Sashe 14
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A tsakar gida su ka tadda Inna ta na tankad’en hatsi, kasancewar ta bababbariya baka ce wulik, doguwa ta na da dogon hanci, fuskar ta d'auke da zane da fashin goshi irin na al’adar barebari. Duk da Bintu ba ta kama da ita, akan ce tsayi da garin jikin Bintu na Inna ne, haka ma gashin kan ta wanda idan ta ware ya na saukar mata har gadon baya.
Da gudun ta Bintu ta je ta rungume ta, Habibu na mai fad’in ‘’Gide ga autar ta ki na kawo mi ki Inna’’
Cike da farin ciki ita ma ta rungume d'iyar ta ta, fad’i ta ke "Usoo am morantiye, wushe k3shero, is3maa?? Nda zawol?"(sannu yan boko, sannu da zuwa, an dawo? Ya hanya?)
‘’Lahiya limi Alhamdulillah, mun same ku k’alau?’’ Cewar Bintu. Inna na mai duban ta cikin nazari ta amsa da ‘’lahiya limi, Gide ya na gan ki da idanu haka jajur?’’
Bintu na fara'a dan gudun kar Inna ta gane halin da ta ke ciki, ta ce idanun ta ke ciwo. Ita ma sai a sannan ta lura da yanda Inna ta rema ta lalace, d’aga idan da za ta yi ta kalli Habibu sai ta ga ashe gwara Inna ma akan shi. Cike da alamar tambaya ta dawo da kallan ta ga Inna, kana ta ce "lafiya kuwa Inna? Ya na gan ku a rame haka? Ina Baba?’’
"Ya na fada.’’ Amsar da Inna ta bata kenan a takaice. Kana Bintu ta ce ‘’Yo to lafiya na ganku haka?’’
Inna ce ta amsa mata da "Yanzu dai ba lokacin tambaya ba ne, Habibu maza k’arasa mata da kayan d’aka, sai ke kuma ki watsa ruwa ki ci abinci ma yi maganar ko?’’
Cike da fargaba Bintu ta gyad’a mata kai kafin ta shige d’akin ta wanda ya ke d’aya daga cikin na falon, Habibu biye da ita.
Shigar su ta bi d’akin na ta da kallo, d'an karamin d’aki ne mai d’auke da gado na k’arfe mai (spring)na daidai kwanciyar mutum d’aya, sai kuma wani k’atan buhu gefe in da Bintu ke aje kayan sawa. Ko tabarma babu a d'akin, sai siminti da ya bi ya faffashe rugu rugu. Gefe guda Habibu ya aje akwatin sannan ya fice ya bar Bintu ta na mai zubewa bisa gadan ta a gajiye. Lalle kuwa kowa fa ya bar gida gida ya bar shi. Daga waje ta jiyo Inna na fad’in ‘’Ki hito ki watsa ruwa fa ‘yar nan’’
Bintu ta amsa ‘’Gani nan hitowa(fitowa) Inna’’
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣2⃣
Ganinsu gabanta nan da nan ta zube k’asa ta na mai fad’in "Rangwame salamun, masu duniya ku na shagalinku, babban bijimi babban Yerima, hadari malafar duniya, barka da siddi!’’
Yerima Nuhu wanda ya ke kyakkyawan saurayi, musammam idan ya sha rawani da shiga irin ta saraki, ya tsinci kan shi ya na mai murmusawa, yayin da abokansa su ka amsawa Bintu da ‘’An gaishe ki yarinya’’ Shi kuwa kallonta ya ke cike da shauki, ya ce ‘’Mu na lahiya Bintu arziki?’’ Dama da sunan da ya ke kiranta kenan.
Cike da nuna ladabi ta ce ‘’Lahiya lumi ran Yerima Nuhu ya d’ade." Kai ya gyad’a kafin ya zunguri dokin shi yayi gaba, haka sauran abokan na sa su ka rufa masa baya. Sai da ta tabbatar sun yi nisa sannan ta tashi ta na mai ajiyar zuciya, ita dai har ga Allah ba ta san irin kallan da Yerima ya ke mata ba tun yau ba, shiyasa ma duk inda ya ke ta ke gudun shi, ko da yake k’awarta wacce su ke kira Cangwai ta ce ina ma ita yake yi wa haka da sauran bayi ‘yan uwanta sun shiga uku da tak’ama. Da wannan tunanin Cangwai ta fad’o mata, ta na mai tunanin ko me ya hana ta zo tun jiya ta ganta yanda ta saba oho, bayan kiran Gimbiya za ta je ta duba ko lafiya, idan kuma sun had’u a babban gida shikenan.
Cikin wannan tunanin ta k’arasa soran da zai sada ta da cikin gidan sarki, wanda su ke kira babban gida. Ginin k’asa ne wanda aka gina tin tale-tele mai cike da kayan ado na al'ada. Sauro shida ne reras, wanda kowanne d’auke ya ke da shimfid’u da ado, biyu daga cikin su da d'akuna, wasu kuma tsuntsaye ne fal ciki musammam jemagu su ka mamaye saman ginin. Haka Bintu tai ta shiga ta na fita, wani ta tadda dogarai, wasu kuma bayi haka ta na gaishe su har ta fito sarari, sai ga ta farfajiyar gidan sarki. Duk da shi ginin bulo ne, amma komai na gidan tsarin al’ada da kuma tambarin sarauta ke gare shi. Wato tsayawa fasalta irin kyawun gidan sai na cika shafi be k’are, dan kuwa tsari dai na al’ada da sarauta gida ya tsaru.
Inna Salti Bintu ta fara cin karo da kasancewar 6angaran ta ne na farko cikin jerin matan gidan. Ta fito daga 6angaran na ta kenan sanye cikin shiga ta alfarma, abin ku da bafulatanar mace Allah ya bata kyau, gashi sam ba ta tsufa. hannun ta rik'e da na Yerima Nadir, sai baiwar ta wacce ta ke biye da ita. Ganinta nan ma Bintu ta zube domin d’ibar gaisuwa ta na mai fad’in ‘’Barka da safiya uwa ma ba da mama, farar aniya alkhairin duniya, jikinki fari, tufar ki fara, zuciyarki fara wane balbela.....’’
Murmushi ta saki ta na mai mamakin yanda karamar yarinya ta iya zaro magana har haka, ko da yake zama da mad’aukin kanwa shi ke kawo farin kai. Shi kuwa Yerima ganin Bintu tuni ya saki hannun Inna Salti ya na mai fad’in ‘’Inna Salti Bintu ce!’’ Har da tsallansa sai gashi jikin Bintu ya na mai rungumota. Ita ma Bintu dariya ta ke saboda farin cikin ganin Yerima Nadir. Inna Salti kuwa kallansu ta ke, ta na mai mamakin wannan soyayya da ke tsakanin Bintu da autan nata, dan kuwa duk cikin bayi babu wacce ya ke sakarwa fuska, amma idan ka ganshi da Bintu ko ciki d’aya su ka fito sai haka. Cikin fara’a Inna Salti ta ce ‘’Brkan ki dai Bintu, an dawo lahiya?”
‘’Lahiya lumi ranki shi dad’e’’ Cewar Bintu.
‘’Toh ja66ama.’’
Yerima Nadir ya dubi Inna Sallati ya ce ‘’Inna Salti zan yi wasa da Bintu’’
Inna Salti na mai murmushi ta ja hannun Yerima Nadir ’’Tunda ka ga ta yi sammako haka, ko shakka babu aiki ke gare ta, ko Bintu?’’
Jin haka Bintu ta san me Inna Salti ta ke nufi, kana ta ce ‘’Dama Gimbiya Binta ce ta yi kira na."
‘’Ka ji ko Nadir? Didi ta yi kiranta’’ Cewar Inna Salti. Ba dai haka ya so ba, amma be fasa tambayar ko anjima Bintu za ta yi wasa da shi ba, in da ta amsa masa da eh, da haka su ka yi sallama, sai da ta tabbatar sun wuce sannan ta tashi daga sunkuyen da ta yi, kai tsaye 6angaran su Gimbiya ta nufa ta na mai fad’uwar gaba.
K’atan falo ne mai d’auke da ado irin na gidan sarauta, haka kuma ya na d'auke da d’akuna biyu, kowanne da b’and’aki ciki, wanda na fari shi ne na Gimbiya K’amariyya, sai kuma na Gimbiya Binta daga can 6angaran.
Bayi ne guda hud’u ke ta kai kawo. Kai tsaye d’akin Gimbiya Binta ta nufa, ganin babu kowa bakin k’ofar d'akin ya sa Bintu kwankwasawa a hankali. Sai da ta kai wajan minti goma tsaye bakin k’ofa sannan ta ji muryar Gimbiya Binta ta na fad’in ‘’Gide wata maratarbiyar na samu a nan?’
Cikin rawar murya Bintu ta ce ‘’Ran gimbiya ya dad'e Bintu ce....’’ Shiru sai bayan wasu d’an dakik’ai ta sake furta ‘’D’iyar bayi ki ke kowa? Kya iya shigowa’’
A hankali ta murd’a hannun k’ofar, tuni wani ni’imantaccen kamshi ya daki hancin Bintu, sa k’afarta, ta ji ya lume cikin lallausar kafet(carpet), ga wani rab'a mai ratsa jiki da ya kama d'akin. Babu shakka d’akin Gimbiya Binta yana da fasalin d’akin d’iyar turawa. Komai na d’akin fari ne fat.
Lullu6e cikin bargo, idanu lumshe ta ce ‘’sai yanzu ki ga damar zuwa?’’ kofar ta mayar ta rufe sannan ta zube k’asa ta na fad’in ‘’Tuba na ke Gimbiya, barka da asuba.’’
Ba tare da ta bud’e idanunta ba ta yi nuni da d’an yatsa zuwa akwatinan da aka jibge gefe guda, sannan ta ja bargo ta rufe fuskar ta. Ko da ba ta yi magana ba, Bintu ta gane umarnin da aka ba ta. Dan haka tashi ta yi ta na mai bin akwatinan da kallo, su goma sha biyu ne cif. Himma ta d'aura, ta bi akwatinan d’aya bayan d'aya ta na fito da kayan ta na jera su cikin durowar Gimbiya.
Wasa wasa aikin nan sai gashi ya d'auke ta awa d’aya. Ta na kan akwati na k’arshe ne Gimbiya K'amariya ta shigo cikin shiga na alfarma. Kallo d’aya za ka mata ka tabbatar da farin cikin da ke tattare da ita. Gimbiya K'amariyya fara ce kamar Gimbiya Binta, doguwa ce siririya, dan kuwa sam ba ta garin jiki, ba ba'a ba, irin wannan matan ne da ake yiwa lak'ani da "Muciya da zani" Tsabar rashin jiki. Ta na da kyawun fuska daidai gwargwado dan har ta fi Gimbiya Binta.
Da sauri Bintu ta zube ta na mai fad’in ‘’barka da safiya Gimbiya’’
Da fara’ar ta ta masa da ‘’Barka dai, kya iya cigaba da aikinki’’
Bintu ta koma ga aikinta, inda Gimbiya K’amariyya ta zauna gefan gadon Gimbiya Binta. A hankali Gimbiya Binta ta yaye bargon daga fuskarta tana mai murmushi ga yar uwarta, ashe duk lokacin nan idanun ta biyu.
‘’A kwana a hantse sai d’iyar sarakai.’’ Cewar Gimbiya K’amariyya tana mai dafa kafad’ar Gimbiya Binta. Tashi ta yi zaune kana ta ce ‘’Gidai ban fa gane wanga farin ciki na ki ba, hallo ana fama da fari gidai ki na fama da farin ciki? me an surrin?(kin gan ki ban gane wannan farin ciki da ki ke ciki ba, muna fama da fari ke ki na ta farin ciki? Menene sirrin?’)’
Da gudun ta Bintu ta je ta rungume ta, Habibu na mai fad’in ‘’Gide ga autar ta ki na kawo mi ki Inna’’
Cike da farin ciki ita ma ta rungume d'iyar ta ta, fad’i ta ke "Usoo am morantiye, wushe k3shero, is3maa?? Nda zawol?"(sannu yan boko, sannu da zuwa, an dawo? Ya hanya?)
‘’Lahiya limi Alhamdulillah, mun same ku k’alau?’’ Cewar Bintu. Inna na mai duban ta cikin nazari ta amsa da ‘’lahiya limi, Gide ya na gan ki da idanu haka jajur?’’
Bintu na fara'a dan gudun kar Inna ta gane halin da ta ke ciki, ta ce idanun ta ke ciwo. Ita ma sai a sannan ta lura da yanda Inna ta rema ta lalace, d’aga idan da za ta yi ta kalli Habibu sai ta ga ashe gwara Inna ma akan shi. Cike da alamar tambaya ta dawo da kallan ta ga Inna, kana ta ce "lafiya kuwa Inna? Ya na gan ku a rame haka? Ina Baba?’’
"Ya na fada.’’ Amsar da Inna ta bata kenan a takaice. Kana Bintu ta ce ‘’Yo to lafiya na ganku haka?’’
Inna ce ta amsa mata da "Yanzu dai ba lokacin tambaya ba ne, Habibu maza k’arasa mata da kayan d’aka, sai ke kuma ki watsa ruwa ki ci abinci ma yi maganar ko?’’
Cike da fargaba Bintu ta gyad’a mata kai kafin ta shige d’akin ta wanda ya ke d’aya daga cikin na falon, Habibu biye da ita.
Shigar su ta bi d’akin na ta da kallo, d'an karamin d’aki ne mai d’auke da gado na k’arfe mai (spring)na daidai kwanciyar mutum d’aya, sai kuma wani k’atan buhu gefe in da Bintu ke aje kayan sawa. Ko tabarma babu a d'akin, sai siminti da ya bi ya faffashe rugu rugu. Gefe guda Habibu ya aje akwatin sannan ya fice ya bar Bintu ta na mai zubewa bisa gadan ta a gajiye. Lalle kuwa kowa fa ya bar gida gida ya bar shi. Daga waje ta jiyo Inna na fad’in ‘’Ki hito ki watsa ruwa fa ‘yar nan’’
Bintu ta amsa ‘’Gani nan hitowa(fitowa) Inna’’
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣2⃣
Ganinsu gabanta nan da nan ta zube k’asa ta na mai fad’in "Rangwame salamun, masu duniya ku na shagalinku, babban bijimi babban Yerima, hadari malafar duniya, barka da siddi!’’
Yerima Nuhu wanda ya ke kyakkyawan saurayi, musammam idan ya sha rawani da shiga irin ta saraki, ya tsinci kan shi ya na mai murmusawa, yayin da abokansa su ka amsawa Bintu da ‘’An gaishe ki yarinya’’ Shi kuwa kallonta ya ke cike da shauki, ya ce ‘’Mu na lahiya Bintu arziki?’’ Dama da sunan da ya ke kiranta kenan.
Cike da nuna ladabi ta ce ‘’Lahiya lumi ran Yerima Nuhu ya d’ade." Kai ya gyad’a kafin ya zunguri dokin shi yayi gaba, haka sauran abokan na sa su ka rufa masa baya. Sai da ta tabbatar sun yi nisa sannan ta tashi ta na mai ajiyar zuciya, ita dai har ga Allah ba ta san irin kallan da Yerima ya ke mata ba tun yau ba, shiyasa ma duk inda ya ke ta ke gudun shi, ko da yake k’awarta wacce su ke kira Cangwai ta ce ina ma ita yake yi wa haka da sauran bayi ‘yan uwanta sun shiga uku da tak’ama. Da wannan tunanin Cangwai ta fad’o mata, ta na mai tunanin ko me ya hana ta zo tun jiya ta ganta yanda ta saba oho, bayan kiran Gimbiya za ta je ta duba ko lafiya, idan kuma sun had’u a babban gida shikenan.
Cikin wannan tunanin ta k’arasa soran da zai sada ta da cikin gidan sarki, wanda su ke kira babban gida. Ginin k’asa ne wanda aka gina tin tale-tele mai cike da kayan ado na al'ada. Sauro shida ne reras, wanda kowanne d’auke ya ke da shimfid’u da ado, biyu daga cikin su da d'akuna, wasu kuma tsuntsaye ne fal ciki musammam jemagu su ka mamaye saman ginin. Haka Bintu tai ta shiga ta na fita, wani ta tadda dogarai, wasu kuma bayi haka ta na gaishe su har ta fito sarari, sai ga ta farfajiyar gidan sarki. Duk da shi ginin bulo ne, amma komai na gidan tsarin al’ada da kuma tambarin sarauta ke gare shi. Wato tsayawa fasalta irin kyawun gidan sai na cika shafi be k’are, dan kuwa tsari dai na al’ada da sarauta gida ya tsaru.
Inna Salti Bintu ta fara cin karo da kasancewar 6angaran ta ne na farko cikin jerin matan gidan. Ta fito daga 6angaran na ta kenan sanye cikin shiga ta alfarma, abin ku da bafulatanar mace Allah ya bata kyau, gashi sam ba ta tsufa. hannun ta rik'e da na Yerima Nadir, sai baiwar ta wacce ta ke biye da ita. Ganinta nan ma Bintu ta zube domin d’ibar gaisuwa ta na mai fad’in ‘’Barka da safiya uwa ma ba da mama, farar aniya alkhairin duniya, jikinki fari, tufar ki fara, zuciyarki fara wane balbela.....’’
Murmushi ta saki ta na mai mamakin yanda karamar yarinya ta iya zaro magana har haka, ko da yake zama da mad’aukin kanwa shi ke kawo farin kai. Shi kuwa Yerima ganin Bintu tuni ya saki hannun Inna Salti ya na mai fad’in ‘’Inna Salti Bintu ce!’’ Har da tsallansa sai gashi jikin Bintu ya na mai rungumota. Ita ma Bintu dariya ta ke saboda farin cikin ganin Yerima Nadir. Inna Salti kuwa kallansu ta ke, ta na mai mamakin wannan soyayya da ke tsakanin Bintu da autan nata, dan kuwa duk cikin bayi babu wacce ya ke sakarwa fuska, amma idan ka ganshi da Bintu ko ciki d’aya su ka fito sai haka. Cikin fara’a Inna Salti ta ce ‘’Brkan ki dai Bintu, an dawo lahiya?”
‘’Lahiya lumi ranki shi dad’e’’ Cewar Bintu.
‘’Toh ja66ama.’’
Yerima Nadir ya dubi Inna Sallati ya ce ‘’Inna Salti zan yi wasa da Bintu’’
Inna Salti na mai murmushi ta ja hannun Yerima Nadir ’’Tunda ka ga ta yi sammako haka, ko shakka babu aiki ke gare ta, ko Bintu?’’
Jin haka Bintu ta san me Inna Salti ta ke nufi, kana ta ce ‘’Dama Gimbiya Binta ce ta yi kira na."
‘’Ka ji ko Nadir? Didi ta yi kiranta’’ Cewar Inna Salti. Ba dai haka ya so ba, amma be fasa tambayar ko anjima Bintu za ta yi wasa da shi ba, in da ta amsa masa da eh, da haka su ka yi sallama, sai da ta tabbatar sun wuce sannan ta tashi daga sunkuyen da ta yi, kai tsaye 6angaran su Gimbiya ta nufa ta na mai fad’uwar gaba.
K’atan falo ne mai d’auke da ado irin na gidan sarauta, haka kuma ya na d'auke da d’akuna biyu, kowanne da b’and’aki ciki, wanda na fari shi ne na Gimbiya K’amariyya, sai kuma na Gimbiya Binta daga can 6angaran.
Bayi ne guda hud’u ke ta kai kawo. Kai tsaye d’akin Gimbiya Binta ta nufa, ganin babu kowa bakin k’ofar d'akin ya sa Bintu kwankwasawa a hankali. Sai da ta kai wajan minti goma tsaye bakin k’ofa sannan ta ji muryar Gimbiya Binta ta na fad’in ‘’Gide wata maratarbiyar na samu a nan?’
Cikin rawar murya Bintu ta ce ‘’Ran gimbiya ya dad'e Bintu ce....’’ Shiru sai bayan wasu d’an dakik’ai ta sake furta ‘’D’iyar bayi ki ke kowa? Kya iya shigowa’’
A hankali ta murd’a hannun k’ofar, tuni wani ni’imantaccen kamshi ya daki hancin Bintu, sa k’afarta, ta ji ya lume cikin lallausar kafet(carpet), ga wani rab'a mai ratsa jiki da ya kama d'akin. Babu shakka d’akin Gimbiya Binta yana da fasalin d’akin d’iyar turawa. Komai na d’akin fari ne fat.
Lullu6e cikin bargo, idanu lumshe ta ce ‘’sai yanzu ki ga damar zuwa?’’ kofar ta mayar ta rufe sannan ta zube k’asa ta na fad’in ‘’Tuba na ke Gimbiya, barka da asuba.’’
Ba tare da ta bud’e idanunta ba ta yi nuni da d’an yatsa zuwa akwatinan da aka jibge gefe guda, sannan ta ja bargo ta rufe fuskar ta. Ko da ba ta yi magana ba, Bintu ta gane umarnin da aka ba ta. Dan haka tashi ta yi ta na mai bin akwatinan da kallo, su goma sha biyu ne cif. Himma ta d'aura, ta bi akwatinan d’aya bayan d'aya ta na fito da kayan ta na jera su cikin durowar Gimbiya.
Wasa wasa aikin nan sai gashi ya d'auke ta awa d’aya. Ta na kan akwati na k’arshe ne Gimbiya K'amariya ta shigo cikin shiga na alfarma. Kallo d’aya za ka mata ka tabbatar da farin cikin da ke tattare da ita. Gimbiya K'amariyya fara ce kamar Gimbiya Binta, doguwa ce siririya, dan kuwa sam ba ta garin jiki, ba ba'a ba, irin wannan matan ne da ake yiwa lak'ani da "Muciya da zani" Tsabar rashin jiki. Ta na da kyawun fuska daidai gwargwado dan har ta fi Gimbiya Binta.
Da sauri Bintu ta zube ta na mai fad’in ‘’barka da safiya Gimbiya’’
Da fara’ar ta ta masa da ‘’Barka dai, kya iya cigaba da aikinki’’
Bintu ta koma ga aikinta, inda Gimbiya K’amariyya ta zauna gefan gadon Gimbiya Binta. A hankali Gimbiya Binta ta yaye bargon daga fuskarta tana mai murmushi ga yar uwarta, ashe duk lokacin nan idanun ta biyu.
‘’A kwana a hantse sai d’iyar sarakai.’’ Cewar Gimbiya K’amariyya tana mai dafa kafad’ar Gimbiya Binta. Tashi ta yi zaune kana ta ce ‘’Gidai ban fa gane wanga farin ciki na ki ba, hallo ana fama da fari gidai ki na fama da farin ciki? me an surrin?(kin gan ki ban gane wannan farin ciki da ki ke ciki ba, muna fama da fari ke ki na ta farin ciki? Menene sirrin?’)’