Sashe 21
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sarki bai gushe ba ya k’ara da ‘’Nan da mako hud'u za mu amra miki aure ga Masarautar Fabarusa, da an amra za a ba mu bashin da mu ka buk'ata, hallo tarewar ki can sai nan da mako hud'u kan nan kin sami shiri mai kyau. Ba mu amince ba sai da mu ka tabbatar de ke baiwa ce mai tarbiya, dattako da kuma sirri,kasancewar kin iya zama da d’iyar mu lamun lahiya ba tare da ta ta6a kawo mana kukan ki gare mu ba’’
Gimbiya Binta aka zagayar da kwayan ido ta cikin mayafi, cikin ranta fad’i ta ke ‘’Yo to ba girin girin ba d'iyar bayi, ta mai......’’
Jin Sarki ya ce ‘’Hajja Kilishi ga wanga d’iya za ta dawo gare ki ina fatan ke da Jakadiya za ku sa ta hanya, cikin surri ku koyar da ita dabarun Masarauta duk dai yanda Jakadiya ta sheda mana yarinyar dama mai sani ce, mu na so duk kan nan ku sani ba mu yarda ko da wasa wani ya k’ara kiran wannan d’iyar arziki da baiwa ba, haka kuma ban amince a yi mata yanda ake yiwa bayi ba, ku sani wanga d’iya d’iyar mu ce, dan haka a daraja ta’’
Gimbiya ta cije le6e, ita dai kam wannan lamari ba ya mata dad’i, ya Takawa ya ke san mata sakiyar da ba ruwa ne, ko da yake ma ita ina ruwan ta k’arshen ta ajali ne ke kiran Bintu, dan kuwa girman Masarautar Fabarusa ko jinin saraki sai sun shirya zaman ta bare baiwar da za ta je a matsayin Gimbiya, tun da dai ta ci nasarar sa min Aisar, ga shi Gimbiya K’amariyya ta sami Barde ai hutatai. Abunda ta ke jaddadawa zuciyar ta da ta ke nemen fashewa tsabagen bakin cikin kalaman Sarki kenan, bilhakki danasani ta fara, dan kuwa ba ta yi zato ba.
‘’Za mu mayar da d’iyarmu Binta kasar Nigeria, in da za ta je can ta cigaba da karatu kan mu biya bashi ga Masarautar Fabarusa komai ya warware........’’
Gimbiya Binta ba ta san sanda ta tashi tsaye a zabure ba, ta na mai girgiza kai. Nan kallo ya koma gare ta har sai da Yarima Inuwa ya daka mata tsawa ya na mai fad’in
‘’Gide kin manta gaban wa ki ke ne! ko ma ki zauna kar ki mana sakarci a nan’’
Gimbiya K’amariyya ce ta jawo hannunta, yayinda ta koma ta zauna a gajiye, tuni idanunta su ka kawo ruwa, ba ta san sanda ta furta.
‘’Tuba na ke Takawa, Allah ya ja da ran Sarki a min rangwame tuba na ke kar a bari na yi nisa da Mai Martaba’’
‘’Ko kuwa dai ba kya so kiya nisa da Aisar Gaddafi Nur ba’’ Fad’in Gimbiya K’amariyya kenan wacce ke rike da hannun kanwarta ta, cike da tausayi ta ke dubanta, dan kuwa ita kad’ai ta san zafin da ta ji jin za a raba ta da masoyinta Barde, yau kuma gashi ‘yar uwarta na shirin rasa na ta masoyinta sakamakon taimakonta da ta yi. Kana ta kada baki ta ce
"Allah shi ja da ran Sarki, dan Allah a duba lamarin nan, Binta har yanzu yarinya ce, za ta cutu muddin ta yi nisa da mu.’’
Yarima Nuhu na dubansu, bakinshi kunshe da murmushin mugunta ya ce
'’Kar ki fad’awa Takawa wanga yashashen zance haka K’amariyya, idan har wanga d’iya( ya nuna Bintu da yatsa) za ta iya taran aradu da ka ta shiga Masarauta mai girma a cikin badda kama, duk da k’aranci shekarunta, ban ga dalilin da zai sa Binta ba za ta iya zuwa wata k’asar ba domin rufawa masarautar ta asiri ba, yo to menene nan da makwafta Nigeria, ai Nigeria da Nijar d’aita, ko kuwa ki na nufin za a aurar da Bintu matsayin Binta ne kuma jama’a na ganin Binta a k’asar nan, dole sai ta tafi’’
Ya k’arasa magana ya na mai duban Gimbiya Binta da ta ke kuka bilhakki.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
2⃣0⃣
‘’Nuhu ya yi gaskiya, kamar yanda wanga d’iyar arziki ta mana biyayya, mu na fatan ke ma haka za ki kasance me biyayya a gare mu, saboda haka sai ki zauna da shirin ki na bulaguro nan da mako hud'u, komai za a yi jiyo shi cikin surru, kar ku yarda da kowa sai amintaccun bayin ku. Mun yi magana, Mun sallame ku’’
Cewar Sarki kenan ya na mai kawar da kai daga kallan Gimbiya Binta gudun kar ta karya masa zuciya, dan kuwa shi dai yaransa su an rauninsa.
Komawarsu d’aki nan Gimbiya K'amariyya ta ga kuka da daru gun Gimbiya Binta, ba shiri Inna Salti da Hajja Kilishi su ka sallami bayin da ke cikin 6angaran gudun yad’uwar maganar. Wanda kuma su ka riga su ka ga halin da Gimbiya Binta ke ciki, Jakadiya ce ta tara su, cikin hikima ta mu su kashedin ko da wasa kar su yarda a ji halin da Gimbiya Binta ta shiga jin Mai martaba ya ba da amran ta ga Sarkin Fabarusa, duk wanda aka ji a bakin sa sai dai uwar sa ta haifi wani. Ai kuwa dai ba su fasa yad’awa ba, ta yanda Allah ya so ma maganar Jakadiya su ke yad’awa ba asalin zancen gaskiya ba.
Dakyar aka samu Gimbiya Binta ta sarara da kukan da ta ke, ita sam ta manta da azanci a maimakon ita za a aurar da Bintu, kasancewar haka ita ma sai an 6oyeta na wani d’an lokaci. Gashi Mai martaba ya ‘yan ta Bintu, wacce ta ke baiwar ta tin tale tale. Bauhaushe dai yayi gaskiya, in za ka gida ramin mugunta, ka gina shi gajere.
Da yamma Bintu na zaune d’aki tare da Hajja Kilishi, ilimin zaman fada ta ke ta koya mata, amma ita sam hankalin ta ma ba ya wajan dan haka ba wani ganewa ta ke ba. Zuba ido ta ke ko za ta ga Innar ta, amma babu Inna baba alamar ta. Hajja Kilishi ta ce da Bintu ta lek’a falo ta ce da d'aya daga cikin bayin ta maza su je 6angaransu Gimbiya K’amariyya su k’ar6o ma Bintu sak’o.
Ko da Bintu ta fito, ta bayin sai kai kawo su ke cikin hidimansu, sai ta kasa tsaida d’aya ta aika, duk da dai yanzu ba cikin sahun su ta ke ba inji Sarki, ita har yanzu ba ta ji wani canji ba, dan haka yanda su ke haka ta d'auki kanta, sutarar jikinta ma kayan bayin Sa'ayrasa ne wanda dama shi ne a jikinta tun safe da su Jakadiya su ka zo tafiya da ita. Hakan ya sa ta yanke hukuncin zuwa da kanta 6angaren. Ta na sa k’afa cikin falon ta yi ido biyu da Gimbiya Binta, wacce fitowar ta daga d’akin K'amariyya kenan, idanun nan sun yi jajur.
Ganinta Bintu ji ta yi kamar ta koma a guje, ile kuwa bud’ar bakin Gimbiya Binta sai cewa ta yi
'’Ke har kin isa ki nuna fuskarki gabana dan ubanki! Ya ki nan munafuka!’’
Jikin Bintu na rawa ta k’arasa gaban Gimbiya ta na mai zubewa a k’asa ta ce
‘’Kimin rai, tuba na ke Gimbiya’’
‘’A gidan ubanwa ki ke tuba! Oho wato Takawa ya ce kin zama daidai da kowa shi ya sa ki ka zo gwada kafad'a da sa’annin ki ko? Shu’uma daina rawar k’afa, kwalla ba amre ba ne! ki na cikin hatsari muddin Masarautar Fabarusa su ka san ke fa baiwa ce kuma d’iyar bayi, zamanki a Masarautar na d’an wani lokaci ne har sai mun cika burinmu, na farko shi ne na gama makaranta na kuma amri masoyi na Aisar, na biyu Didi ta amri burin ranta, wato Barde, na uku Mai Martaba ya biya bashi ba tare da an yi amfani da farin cikin iyalinsa ba, ke kuwa Allah kad’ai ya san ya rayuwar ki za ta kasance, hallo tsire ki Sarki Abdulraman zai sa a yi idan ya gano mak’aryaciya ya ke amre.....’’
‘’Ku kuwa Masarautar mak’aryata su ka bashi amren ta ba.....’’
Yarima Nuhu ne ya katse ta, da sauri ta juya ta kai kallonta gare shi, ashe ya shigo ba ta sani ba. Ya na jingine jikin bango daga bakin k'ofa, hannunsa sarke bisa k’irjinsa. Sanye ya ke cikin shud’ayan kaya, ya d’aura farar falmaran akai. Bai gushe ba ya k’ara.
‘’Ina tunanin halin da ki ke ciki ya sa ni tattaki dan zuwa na ganki, ba shakka garau ki ke tun da gashi kin sa d’iyar arziki gaba ki na mata yashasshen zance irin na marasa tunani, shin kin manta wanga d’iya ba baiwa ba ce?’’
Yanda ya ga ta cuna baki ya sa shi fad’in
‘’Dakyau, yanzu ina ga kin tuna, dan haka na miki uziri, amma daga yanzu ba na fatan sake tuna miki, hallo za ki kula.'’
Ya mayar da kallonsa ga Bintu,
"Bintun arziki tashi ki yi tafiyar ki, gide kar ki sake tsugunnawa haka gaban kowa, tabbas akwai aiki ja gaban Jakadiya muddin za ki kasance mata ga Sarkin Fabarusa dole ki wuce raini, ke ba baiwa bace, kar ki ta6a mantawa da wannan.’’
Da saurin ta ta tashi, ta na mai godiya ga Yarima Nuhu, ta bi ta gaban Gimbiya Binta, ta zo gaban Yarima Nuhu sannan ta fice ba tare da ta damu da ta k’arbo sakon na ta gun Gimbiya K’amariyya ba.
Ganin yanda ta ke tafiya ba Yarima Nuhu ba, hatta Gimbiya Binta sai da ta bita da ido, ba ta san sanda ta je tsaki ba ta ce
‘’Mtsw! Ka ga yanda ta ke tafiya d’iyar bayi sai shegen tak’ama da isa.'’
Ciki Yarima Nuhu ya shigo sosai, yayinda ya sami kujera ya zauna ya na mai murmushi ya ke duban k'anwar ta sa sannan ya ce
'’Halittarta ce haka’’
Da sauri Gimbiya ta dawo da kallonta gareshi, cikin rashin fahimta ta ce ‘’Na’am?’’
Gimbiya Binta aka zagayar da kwayan ido ta cikin mayafi, cikin ranta fad’i ta ke ‘’Yo to ba girin girin ba d'iyar bayi, ta mai......’’
Jin Sarki ya ce ‘’Hajja Kilishi ga wanga d’iya za ta dawo gare ki ina fatan ke da Jakadiya za ku sa ta hanya, cikin surri ku koyar da ita dabarun Masarauta duk dai yanda Jakadiya ta sheda mana yarinyar dama mai sani ce, mu na so duk kan nan ku sani ba mu yarda ko da wasa wani ya k’ara kiran wannan d’iyar arziki da baiwa ba, haka kuma ban amince a yi mata yanda ake yiwa bayi ba, ku sani wanga d’iya d’iyar mu ce, dan haka a daraja ta’’
Gimbiya ta cije le6e, ita dai kam wannan lamari ba ya mata dad’i, ya Takawa ya ke san mata sakiyar da ba ruwa ne, ko da yake ma ita ina ruwan ta k’arshen ta ajali ne ke kiran Bintu, dan kuwa girman Masarautar Fabarusa ko jinin saraki sai sun shirya zaman ta bare baiwar da za ta je a matsayin Gimbiya, tun da dai ta ci nasarar sa min Aisar, ga shi Gimbiya K’amariyya ta sami Barde ai hutatai. Abunda ta ke jaddadawa zuciyar ta da ta ke nemen fashewa tsabagen bakin cikin kalaman Sarki kenan, bilhakki danasani ta fara, dan kuwa ba ta yi zato ba.
‘’Za mu mayar da d’iyarmu Binta kasar Nigeria, in da za ta je can ta cigaba da karatu kan mu biya bashi ga Masarautar Fabarusa komai ya warware........’’
Gimbiya Binta ba ta san sanda ta tashi tsaye a zabure ba, ta na mai girgiza kai. Nan kallo ya koma gare ta har sai da Yarima Inuwa ya daka mata tsawa ya na mai fad’in
‘’Gide kin manta gaban wa ki ke ne! ko ma ki zauna kar ki mana sakarci a nan’’
Gimbiya K’amariyya ce ta jawo hannunta, yayinda ta koma ta zauna a gajiye, tuni idanunta su ka kawo ruwa, ba ta san sanda ta furta.
‘’Tuba na ke Takawa, Allah ya ja da ran Sarki a min rangwame tuba na ke kar a bari na yi nisa da Mai Martaba’’
‘’Ko kuwa dai ba kya so kiya nisa da Aisar Gaddafi Nur ba’’ Fad’in Gimbiya K’amariyya kenan wacce ke rike da hannun kanwarta ta, cike da tausayi ta ke dubanta, dan kuwa ita kad’ai ta san zafin da ta ji jin za a raba ta da masoyinta Barde, yau kuma gashi ‘yar uwarta na shirin rasa na ta masoyinta sakamakon taimakonta da ta yi. Kana ta kada baki ta ce
"Allah shi ja da ran Sarki, dan Allah a duba lamarin nan, Binta har yanzu yarinya ce, za ta cutu muddin ta yi nisa da mu.’’
Yarima Nuhu na dubansu, bakinshi kunshe da murmushin mugunta ya ce
'’Kar ki fad’awa Takawa wanga yashashen zance haka K’amariyya, idan har wanga d’iya( ya nuna Bintu da yatsa) za ta iya taran aradu da ka ta shiga Masarauta mai girma a cikin badda kama, duk da k’aranci shekarunta, ban ga dalilin da zai sa Binta ba za ta iya zuwa wata k’asar ba domin rufawa masarautar ta asiri ba, yo to menene nan da makwafta Nigeria, ai Nigeria da Nijar d’aita, ko kuwa ki na nufin za a aurar da Bintu matsayin Binta ne kuma jama’a na ganin Binta a k’asar nan, dole sai ta tafi’’
Ya k’arasa magana ya na mai duban Gimbiya Binta da ta ke kuka bilhakki.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
2⃣0⃣
‘’Nuhu ya yi gaskiya, kamar yanda wanga d’iyar arziki ta mana biyayya, mu na fatan ke ma haka za ki kasance me biyayya a gare mu, saboda haka sai ki zauna da shirin ki na bulaguro nan da mako hud'u, komai za a yi jiyo shi cikin surru, kar ku yarda da kowa sai amintaccun bayin ku. Mun yi magana, Mun sallame ku’’
Cewar Sarki kenan ya na mai kawar da kai daga kallan Gimbiya Binta gudun kar ta karya masa zuciya, dan kuwa shi dai yaransa su an rauninsa.
Komawarsu d’aki nan Gimbiya K'amariyya ta ga kuka da daru gun Gimbiya Binta, ba shiri Inna Salti da Hajja Kilishi su ka sallami bayin da ke cikin 6angaran gudun yad’uwar maganar. Wanda kuma su ka riga su ka ga halin da Gimbiya Binta ke ciki, Jakadiya ce ta tara su, cikin hikima ta mu su kashedin ko da wasa kar su yarda a ji halin da Gimbiya Binta ta shiga jin Mai martaba ya ba da amran ta ga Sarkin Fabarusa, duk wanda aka ji a bakin sa sai dai uwar sa ta haifi wani. Ai kuwa dai ba su fasa yad’awa ba, ta yanda Allah ya so ma maganar Jakadiya su ke yad’awa ba asalin zancen gaskiya ba.
Dakyar aka samu Gimbiya Binta ta sarara da kukan da ta ke, ita sam ta manta da azanci a maimakon ita za a aurar da Bintu, kasancewar haka ita ma sai an 6oyeta na wani d’an lokaci. Gashi Mai martaba ya ‘yan ta Bintu, wacce ta ke baiwar ta tin tale tale. Bauhaushe dai yayi gaskiya, in za ka gida ramin mugunta, ka gina shi gajere.
Da yamma Bintu na zaune d’aki tare da Hajja Kilishi, ilimin zaman fada ta ke ta koya mata, amma ita sam hankalin ta ma ba ya wajan dan haka ba wani ganewa ta ke ba. Zuba ido ta ke ko za ta ga Innar ta, amma babu Inna baba alamar ta. Hajja Kilishi ta ce da Bintu ta lek’a falo ta ce da d'aya daga cikin bayin ta maza su je 6angaransu Gimbiya K’amariyya su k’ar6o ma Bintu sak’o.
Ko da Bintu ta fito, ta bayin sai kai kawo su ke cikin hidimansu, sai ta kasa tsaida d’aya ta aika, duk da dai yanzu ba cikin sahun su ta ke ba inji Sarki, ita har yanzu ba ta ji wani canji ba, dan haka yanda su ke haka ta d'auki kanta, sutarar jikinta ma kayan bayin Sa'ayrasa ne wanda dama shi ne a jikinta tun safe da su Jakadiya su ka zo tafiya da ita. Hakan ya sa ta yanke hukuncin zuwa da kanta 6angaren. Ta na sa k’afa cikin falon ta yi ido biyu da Gimbiya Binta, wacce fitowar ta daga d’akin K'amariyya kenan, idanun nan sun yi jajur.
Ganinta Bintu ji ta yi kamar ta koma a guje, ile kuwa bud’ar bakin Gimbiya Binta sai cewa ta yi
'’Ke har kin isa ki nuna fuskarki gabana dan ubanki! Ya ki nan munafuka!’’
Jikin Bintu na rawa ta k’arasa gaban Gimbiya ta na mai zubewa a k’asa ta ce
‘’Kimin rai, tuba na ke Gimbiya’’
‘’A gidan ubanwa ki ke tuba! Oho wato Takawa ya ce kin zama daidai da kowa shi ya sa ki ka zo gwada kafad'a da sa’annin ki ko? Shu’uma daina rawar k’afa, kwalla ba amre ba ne! ki na cikin hatsari muddin Masarautar Fabarusa su ka san ke fa baiwa ce kuma d’iyar bayi, zamanki a Masarautar na d’an wani lokaci ne har sai mun cika burinmu, na farko shi ne na gama makaranta na kuma amri masoyi na Aisar, na biyu Didi ta amri burin ranta, wato Barde, na uku Mai Martaba ya biya bashi ba tare da an yi amfani da farin cikin iyalinsa ba, ke kuwa Allah kad’ai ya san ya rayuwar ki za ta kasance, hallo tsire ki Sarki Abdulraman zai sa a yi idan ya gano mak’aryaciya ya ke amre.....’’
‘’Ku kuwa Masarautar mak’aryata su ka bashi amren ta ba.....’’
Yarima Nuhu ne ya katse ta, da sauri ta juya ta kai kallonta gare shi, ashe ya shigo ba ta sani ba. Ya na jingine jikin bango daga bakin k'ofa, hannunsa sarke bisa k’irjinsa. Sanye ya ke cikin shud’ayan kaya, ya d’aura farar falmaran akai. Bai gushe ba ya k’ara.
‘’Ina tunanin halin da ki ke ciki ya sa ni tattaki dan zuwa na ganki, ba shakka garau ki ke tun da gashi kin sa d’iyar arziki gaba ki na mata yashasshen zance irin na marasa tunani, shin kin manta wanga d’iya ba baiwa ba ce?’’
Yanda ya ga ta cuna baki ya sa shi fad’in
‘’Dakyau, yanzu ina ga kin tuna, dan haka na miki uziri, amma daga yanzu ba na fatan sake tuna miki, hallo za ki kula.'’
Ya mayar da kallonsa ga Bintu,
"Bintun arziki tashi ki yi tafiyar ki, gide kar ki sake tsugunnawa haka gaban kowa, tabbas akwai aiki ja gaban Jakadiya muddin za ki kasance mata ga Sarkin Fabarusa dole ki wuce raini, ke ba baiwa bace, kar ki ta6a mantawa da wannan.’’
Da saurin ta ta tashi, ta na mai godiya ga Yarima Nuhu, ta bi ta gaban Gimbiya Binta, ta zo gaban Yarima Nuhu sannan ta fice ba tare da ta damu da ta k’arbo sakon na ta gun Gimbiya K’amariyya ba.
Ganin yanda ta ke tafiya ba Yarima Nuhu ba, hatta Gimbiya Binta sai da ta bita da ido, ba ta san sanda ta je tsaki ba ta ce
‘’Mtsw! Ka ga yanda ta ke tafiya d’iyar bayi sai shegen tak’ama da isa.'’
Ciki Yarima Nuhu ya shigo sosai, yayinda ya sami kujera ya zauna ya na mai murmushi ya ke duban k'anwar ta sa sannan ya ce
'’Halittarta ce haka’’
Da sauri Gimbiya ta dawo da kallonta gareshi, cikin rashin fahimta ta ce ‘’Na’am?’’