← Book details Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 28

Sashe 27

Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zoben Aisar kuwa d’aya daga cikin bayi ne, wanda saurayi ne, mai kula da lambu ya tsinta yayinda ya ke shara. Ganin zobe mai matuk’ar tsada yayi saurin 6oyewa cikin aljihunshi, don jira ya ji ko mai shi zai nema, idan kuma ba a yi cigiya ba ya kai kasuwa ya siyar ya sami kud’i.

********
Kwanaki uku ya rage auren Bintu. Da hantsi Inna Salti ta kawo ziyararta ga Bintu. Daga ita sai Bintu da ke d'urkushe gabanta ne a d'akin. A sannu cikin lallami Inna Salti ke mata magana, in da ta ce
‘’Bintu ki sani wannan lamari jarabawa ce daga Allah, saboda haka ki kasance mai biyayya sai ki ga kin ci jarabawar. Wagga amre za a yi shi ne cikin surri, duk wanda ki ga ya san wani abu na game da gaskiyar wagga amre to amintaccen fada ne, hallo sai sun rantse ake ba su amanar ga, dan haka kema wagga al'amari ya kasance amana a naki 6angaren, idan ki ka kuskura gaskiyar al’amari ya hito, rayuwarki za ta kasance cikin hatsari Bintu, wanda ba na fata. Daga sanda aka amra miki amre za ki tashi daga Bintu, za ki fara amsa Gimbiya Binta.’’

Numfashi ta ja, sa’annan ta cigaba
‘’Kin dai ga yanda sarauta ta ke, a fada aka haife ki ciki ki tashi har rana ita yau da ake shirin amrar da ke. Hallo sai kin yi takatsantsan da rayuwar da za ki shiga, zaki shiga rayuwar amre hallo a fada, akwai wuyar ganewa. A fada ba kowa ne zai 6ud’i hak’ora ya miki dariya ya kasance masoyi gareki ba, wani sa'in ma mak’iyinki ka iya nunawa kin fi kowa soyuwa a gareshi, haka zalika ba kowani mai 6ata miki ba ne mak’iyi a gareki, ta iya yiyuwa kauna ke kawo 6acin ran, don haka ki nutsu ki gane.’’

Bintu na mai share hawaye sai gyad'a kai kawai ta ke. Inna Salti na mai nisawa ta k’ara da
‘’Ki ji ki k’i ji, ki gani ki k’i gani, ki iya harshenki, hatta bangon fada kunne gareshi, ki kyautata dangantakarki da kowa, ki sa Allah a ranki, ki yawaita addu'a da zikiri, ki kasance mai yawan zama da alwala, shin kin iya azkar?’’

Bintu ta girgiza kai alamar ah ah,
Inna Salti na mai gyad’a kai ta ce
‘’Zan yi k’ok’arin sawa a koya miki kan a kai ki ga Fabarusa, ki na yi safe da yamma, ni ma da kika ganni anan addu'a ce da tawassali ga Allah kad’ai ke zaunar da ni a wagga Masarauta bare kuma Masarauta mai girman gaske kamar Fabarusa.’’

Jakadiya ce ta shigo, yayinda ta zube gaban Inna Salti cike da girmamawa duk da dai ba yin Inna Salti ta ke ba, ba ta yi mata kyauta da cin hanci kamar sauran matan Sarki.
‘’Barka da hantsi ranki shi dad’e.’’

‘’Barka dai Jakadiya, na sameki lahiya?’’
‘’Lahiya lumi ranki shi dad’e.’’
Kana Inna Salti ta maida dubanta ga Bintu ta ce
‘’Inaso na san adadin bayin da za su bi Bintu Masarautar Fabarusa.’’

Jakadiya na mai gyara zama ta ce
‘’Akwai Ladiyo da Kyallu, wanda Gimbiya Binta ce ta za6esu da kan ta....’’
Jin haka sai da Bintu ta d’ago ta dubi Jakadiya cike da fad’uwar gaba, don kuwa ta san hakannan siddin Gimbiya Binta ba za ta ta6a za6a mata kowani abu ba, muddin ba sharri ba ne. Ita kuwa Jakadiya da ba ta san ma ta na yi ba, ba ta gushe cikin jawabinta ba
‘’Sai kuma Uwanini, amintacciyar baiwar Yarima Nuhu wanda shi da kansa ya buk’aci hakan.....’’

Ihu ne kawai Bintu bata kurma ba jin wannan masifar da ake shirin had’a mata, maganar Inna Salti ne ya d’an kwantar mata da hankali, jin ta ce
‘’Ita fa Bintu? Shin an tambayeta ko ta na da baiwar da ta ke son tafiya da ita?’’
Jin haka Jakadiya ta kai kallanta ga Bintu, ta ce
‘’Bintu shin ko kina da wannan buk'atar gide? Wa ki ka za6a”
Bud’ar Bakin Bintu sai cewa ta yi
‘’Innata, dan Allah a tafi da Innata’’

Jakadiya na mai girgiza kai ta ce
‘’Innar ki gobe goben nan za su yi bulaguro zuwa marad’i bisa ga umarnin Babban Bijimi, har sai an sami lafawar al’amura za su dawo, sai dai fa ki za6i wata baiwar.’’
Nan da nan Bintu ta fashe da kuka jin Innarta za su bar gari, Inna Salti ta fara k’ok’arin rarrashinta Jakadiya ta ce
‘’Ai da kin kyaleta ranki shi dad’e, abun ga ne ya zo ga ma su shi, kukan amre da sallallami '’
Inna Salti ba ta fasa rarrashin Bintu ba, har ta samu ta d’an yi shiru kafin ta k’ara bata za6i, inda ta za6i aminiyar Inna kuma mahaifiyar k'awarta Cangwai, wacce aka fi sani da Maman Cangwai.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
[5/15, 7:44 PM] ‪+234 703 962 5239‬: ®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

GARGA'DI

KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.

Na gaishe ki aminyar arziki Ummi Aysha, ina alfahari da ke. Allah ya bar zuminci🤝

©Khadija Sidi.....✍🏼

2⃣6⃣

Da yammaci Inna ta zo mata sallama d’auke da su langar tuwo da miya, da humra da turaren wuta. Tun zuwanta Bintu ta ke kuka, har yanzu da Inna ta ke mata jawabi kamar haka
‘’Bintu kar ki damu, wani hani ga Allah baiwa Bintu. Ki yi addu'a Allah Ya sa hakan da ya zo mana shi an alkahiri, ina so ki sani Allah ne ya za6a miki wagga rayuwa da za ki shiga, ki sa Allah a ranki shi kad’ai zai miki gata.’’
Bintu ta gyad’a kai alamar toh.

‘’Duk da amren ga ba a san ranmu za a yi ba, ki na jinin barebari ba zan bari ki tafi haka ba, wagga(ta nuna kwalaban turarukan da ke aje gaban Bintu da yatsa) tun kina shekara biyar a duniya na had’a mi ki su na binne da niyyar sai amrenki ya tashi na hak’o, wannan kuma langar tuwo da miya da cokali da ludiya wanda na fara miki taro ne, duk da dai na san ba lalle ba ne a bari ki tahi da su ba, gashinan dai na baki a matsayin uwa, na hita hakkinki.’’

Bintu na kuka ta ce
‘’Wallahi ba na so! Ba na so Inna! Inna makaranta na ka so, dan Allah Inna ki taimaka kin ga dai sati uku ya rage mu koma....’’

Rungumeta Inna ta yi cike da tausayawa, Allah kad’ai yasan iya adadin lokacin da su ka d’auka a haka, kafin Bintu ta zame jikinta daga na Inna, kayanta ta nufa ta na mai bincikawa, nan ta fito da turarikan da Aisar ya bata, ta dawo ta durkusa gaban Inna, ta na mai mik’a mata ta ce
‘’Inna ga wagga, dan Allah ki kar6a ko da kuwa ba za ki yi amfani da su ba, wannan kyauta ne tsakanin uwa da d’iyarta, dan Allah Innata, wagga shi ne kad’ai abunda na mallaka nawa na kaina’’
Hannun Inna na rawa ta kar6a ta na mai fad’in
‘’Allah Ya sadamu da alkhairinsa d'iyar arziki, Allah ya sada mu ko da a darussalamu ne, saduwa ta alkahairi......’’
Kuka ne ya su6ucewa Inna, nan su ka yi mai isarsu, har dai Inna ta ga abin ba na k’arau ba ne, dakyar ta janye jikinta ta fice ta na jiwo kukan Bintu.

Yarima Nuhu kuwa har da jinya don kuwa babu yanda baiyi ba na ganin an fasa aurennan amma abu sai dad'a kankama ya ke, haka kuma ya so k’ara ganin Bintu amma Jakadiya ta k’i. Ta wannan dalili ya sa ko ganin Gimbiya Binta ba ya san yi, don kuwa ba zai manta da asarar da ta jawo masa da kuma halin da ta sanyashi ciki ba. Haka kuma bai fasa zayyanawa amintacciyar baiwarsa yanda ya ke san ta kula da al’amuran Bintu yanda zai kasance ba zai cutu ba har ya samu ta dawo gare shi.
Ana gobe d’aurin aure da daddare aka yiwa Bintu k’unshi irin na amare. Yanda ta ga dare haka ta ga rana, haka ma Yarima Nuhu wanda zazza6i ya rufe har da k’arin ruwa. Aisar kuwa farin cikin zai ga Bintu ne ya hana shi bacci, don da an bi ta tashi da tun aranar zai d’au hanyar Sa’ayrasa, sa idon Junaidu da gudun sharrinshi ya sa ya hakura. Haka ma Yarima Barde wanda farin cikin zai had'u da Gimbiya K'amariyya ya hana shi bacci, da ita kanta Gimbiyar.

******* ******
Washegari tun da sassafe Jakadiya ta sa Bintu wanka da wani ruwan magani gudun kar bak'in da su ka zo daga Fabarusa d’aurin aure su buk'aci ganin amarya, ko kuma Sarki Abdulrahman da kansa ya buk’aci hakan bayan an d’aura masa aure da Bintu ba tare da an shiryawa hakan ba. Leshi fari kyal mai adon koren duwatsu ta ce ta sanya. Farar alkyabba Jakadiya ta d’aura mata bisa, da wani takalmi kore. Kai da ka ga Bintu ka ce d’iyar Sarkin ce, ita kanta Gimbiya Binta da ta shigo ta gan ta sai da ta girgiza, ta kasa zama bare kuma dama tunda Allah ya wayi gari ta ke fama da fad’uwar gaba na ba gaira ba dalili.
Chapter 27 · 0% Book details