saba kujerar ta na bayan na Gimbiya Binta. Ta doka uban tagumi in ban da k'ugin yunwa babu abun da cikin ta ya ke dan kuwa raban ta da abunci tin na dare da ke yau sun makara, hakan be sa Gimbiya ta aga mata k’afa ba ta bari ta ci abunci lokacin da ta ke cin abunci,kafin ta gama kuma aka shiga aji. Ta na ji ta na gani sai hakura ta yi.
Duka duka ba su kai talatin ba cikin ajin amma gaba aya sun ciki ajin da surutu. Hirar abubuwa masu tsada da k’asashen da su ka tab’a zuwa kowa ya ke. Ita kuwa Bintu da hirar ta su ko hankali ba ya bata sai hamma ta ke,ta kalli agogon bangon ajin,awa aya ya rage a fita gajeran hutu dan cin abunci. Malamin da ya kamata ya shigo kuma ya ki shigowa, sai kawai ta kifa kan ta bisa teburi.
Shirun da ta ji anyi ya tabbatar mata da Malam ya shigo aji. Ta yi sauri ta ago kan ta sai gashi kowa ya tashi tsaye ita ka ai ce zaune,baki bu e ganin wanda ya ke tsaye gaban ajin. Kamar yanda ta gan shi jiya yau ma bak’ak’en kaya ne sanye jikin sa,idanun sa rufe da bakin glass. Da kyar ta sa mu ta ja jikin ta ta tashi.
Gaishe su yayi cikin harshen turanci nan da nan su ma su gaishe shi. Ya umarce su da su zauna. Da zaman su da jin wani abu ya sauko mata lokaci guda ne,ta yi kasake ta na tunanin wannan wani irin saban lamari ne? Can dai ta yi tunanin dan wannan abun da ya saba zubo mata lokaci lokaci ne.
Malam ya gabatar da kan sa a matsayin saban malamin su na fannin zaman lafiya da sulhu [peace and conflict resolution" ta re da fa a ma su sunan sa wato Aisar Gaddafi Nur. Ko da jin sunan aji aka fara kus kus, daga fa in
"Gaddafi Nur shugaban kasa?’’
sai mai fa in
"haba da ma ni na ga yayi min kama da wanda na sani,ashe dan shugaban kasa ne’’
wata kuma
"toh me zai yi da koyarwa kuma?ba mamaki su nan ne ya zo aya dan kuwa an shugaban kasa ya fi karfin koyarwa’’
Ita dai Bintu ta saki baki ta na kallan sa,shi ko lura da ita be yi ba. Gashi ta na fama da wani saban lamari da ke zubo mata har ta na ji ta an fara jikewa. Tun ta na gane abun da ya ke fa a har ta zo ta dena dan kuwa ta fita hayyacin ta. Har fitar sa be lura da ita ba,ita kuwa gaba aya hankalin ta a tashe ya ke ganin abun da ya b’ata ba kayan makarantar ta ba hatta in da ta ke zaune.
Aisar na fita jiniya ta yi k’ara,lokacin fita hutun karamin lokaci yayi,dalibai su ka fara fita domin cin abunci da sauran su. Amma tashi ya gagari Bintu. Jaka Gimbiya Binta ta cilla mata yanda ta saba,wato ta auka ta biyo bayan ta. Murya na rawa Bintu ta furta
"dan darajar Allah Gimbiya ki yi min rai ki gafarce ni,na tuba’’
cike da mamaki ta juyo ta na duba ta,yan aji tuni kowa ya watse daga ita sai kawayen ta biyu masu masifar girman kai,Ruqayya da Zahira.
Zahirar ce ta ce
"kun ga shashashar banza,me ki ka yi da za ki hau magiya kamar iyar marok’a?’’
Ruqayya ta amsa da
"to menene banbamcin iyar bayi da ta marok’a?’’
Cike da nuna b’acin rai Gimbiya Binta ta ce ‘’jakar tawa ce ba za ki sami damar auka ba ko kuwa tashin ne ya gagare ki?’’
Bintu na kuka ta ce
"Allah shi taimake ki,wani abu ne kamar jini ya zubo min.......’’
‘’JINI!’’
Ruqayya da Zahira su ka ha a baki yayin da su ka ja gefe cikin nuna kyamkya mi. A wulakance Gimbiya ta ce
"duk sanda jinin ya dena zubo mi ki kya tashi,dan Allah ku zo mu tafi ko na dai na ganin wannan k’azantar’’
Zahira ce ta auki jakar na ta su ka tafi su ka barni. Tini duk wata yunwa ta dena jin ta,ta aura kan ta bisa taburi ta na hawaye,ta rasa in da za ta sa kan ta.
Ba ta jima a haka ba ta ji wani sanyayyen kamshi ya bakonci hancin ta,a hankali ta ago. Hannun sa ruk'e da bakin gilashin sa,fuskar sa auke da alamar tambaya, ya ce
‘’wannan fuskar ina na san ta ne?’’
Bintu ta yi saurin kau da kai gefe ta na mai adduar Allah kar ya tuna. Ai kuwa dai adduar ta ba ta karb’u ba jin ya ce
"Sa’ayyarsa,tabbas. Dama ke daliba ce a makarantar nan?me ya same ki ki ke kuka?ko dama ke kullum cikin tashin hankali ki ke? na wucewa na hango ki kai kife kan tebur bayan yan uwan ki dalibai suna can suna cin abunci’’