← Book details Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 28

Sashe 17

Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da shigarsa ya tadda Mai martaba hakimce, k’ishingid’e bisa wata k'atuwar dadduma da aka yi da fatar rak’umi, yayiwa hannun sa na hagu majingini bisa wani k’aton tintin mai zanen tambarin masarautar fabarusa, hannunsa na dama rik’e da k’aton jarbi ya na ja.

Kyakkyawan tsoho ne mai kimanin shekara tamanin a duniya, shi kanshi Barde be k’ara ganin tsufar mahaifin na sa ba sai yanzu da ya gansa sanye cikin farar jallabiya, furfura fal bisa kansa, amma ace ya nemi auren yarinya yar shekara ishirin, wanda ya yi jika da ita, kai har tattaba kunne ma! Gaskiya dai maganar nan da kuskure.

Zancen zucin da Barde ke yi kenan yayin da ya zube gaban Mahaifin na sa ya na mai mik’a gaisuwar sa. Amsawa Sarki yayi, tare da fad’in "Barde da wani abu ne?’’
"Barde ya dukar da kai kasa, kana ya ce
‘’Allah ya ja zamanin ka, shin za a taimakawa masarautar S’ayrasa ne?’’

Sarki na mai murmushi ya bashi amsa da
‘’Tabbas za mu taimaka musu, amma fa sai sun ba mu dama’’

Barde bai gushe ba ya k’ara tambayar Sarki
‘’Allah ya taimake ka, tunda su ka zo gare mu, ai sun bada damar kenan, Allah ya taimaki Sabkawa.’’

‘’Ba su ba mu dama ba, kila dai za su bayar, amsar ta su mu ke jira’’
Sarki ya amsa a tak’aice. Jin haka Barde ya rusunar da kai, kana ya ce "Allah ya d’aukake ka ranka shi dad'e shin wata dama ce wannan?’’

Sai da wasu d’an dak’ikai su ka wuce, kafin Sarki ya bud’i baki ya ce
‘’Ba wata dama ba ce, illa kulla aminci ta hanyar kawar da gaba har abada. Mu na son tabbatar da amincin Sa’ayrasa, kafin mu fidda tsagwaran dukiya wajan taimaka musu, don haka mu ka yanke hukuncin auratayya tsakanin masarautarmu da ta su’’

Gaban Barde ne ya fad’i, cikin ransa ya na mai nanata "Dagaske ne kenan, innalillahi wa innailaihi rajiun!’’ Sarki na mai dubanshi, ganin yanayin da ya shiga ya ce
‘’Mu na sauraran Barde, akwai abun da ya kamata mu sani ne?’’

Nan da nan Barde ya nutsu, ya na mai 6oye halin da ya ke ciki ta hanyar yin nauyin baki ya ce
"Babu Allah ya ja da ran Mai martaba, Allah ya tabbatar mana da alkairinsa’’

Cikin nuna jin dad’i Sarki ya ce
‘’D'an mu ya gama magana, mun san a koda yaushe kai mai amincewa da hukuncin mu ne ba tare da ka tsananta bincike ba, shi ya sa ba mu da haufi akanka. Wannan lamari alkhairi ne ga masarautar mu’’

Jikin Barde kamar wanda aka d’aure, zuciya sark’ak’e ya yiwa sarki sallama. Kai tsaye na shi sashen ya nufa, in da ya ji zazza6i na neman rufe shi tsabagen 6acin rai.

******* ********
Sa’ayrasa kuwa, Gimbiya Binta na fita turakar Sarki ta nufa, in da take da tabbacin za ta sami Jakadiya. Ta ko yi sa’a ta same ta ta gama shirya Sarki kenan, ya fita ran gadi. Zaune ta ke farfajiyar turakar sarki, ta na cin goro. Ganin Gimbiya Binta gabanta, ta shiga mata kirarin da ta saba mata

‘’Ture a ga tsiya, a kalla ruwan ido ya tsiyaye, tanka ka lalace, shiga d’aki bakin ciki ya kashe ka, ta Amale(Sarki) kin fi darbejiya d'aci, mai san zama da ke ya tambayi hali.’’

Gimbiya Binta na mai murmushi ta d'agawa bayin da su ka taka mata baya hannu, ma’ana su ba ta waje, nan da nan su ka koma da baya, yayin da Jakadiya ta mata tayin ko za su shiga daga ciki ne? Gimbiya ta ce rariyar ma ba laifi. Sabuwar shifid'a Jakadiya ta mata, In da Gimbiya ta ke tambayar shin ya lafiyar Takawa?

Jakadiya na mai girgiza kai ta ce "Bijimin Duniya ana wani hali, damuwarshi ta kai matuk’a, abinci ma ba sosai ya ke iya ci ba, fari da batun tsohon banza na Fabarusa shi ya sako shi gaba Gimbiya’’

Gimbiya Binta na mai duban Jakadiya ta ce ‘’Jakadiya, halin da mai martaba ya ke ciki zai iya illata shi da ma iyalan sa baki d’aya, kuma watsi da lamarin Fabarusa barazanar rasa rayukan talakawa ne, domin za su ga Takawa ya fi san iyalan sa akan talakawan sa, wanda hakan ka iya kawo rabuwar kai a wannan masarauta ta mu, kuma ko shakka babu k’udirin abokan gaba Masarautar Fabarusa kenan’’

Jakadiya na mai jinjina kai ta ce
"Sadak’ata Gimbiya, wannan batu na ki na yarda da shi’’

Gimbiya Binta ba ta gushe ba, ta nisa sannan ta k’ara da
‘’Masarautarnan kaf, babu wanda ya kai Jakadiya kusanci da sarki, yanda ya yarda da ke babu na biyunki, ke ki kasan Takawa, ke ki kasan cikin Takawa, shi ya sa ake kama k’afa da ke kan lamarin Takawa, gani na zo da shawara da kuma neman taimako daga gare ki, ban sani ba ko Jakadiya za ta amince da ni’’

Jin haka Jakadiya ta jefa kan ta baya, ta saki wani irin dariya mai k’ara kafin ta fara yiwa kan ta kirari kamar haka

‘’Sai ni Hindu Maryamu, jikar Baba Kilishi, jikar Nana, ban fito ba sai da na shirya ko a lahira rago ake duka dan bantan uba, lokacin iska akan ci 'ya'yan tsuntsu, kuci bayan gaban da k’aya’’

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪[5/5, 1:06 AM] ‪+234 703 962 5239‬: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

©Khadija Sidi.....✍🏼

1⃣5⃣

Ko da Jakadiya ta kai ga aya a kirarin ta, ta na mai duban Gimbiya Binta ta ce fad’i in ji, in dai cigaban Babban biji ne sha yanzu magani yanzu. Jin haka Gimbiya Binta ta waiga kudu da arewa, gabas da yamma sannan ta dubi Jakadiya ta ce
‘’bangon gidan ga kunnuwa gare shi Jakadiya’’

Jin haka Jakadiya ta matsawo kusa da Gimbiya Binta, ta amsa da ‘’oh toh toh, bari na matso kusa kar iska ta kwasa ta kai d’akin o o da o o yan bantan uba’’ kunnan ta tafitar daga lullub’in ta, nan Gimbiya Binta ta shiga zayyana mata buk’atun ta, ko da Gimbiya ta gama, Jadiya ta ja da baya ta na mai fad’in

‘’Timirin katauje ba sai da kwandala ba, da kwandalar ne da yafi dama dama, haihuwa babu ciwo sai ka ce fitsari? Gwara ma fitsarin kayi yau da gobe, haihuwar da babu ciwo sai kace ruwan famfo? Gwara ma ruwan famfo ka yi murd’e murd’e’’

Gimbiya da ta gano in da Jakadiya ta dosa, ta na mai kallan gefe da gefe, kusurwa kusurwa gudun kar a jiyo Jakadiya, ta ce ‘’ kar ki ji komai Jakadiya, ina mai tabbatar mi ki idan har ki ka fad’awa Takawa wannan shawara sai ya mi ki babban kyauta, dadin dad’awa kuma ni ma mai mi ki kyautan zannuwa shirin ce, kuma hajjin bana har da ke, aradu ma kuwa’’

Jin haka Jadiya ta ce ‘’yo to menene, dan dai d’an wannan lamarin da be taka kara ya karya ba? An gama ran ki shi dad’e, yau d’in nan ma kuwa’’
Gimbiya na mai jin dad’i, babu shakka tarkon ta ya kama tsuntsuwa ta yiwa Jakadiya sallama, ta bar Jakadiya ta na Allah Allah ta ga dawowar sarki, dan kuwa dai bana kakar ta ta yanke sak’a in dai batun Gimbiya Binta mai yiyuwa ne, ga zannuwa da zuwa hajja, wannan shekara dai ta zo mata da kyau.

******
Bayan an idar da sallar Ishai, kamar kullum Bintu tare da su Innar ta zaune tsakar gida bisa tabarma su na shan iska. Tun da su ka zauna Bintu ta tsurawa zoben hannun ta ido, gaba d’aya ta rasa kwanciyar hankali.

Inna ce ta ta6o ta tana fad’in ‘’ba da ke ake magana ba Bintu?’’ Bintu ta yi firgita ta dawo cikin hayyacin ta "eyee? Na’am?’’ cewar Bintu ta na mai duban Inna da Habibu da su ka kafe ta da ido suna kallan ikon Allah. Inna na buga hannu a iska ta ce ‘’yo to ba na fad’a ma ba, ba ta san ka na yi ba Habibu’’

Habibu na duban Bintu da ta sunkuyar da kai, har lokacin hannun ta be bar kan zuben ba, ya ce ‘’Inna kin sa halin ta, akwai damuwa da damuwar wasu, yanzu haka babu mamaki lamarin Babban gida ke damun ta, ko ta ce rashin lafiyar shugaban k’asa.

‘’mtsw wahalar da rai fushi da makwafci’’ cewar Inna ta na mai nuna Bintu da yatsa ‘’ki je ki d'aurawa kan ki ciwo akan wanda ba su san da ke ba bare su san ki na yi’’

Bintu ta dai ba ta ce komai ba, ita kad'ai ta san irin fad’uwar gaban da ta ke fama da shi. Ita dai adduar ta Allah ya sa alkahiri ne yanayin da ta ke ji.

***** ****
Babban gida kuwa, Jakadiya ba ta yi k’asa a gwiwa ba, bayan ta gama shirya sarki cikin shirin bacci, Sarki na daga shingid’e, kafin ta raka shi wajan matar da ta za6a ma sarki kwana gurin ta ne ta ke bawa Sarki shawara akan lamarin da Gimbiya Binta ta sheda mata, ta k’are maganar na ta da
‘’watsi da al’amarin Sarki Abdulrahman barazanar rasa rayukan talakawa ne, sake dabara a nemi taimako wata masarautar talakawa za su ga kamar an fi san iyalan sarki akan lamarin rayuwar su, hakan ka iya kawo rabuwar kai cikin wanga masarauta wanda dama k'udirin Masarautar kenan. Tun da Sarki Abdulrahman be ji kunyar yada girman sa ba, da saka rayuwar mu cikin kunci, mu kuwa ba za mu kasa masa bita da kulle ba, dukan kabarin kishiya’’ shiru ta yi dan shan nufashi kafin ta k’ara da
‘’wannan dalili ya sa na yi bincike ta hannnun Gimbiya Binta, ta kuma amince da wannan batu, Allah ya ja da ran sa, idan na yi kuskure a yi min rai, ina tuba’’
Chapter 17 · 0% Book details