Sashe 15
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanciya Gimbiya K’amariyya ta yi gami da runtse idanu, sannan ta furta ‘’Barde ne’’
Cikin nuna rashin fahimta Gimbiya Binta ta maimata ‘’Barde ne?’’
Idanunta ta bud’e ta na mai duban Gimbiya Binta ta ce ‘’Soyayya na ke da Yerima Barde na Fabarusa!’’
Wato ba Gimbiya Binta ba, hatta Bintu da ke can gefe sai da ta tsaya cak ta na fidda idanu jin batun na Gimbiya K’amariyya cikin ran ta tana mai maimaita ‘’Yerima Barde mai kyawun duniya? Kai ba k’aramin baiwa Allah yayiwa Gimbiya K'amariyya ba’’
Cikin k’aguwa Gimbiya Binta ta ce "Didi ina ku ka had’u? Takawa(sarki) ya sani? Da gaske kyawunshi ya wuce na kowa a duniya?’’
‘’Wanga tambayoyi haka kauna(kanwa) ta? Kimin d’aya bayan d’aya’’
Kana Gimbiya Binta ta ce ‘’Toh, ina kuka had’u?’’
‘’A k’asa mai tsarki mu ka had’u, kin san mun je ki na makaranta’’
‘’Ya san ke wacece kuwa?’’
Gimbiya K’amariyya na mai d’aga mata hannu ta ce ‘’Tsaya dai ki ji komai, bayan had’uwar mu, jinin mu ya had’u, hallo mu ka kulla soyayya mai k’arfi, kullum cikin waya mu ke ta sabuwar wayar tafi da gidanka da ya shigo k’asar ga, mun yi alk’awarin amre(aure) da kuma kawo k’arshen gaba da ke tsakanin masarautar nan ta mu guda biyu, hallo hakan ne ma ya sa Allah ya had’a mu’’
Gaba d’aya Bintu ta manta da aikin da aka saka ta, ta saki baki da hanci ta na jin lamarin ubangiji, ‘’Ashe dai da rabon za ta ga Yerima Barde a rayuwarta’’ Farin cikin da ya mamaye ranta kenan. Kamar daga sama ta ji an daka mata tsawa
‘’Yallah can (dalla can) makira fita ki ba mu wuri! Ki ga yanda ta saki baki da hanci ta na jin mutane, wato ki sami wanda za ki d’auka ki watsa rariya(waje) ko?’’
A firgice Bintu ta dawo cikin hayyacin ta ta na mai raba idanu kamar 6era cikin tarko yayin da ta zube k’asa.
Gimbiya Binta bata gushe ba ta k’ara da ‘’Idan na ji wanga magana ta hita rariya(idan na ji wannan maganar ta fita waje) sai dai uwar ki ta haifi wata! Aradu ma kuwa!’’
‘’Lalle ma kuwa, yo to ai na manta tana nanniya’’ Cewar K’amariyya ta na duban Bintu. Jikin Bintu na rawa ta ce ‘’Tuba na ke! Aradun Allah na tuba, in na kara kada rabbi ya gafirce ni!’’
‘’Hita yallah(fita dallah) jaka kawai!’’ Gimbiya Binta ta daka mata tsawa. Tuni Bintu ta tashi jiki na rawa ta fita.
Bayan fitarta Gimbiya Binta ta ce "Wai har wanga d’iyar bayin ni za ta yiwa alherin maye ramuwa da mugunta? Har ta isa had’a samrayi(saurayi) da ni?’’
Baki bud’e Gimbiya K'amariyya ta ce ‘’Kwarainiya mota a randa! Shi ko wanene wanga samrayi?’’
Gimbya Binta na mai murmushi ta ce ‘’Aisar Gaddafi Nur."
Cike da mamaki Gimbiya K'amariyya ta ce ‘’Kai haba dan Allah, Aisar dan shugaban k'asa gide?"
Gimbiya Binta ta gyad'a mata kai.
"Yo to in ban da abun ki ina tusa zata hure wuta? Ina d’iyar bayi ina dan mulki? Ai komai tsiyar 6arawo ya bar wuta a murhu’’ Cewar Gimbiya K'amariyya.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣3⃣
Kai Gimbiya Binta ta girgiza, tana mai fad’in ‘’Ba ki san makircin wanga d’iya ba ne Didi, bari dai na baki labarin kad’an daga cikin halin ta.’’ Nan fa ta saka Bintu a faifai, k’arya da gaskiya haka ta had’a ta shedawa Gimbiya K’amariyya, ba don komai ba ko don ta samu mai taya ta saka baki a hana Bintu komawa makaranta.
Jiki na kyarma Bintu ta fito, Allah ya sa shigowar Inna kenan su ka had’u a rariya. Inna na ganin Bintu ta san akwai abin da ke damunta, tambayar duniyar nan Inna ta yi mata, amma ta k’i fad’a mata, sai k’arya ba ta jin dad’i ta yi mata. Ta na mai mata Allah ya sauwake ta ja ta gefe ta bata fatan dusan da ta taho mata da shi dan karin kumallo kafin ta yi na ta wajan, tabar Bintu ta na zabga loma.
*** *** ***
Da yammaci, sati guda kenan da dawowa su Bintu.
Bintu kwance tare da Inna da Habibu zaune bisa tabarma a tsakar gida su na shan iska dan kuwa zafi ake na gaske ma kuwa. Inna da ya Habibu ke hirar halin da ake ciki na fari a yanki, su na muhawarar yanda za a sami mafita, in da Bintu ta yi kwance can gefe, gaba d’aya tunanin Aisar ne ya addabi rayuwar ta, dan ko yanzu ma tunanin na shi ta ke yayinda ta ke murza zobensa da ke sanye cikin yatsunta.
Baba ne ya shigo kamar an jefoshi, fad’i ya ke ‘’An dai wad’i(fad’i) ba nauyi!'’ Tashi su ka yi tsaye a tare, Inna na mai tambayar ‘’Malam lafiya kuwa?’’
Baba ya ce ‘’Yo to tunda aka fara fari ina mu ka ga lafiya? Yau fa kur’ia aka doka a fada, kuma sakamakon shi ne za mu nemi sulhu da kuma taimako daga wajan mak’iya abokan gaba, eh masarautar Fabarusa!’’
Babu wanda bai girgiza ba jin kalamin na Baba. Habibu ne ya ce "Gide a rasa in da za a k’ask’antar da kai sai wajan abokan gaba?’’ Baba na mai d’aga kafad’a ya ce "Ta dai faru ta k’are an yiwa mai damo d’aya sata, don kuwa magatakarda ya tura wasik’a zuwa Fabarusa, idan an amsa gobe da sassahe za a d’auki hanya tare da Uban Gabasawa(Sarki) da kansa zuwa wajan abokan gaba nema sulhu’’
Ya na gama fad’in haka ya shige ciki Inna na mai bin bayansa. Shi kuwa Habibu silifa d’insa ya ja ya saka sannan ya fice, wato ya fita yad’a zancen kenan. Bintu kuwa komawa ta yi zaune abin ta, duk da dai itama ta yi tunanin neman taimako daga Fabarusa, jin za a je d’in da gaske sai ta tsinci kanta tana mai fad’uwar gaba.
********
Washegari da sassafe Mai Martaba da tawagarsa su ka d’auki hanyar Faburusa. Babban gida sam babu armashi kowa cikin fargaba ya ke. Gimbiya K’amariyya tafi kowa shiga tashin hankali, gashi tun jiya ta ke kiran wayar Yerima Barde amma wayar ba ta shiga. Gani ta ke kamar alakarsu ce ta zo k’arshe. Ita kuwa Gimbiya Binta damuwarta daban ne, tun dawowar su ta ke ta sak’e-sak’e akan abinda za ta ce da Takawa(sarki) ya canza mata baiwa, dan ita aradu ba za ta koma makaranta da Bintu ba.
Ranar Allah ya taimaki Bintu ta yi aiki da hidimarta cikin Babban gida ba tare da ta sami matsala daga wajan Gimbiya Binta ba. Da yammacin ranar ta raka Yerima Nadir Lambu, nan su ka ta tad’in su kamar ta sami babban mutum. Labarin makarantar su ya ce ta bashi, nan fa Bintu tai ta bashi, har da labarin Aisar. Bata san ta na kewan sa sosai ba sai da take maganar sa a zahiri ba a zuci ba, wata k’ila ma ya manta da wata Bintu, abun da take fad’awa kan ta kenan. Shi kuwa Yerima Nadir kallon ta kawai ya ke ba tare da ya fahimci in da ta dosa ba, ballantana ya gane halin da ta ke ciki.
******
Bayan magrib ta koma gida, shiru har lokacin sarki be dawo ba. Bayan sun ci abinci suna kwance a falo ita da Inna, sun ci sa’a akwai wutar lantakarki, fanka ke kad’awa ta na mai fitar da k’ara alamar ta fara gazawa.Akwatin radiyon Inna su ke sauraro in da ake labaran duniya.
Jin mai karanto labarai ya ce ‘’Jikin shugaban k’asa Gaddafi Nur ya tashi, za'a fitar da shi zuwa k’asar waje domin ba shi taimako’’ Ya sa Bintu tashi zaune da sauri ta na mai tambayar ‘’Inna daman shugaban K’asa be da lafiya?’’
‘’Eh Allah sarki ai be da lafiya, yo to da k’alau ya ke ai da tuni ya magance wanga fari da mu ke ciki, dan ba kya sauraran labarai ne shi ya sa ba ki ji ba’’ Inna ta amsa mata.
Bintu na mai dafe kai ta ce "innalillahi wa innailaihirrajiun, Allah sarki Monsieur Aisar, suna cikin tashin hankali’’
Inna ta dubeta, ‘’Waye shi kuma Bintu?’’
Nan Bintu ta kwashe labarin Aisar ta fad’awa Innar ta. Fuskarta na nuna rashin jin dad’in labarin, Inna ta had’e fuska. ‘’Ai da walakin goro a miya, shi ya sa mana na ga kin dawo wata wuri wuri da ke, d’an shugaban k’asa Bintu?’’
Bintu na mai tura baki ta ce ‘’Yo to Inna minene ciki? Ba fa wani abu ba ne taimako gareshi kawai........’’
‘’Wani taimako? Chiim zanne la nya bangin! (rufa min baki ko na buge ki)’’ Inna ta katse ta, ta k’ara da ‘’Taimako ne har da siya miki turare ma su tsada haka Bintu? Binta sudan? Kafin kafin? Danduala? Turaren da sai Saraki kad’ai ke sawa? Kuma ki na dai ganin yanda Gimbiya ta yi mi ki saboda shi? ngoy awo gulgin d3! (ai ga abinda nake fada), yanzu ba za ta bari ko koma maranta (makaranta) da ke ba!"
Komawa Bintu ta yi ta kwanta, ta na mai lumshe idanu. Kana ta ce ‘’Allah ya ba shi lafiya’’
"Wa fa?’’ Inna ta tambaya. Bintu na mai bud’e idanunta ta ce ‘’Mahaifin Monsieur’’
Tsaki Inna ta ja, kafin ta amsa da ‘’Yo to amin, amma kanki ya kamata ki yiwa addu’a fero (yarinya) a halin da ki ke ciki, ki ma cire wannan mutumin daga ranki, can ga su gada zomo ya ji kid’an farau ta’’
‘’Inna Allah na sa a raina." Cewar Bintu. Kamar daga sama su ka jiyo Habibu daga tsakar gida ya ce
"Kin gama komai kauna(kanwa) ta?''
Ashe duk maganar da su ke ya na can zaune tsakar gida ya na jiyo su ba su sani ba. Murmushi Bintu ta saka, ita kuwa Inna cewa ta yi ‘’Ala sakaa (Allah ya kare)"
Washegari da asubar fari Bintu na tashi daga barci Baba ne ya fad’o ranta, don kuwa har su ka yi bacci be dawo ba. A tsakar gida ta tadda Inna ta na alwala, ka na ta ce ‘’Inna barka da asuba’’
‘’Barka dai Bintu, kin tashi k’alau?’’ Inna ta amsa mata.
Cikin nuna rashin fahimta Gimbiya Binta ta maimata ‘’Barde ne?’’
Idanunta ta bud’e ta na mai duban Gimbiya Binta ta ce ‘’Soyayya na ke da Yerima Barde na Fabarusa!’’
Wato ba Gimbiya Binta ba, hatta Bintu da ke can gefe sai da ta tsaya cak ta na fidda idanu jin batun na Gimbiya K’amariyya cikin ran ta tana mai maimaita ‘’Yerima Barde mai kyawun duniya? Kai ba k’aramin baiwa Allah yayiwa Gimbiya K'amariyya ba’’
Cikin k’aguwa Gimbiya Binta ta ce "Didi ina ku ka had’u? Takawa(sarki) ya sani? Da gaske kyawunshi ya wuce na kowa a duniya?’’
‘’Wanga tambayoyi haka kauna(kanwa) ta? Kimin d’aya bayan d’aya’’
Kana Gimbiya Binta ta ce ‘’Toh, ina kuka had’u?’’
‘’A k’asa mai tsarki mu ka had’u, kin san mun je ki na makaranta’’
‘’Ya san ke wacece kuwa?’’
Gimbiya K’amariyya na mai d’aga mata hannu ta ce ‘’Tsaya dai ki ji komai, bayan had’uwar mu, jinin mu ya had’u, hallo mu ka kulla soyayya mai k’arfi, kullum cikin waya mu ke ta sabuwar wayar tafi da gidanka da ya shigo k’asar ga, mun yi alk’awarin amre(aure) da kuma kawo k’arshen gaba da ke tsakanin masarautar nan ta mu guda biyu, hallo hakan ne ma ya sa Allah ya had’a mu’’
Gaba d’aya Bintu ta manta da aikin da aka saka ta, ta saki baki da hanci ta na jin lamarin ubangiji, ‘’Ashe dai da rabon za ta ga Yerima Barde a rayuwarta’’ Farin cikin da ya mamaye ranta kenan. Kamar daga sama ta ji an daka mata tsawa
‘’Yallah can (dalla can) makira fita ki ba mu wuri! Ki ga yanda ta saki baki da hanci ta na jin mutane, wato ki sami wanda za ki d’auka ki watsa rariya(waje) ko?’’
A firgice Bintu ta dawo cikin hayyacin ta ta na mai raba idanu kamar 6era cikin tarko yayin da ta zube k’asa.
Gimbiya Binta bata gushe ba ta k’ara da ‘’Idan na ji wanga magana ta hita rariya(idan na ji wannan maganar ta fita waje) sai dai uwar ki ta haifi wata! Aradu ma kuwa!’’
‘’Lalle ma kuwa, yo to ai na manta tana nanniya’’ Cewar K’amariyya ta na duban Bintu. Jikin Bintu na rawa ta ce ‘’Tuba na ke! Aradun Allah na tuba, in na kara kada rabbi ya gafirce ni!’’
‘’Hita yallah(fita dallah) jaka kawai!’’ Gimbiya Binta ta daka mata tsawa. Tuni Bintu ta tashi jiki na rawa ta fita.
Bayan fitarta Gimbiya Binta ta ce "Wai har wanga d’iyar bayin ni za ta yiwa alherin maye ramuwa da mugunta? Har ta isa had’a samrayi(saurayi) da ni?’’
Baki bud’e Gimbiya K'amariyya ta ce ‘’Kwarainiya mota a randa! Shi ko wanene wanga samrayi?’’
Gimbya Binta na mai murmushi ta ce ‘’Aisar Gaddafi Nur."
Cike da mamaki Gimbiya K'amariyya ta ce ‘’Kai haba dan Allah, Aisar dan shugaban k'asa gide?"
Gimbiya Binta ta gyad'a mata kai.
"Yo to in ban da abun ki ina tusa zata hure wuta? Ina d’iyar bayi ina dan mulki? Ai komai tsiyar 6arawo ya bar wuta a murhu’’ Cewar Gimbiya K'amariyya.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣3⃣
Kai Gimbiya Binta ta girgiza, tana mai fad’in ‘’Ba ki san makircin wanga d’iya ba ne Didi, bari dai na baki labarin kad’an daga cikin halin ta.’’ Nan fa ta saka Bintu a faifai, k’arya da gaskiya haka ta had’a ta shedawa Gimbiya K’amariyya, ba don komai ba ko don ta samu mai taya ta saka baki a hana Bintu komawa makaranta.
Jiki na kyarma Bintu ta fito, Allah ya sa shigowar Inna kenan su ka had’u a rariya. Inna na ganin Bintu ta san akwai abin da ke damunta, tambayar duniyar nan Inna ta yi mata, amma ta k’i fad’a mata, sai k’arya ba ta jin dad’i ta yi mata. Ta na mai mata Allah ya sauwake ta ja ta gefe ta bata fatan dusan da ta taho mata da shi dan karin kumallo kafin ta yi na ta wajan, tabar Bintu ta na zabga loma.
*** *** ***
Da yammaci, sati guda kenan da dawowa su Bintu.
Bintu kwance tare da Inna da Habibu zaune bisa tabarma a tsakar gida su na shan iska dan kuwa zafi ake na gaske ma kuwa. Inna da ya Habibu ke hirar halin da ake ciki na fari a yanki, su na muhawarar yanda za a sami mafita, in da Bintu ta yi kwance can gefe, gaba d’aya tunanin Aisar ne ya addabi rayuwar ta, dan ko yanzu ma tunanin na shi ta ke yayinda ta ke murza zobensa da ke sanye cikin yatsunta.
Baba ne ya shigo kamar an jefoshi, fad’i ya ke ‘’An dai wad’i(fad’i) ba nauyi!'’ Tashi su ka yi tsaye a tare, Inna na mai tambayar ‘’Malam lafiya kuwa?’’
Baba ya ce ‘’Yo to tunda aka fara fari ina mu ka ga lafiya? Yau fa kur’ia aka doka a fada, kuma sakamakon shi ne za mu nemi sulhu da kuma taimako daga wajan mak’iya abokan gaba, eh masarautar Fabarusa!’’
Babu wanda bai girgiza ba jin kalamin na Baba. Habibu ne ya ce "Gide a rasa in da za a k’ask’antar da kai sai wajan abokan gaba?’’ Baba na mai d’aga kafad’a ya ce "Ta dai faru ta k’are an yiwa mai damo d’aya sata, don kuwa magatakarda ya tura wasik’a zuwa Fabarusa, idan an amsa gobe da sassahe za a d’auki hanya tare da Uban Gabasawa(Sarki) da kansa zuwa wajan abokan gaba nema sulhu’’
Ya na gama fad’in haka ya shige ciki Inna na mai bin bayansa. Shi kuwa Habibu silifa d’insa ya ja ya saka sannan ya fice, wato ya fita yad’a zancen kenan. Bintu kuwa komawa ta yi zaune abin ta, duk da dai itama ta yi tunanin neman taimako daga Fabarusa, jin za a je d’in da gaske sai ta tsinci kanta tana mai fad’uwar gaba.
********
Washegari da sassafe Mai Martaba da tawagarsa su ka d’auki hanyar Faburusa. Babban gida sam babu armashi kowa cikin fargaba ya ke. Gimbiya K’amariyya tafi kowa shiga tashin hankali, gashi tun jiya ta ke kiran wayar Yerima Barde amma wayar ba ta shiga. Gani ta ke kamar alakarsu ce ta zo k’arshe. Ita kuwa Gimbiya Binta damuwarta daban ne, tun dawowar su ta ke ta sak’e-sak’e akan abinda za ta ce da Takawa(sarki) ya canza mata baiwa, dan ita aradu ba za ta koma makaranta da Bintu ba.
Ranar Allah ya taimaki Bintu ta yi aiki da hidimarta cikin Babban gida ba tare da ta sami matsala daga wajan Gimbiya Binta ba. Da yammacin ranar ta raka Yerima Nadir Lambu, nan su ka ta tad’in su kamar ta sami babban mutum. Labarin makarantar su ya ce ta bashi, nan fa Bintu tai ta bashi, har da labarin Aisar. Bata san ta na kewan sa sosai ba sai da take maganar sa a zahiri ba a zuci ba, wata k’ila ma ya manta da wata Bintu, abun da take fad’awa kan ta kenan. Shi kuwa Yerima Nadir kallon ta kawai ya ke ba tare da ya fahimci in da ta dosa ba, ballantana ya gane halin da ta ke ciki.
******
Bayan magrib ta koma gida, shiru har lokacin sarki be dawo ba. Bayan sun ci abinci suna kwance a falo ita da Inna, sun ci sa’a akwai wutar lantakarki, fanka ke kad’awa ta na mai fitar da k’ara alamar ta fara gazawa.Akwatin radiyon Inna su ke sauraro in da ake labaran duniya.
Jin mai karanto labarai ya ce ‘’Jikin shugaban k’asa Gaddafi Nur ya tashi, za'a fitar da shi zuwa k’asar waje domin ba shi taimako’’ Ya sa Bintu tashi zaune da sauri ta na mai tambayar ‘’Inna daman shugaban K’asa be da lafiya?’’
‘’Eh Allah sarki ai be da lafiya, yo to da k’alau ya ke ai da tuni ya magance wanga fari da mu ke ciki, dan ba kya sauraran labarai ne shi ya sa ba ki ji ba’’ Inna ta amsa mata.
Bintu na mai dafe kai ta ce "innalillahi wa innailaihirrajiun, Allah sarki Monsieur Aisar, suna cikin tashin hankali’’
Inna ta dubeta, ‘’Waye shi kuma Bintu?’’
Nan Bintu ta kwashe labarin Aisar ta fad’awa Innar ta. Fuskarta na nuna rashin jin dad’in labarin, Inna ta had’e fuska. ‘’Ai da walakin goro a miya, shi ya sa mana na ga kin dawo wata wuri wuri da ke, d’an shugaban k’asa Bintu?’’
Bintu na mai tura baki ta ce ‘’Yo to Inna minene ciki? Ba fa wani abu ba ne taimako gareshi kawai........’’
‘’Wani taimako? Chiim zanne la nya bangin! (rufa min baki ko na buge ki)’’ Inna ta katse ta, ta k’ara da ‘’Taimako ne har da siya miki turare ma su tsada haka Bintu? Binta sudan? Kafin kafin? Danduala? Turaren da sai Saraki kad’ai ke sawa? Kuma ki na dai ganin yanda Gimbiya ta yi mi ki saboda shi? ngoy awo gulgin d3! (ai ga abinda nake fada), yanzu ba za ta bari ko koma maranta (makaranta) da ke ba!"
Komawa Bintu ta yi ta kwanta, ta na mai lumshe idanu. Kana ta ce ‘’Allah ya ba shi lafiya’’
"Wa fa?’’ Inna ta tambaya. Bintu na mai bud’e idanunta ta ce ‘’Mahaifin Monsieur’’
Tsaki Inna ta ja, kafin ta amsa da ‘’Yo to amin, amma kanki ya kamata ki yiwa addu’a fero (yarinya) a halin da ki ke ciki, ki ma cire wannan mutumin daga ranki, can ga su gada zomo ya ji kid’an farau ta’’
‘’Inna Allah na sa a raina." Cewar Bintu. Kamar daga sama su ka jiyo Habibu daga tsakar gida ya ce
"Kin gama komai kauna(kanwa) ta?''
Ashe duk maganar da su ke ya na can zaune tsakar gida ya na jiyo su ba su sani ba. Murmushi Bintu ta saka, ita kuwa Inna cewa ta yi ‘’Ala sakaa (Allah ya kare)"
Washegari da asubar fari Bintu na tashi daga barci Baba ne ya fad’o ranta, don kuwa har su ka yi bacci be dawo ba. A tsakar gida ta tadda Inna ta na alwala, ka na ta ce ‘’Inna barka da asuba’’
‘’Barka dai Bintu, kin tashi k’alau?’’ Inna ta amsa mata.