Sashe 6
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan haka ya k’ara tambayar "su waye ‘yan masarautar Faburasa cikin ajin nan?’’ wajan mutum uku ne su ka d’aga hannu, bayan wani d'an sakanni ya ce su sauke, masarautar Sa’ayrasa ma su d’aga hannu. D’alibai shida ne su ka d’aga hannu, ciki har da Gimbiya. Bintu kuwa ta na can ta na tunanin duniya, gaba d’aya hankalin ta ba ya ajin. Hannun su d'age be ba su izinin saukewa ba dan shi hankalin sa kan Bintu ya ke, suma kuma ‘yan ajin sun lura da hakan dan su ma d’in Bintu da ta doka uban tagumi su ke kallo.
Kamar daga sama ta ji ya ce ‘’Bintu hankalin ki ba ya aji na!’’ ta yi firgit ta dawo cikin hankalin ta ta na mai cire hannun ta daga tagumin da ta yi. Ganin idanun kowa kan ta, ga hannun wasu daga cikin yan ajin har da Gimbiya d’age ya sa Bintu kai duban ta ga Aisar, in da shi kuma ya maimaita mata umarnin da ya ba su. Da saurin ta ta d’aga na ta hannun sama sannan ya ce su aje hannun na su. Wata har da fad’in "wash hanuna" a hankali yanda Aisar ba zai jiyo ta ba.
Bintu ba ta tsorata ba sai da ta ga Gimbiya ta juyo ta watsa mata harara. Wani mugun yawu ta had’iya tuni hantar cikin ta ta kad’a. Malam Aisar kuwa be gushe ba ya cigaba da "shin wa zai fad’a min lokacin da gabar ta samo asali?’’ d’aya daga cikin su ta amsa da "gabar ta samo asali ne tun kaka da kakanni amma anfi dangan ta shi da lokacin mulkin sarki Abdulrahaman III na masarautar Faburusa’’ Malam Aisar ya ce a tafa mata sannan ya sake tambayar hanyoyin da ya dace a bi domin kawo karshen gaba tsakanin k’asa da k’asa ko masarauta da masarauta. Dalibai da yawa su ka d’aga hannu, amma ga mamakin kowa sai ji su ka yi ya ambaci sunan "Bintu’’
‘’Wayyo shi dai sai ya fad’awa kowa ya san sunana ko menene haka?’’ ihun da Bintu ta kurma cikin ran ta kenan. Gaba d’aya ajin idanu su ka zubo mata yayinda ta tashi a hankali murya kamar ba nata ta ba, ta furta abun da ya fara zuwa bakin ta "auratayya tsakanin masarautar’’ nan fa aji aka kwashe da dariya, Zahira ta ce "auratayya tsakanin bayi, d’iyar bayi ta auri dan bayi.....’’ aka dad’a sa dariya.
Kunya ta rufe Bintu kamar ta shige k’ark’ashin kujera ta 6uya. "shiru!’’ Aisar ya daka musu tsawa. Aji yayi shiru kamar wanda ruwa ya shanye, ran malam ya 6aci. ‘’wata mara tarbiya ce ta yi wannan maganar?’’ ya tambaya a fusace. Aka rasa mai bashi amsa, har sai da ya sake maimaitawa sannan Zahira ta tashi tsaye gwiwa a sanyaye. Bintu ya duba ya umarce ta da ta zauna kafin ya koma ga Zahira. Ya ce da yan aji kowa ya dube ta, shin ita yar wata yanki ce. Ta na zumb’ure zumb’ure ta amsa da ‘’Niamey’’ kai ya girgiza kan ya ce ‘’Niamey na alawadar da masu hali da kalimi irin na ki, kalamai ne irin na marasa tarbiya wanda su ka tashi a watse, lalle idan har Jamhuriyar Nijar na da yan k’asa irin gaba tsakanin yankuna ba zai tab’a yankewa ba, fitar min daga aji kuma kar ki sake shigowa in har ni ne cikin ajin’’ Zahira ta wuce fuuuu za ta fita ya ce ‘’dube ta k’azama kawai’’ kunya ya rufe ta ta fice da sauri.
Jikin kowa yayi sanyi, tin ba ma Bintu ba. Aisar kuwa be sake cikakken minti goma ba ya fice da ga ajin,dan kuwa tabbas d’aliban makarantar na fama da rashin tarbiya na gaske. Surutai kuwa ta sha wajan yan aji, daga mai fad’in "kun ji yanda ya ke kiran sunan ta kuwa?’’ sai mai fad’in ‘’ta yaya ya san sunan ta bayan be ta6a tambayar sunayen mu ba?’’ ita kuwa Bintu kai ta kifa bisa teburi dan Allah kad’ai ya san masifun da ke gudana cikin zuciyar Gimbiya, ta san yau kam sai yanda aka yi da ita wai d'an daudu a kabari.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣5⃣
Bayan an tashi daga makaranta, ko kallan ta Gimbiya Binta ba ta yi ba ta ta wuce gaba ita da Ruqayya, Bintu na rawar jiki rik’e da jakar Gimbiya ta bi bayan su. Ba su zame koina ba sai d’akin su in da su ka tadda Zahira na jiran su dan gasawa Bintu gurasa danya a hannu.
Zagaye Bintu su ka yi tsakiyar d’aki, sai ta fad’a musu yanda aka yi Aisar ya san ta yasan sunanta da har ya ci mutuncin Zahira saboda ita. Bintu na raba idanu ta ce ‘’Dan Allah Gimbiya ki min afuwa, aradu shi da kan sa ya tambayi sunana........’’
Ji ka kake tas! Gimbiya ta kwashe ta da marin da sai da Bintu ta ga wuta a idonta, a gigice ta sa hannu bisa kuncin ta na mai fashewa da kuka. Gimbiya ba ta gushe ba ta ce " Yar iska! A shekarun ki har kin iya karuwanci?!!!’’ Ta sa k'afa ta shure Bintu. "Yo dama ana raba bayi da karuwanci ne Gimbiya?’’ Rukayya ce ta ara ta yafa. Zahira ta k’ara da, "Wallahi tunda ki ka sa mutum kamar Aisar ya ci mutuncina sai kin yabawa aya zak’inta."
Ita dai Bintu ta kasa magana, kanta durk’ushe, sautin kuka kad’ai ke iya fita daga bakinta. Gimbiya ta ce ko dai ta fad’a mu su yanda aka yi ya san ta har ya tambayi sunan ta ko ta kira waya fada a zo a mayar da ita Sa’ayrasa. Jin haka haka nan da nan Bintu ta shaida musu komai. Duka da mari babu wanda ba ta sha ba. A fad’ar Gimbiya don tasan tana da k’udirin auren Aisar ya sa ta ke masa shisshigi dan ta 6ata ta wajan shi, toh wallahi ta yi kad’an, duk randa ta yarda wani abu ya k’ara shiga tsakanin su ta tabbatar ranar zaman ta a wannan makarantar ya k’are. "Godiya nake Gimbiya’’ a
Abinda ke fita daga bakin Bintu kenan har su ka k’araci masifar su, su ka tafi d’akin Zahira.
Bintu na zaune inda suka bar ta, ta had’e kai da gwiwa in ban da ajiyar zuciya babu abun da ta ke, sai ga Iya Dije ta shigo da sallamar ta. Ganinta Bintu ta yi saurin gyara zama ta na mai k’ok’arin goge hawayen da ke fuskar ta gudan kar Iye Dije ta gani. Cike da mamaki Iye Dije ta ce "Bintu lafiya? Me ya sa ki kuka haka? Ya na ga idonki d’aya ya kumbura?’’ "Ba na jin dad’i ne Iya Dije, ciwon kai da ido na ke’’ Bintu ta yiwa Iya Dije k’arya gudun abun da zai je ya dawo. Cikin nuna tausayawa Iya Dije ta ce " Ayya Allah ya sauwake, na ce dai kin je kilinik (clinique, karamin asibitin makarantar) an duba ki ko?’’ Kai Bintu ta girgiza alamar ah ah, sannan ta k’ara da ‘’Ba sai na je ba, ina da magani, idan na sha shikenan."
Kallan ta Iya Dije ta ke kamar mai nazarin wani abu, kafin daga bisani ta ce ‘’Toh Allah ya sauke.’’ Ta ja wata yar kujera ta zauna sai a sannan Bintu ta lura da ledar hannunta, a gaban Bintu ta aje ledar kan ta tambaya "Shin al’adar ta ki ta d’auke ne?’’ Cikin nuna jin kunya Bintu ta girgiza kai alamar ah ah. Iya Dije ta ce "Ai bakomai, dama daga kwana d’aya har zuwa kwanaki goma sha biyar yakan iya kai wa. Dama batun turaren ne, Malam Aisar ya ba ni kud’i, sanin ba a bari dalibai su fita daga makaranta yasa na yi karambani na siyo miki’’ Ta sa hannu cikin ledar sai gashi ta fito da kwalaban turare har guda uku, ta aje gaban Bintu ta na fad’in ‘’Kinga wannan Danduwala ne, ga kuma Kafin-kafin, ga Binta Sudan duka na ki ne." Ta k’arasa maganar tana mai washe hak'ora don tasan ba k'aramin gwanin ta ta yiwa Bintu ba, duk da dai rabin kud’in da Aisar ya bata a aljihun ta ya k'are.
Bud’ar bakin Bintu sai cewa ta yi "Iye Dije na gode amma dan Allah ki mayar masa, aradu ba zan iya karb'a ba, ba na so’’ ‘’La'ilaha illallahu!" Fad’in Iye Dije ta na mai tafa hannu "Ku ga yarinya za ta watsan k'asa a ido! Ba kya so a na wani dalili? Iyye?!!!’’ Ta yi tambayar ta na mai fidda idanu ganin Bintu na shirin kwance mata zani a kasuwa, don kuwa karya da gaskiya ta had’a ta fad’awa Aisar kan buk’atun Bintu, haka ya bata kud’i CFA na gugan CFA har (10000 CFA), fiye da rabin kud’in ta kashe. Bintu ta rasa amsar da za ta bata, ta tsinci kanta tana mai fad’in ‘’Na ga ba na buk’ata ne Iya Dije.’’
Ba ta ankara ba sai ganin Iya Dije ta yi ta d’aga hannunta tana mai k’ok’arin cusa hancin ta k’ark’ashin hammatar Bintu. Da sauri Bintu ta ja da baya ta na k’ok’arin kwatar kanta, fad’i ta ke ‘’Iye Dije ya haka?” Iya Dije kuwa duk da babu abinda ta shak’a na wari daga jikin Bintu don kuwa Bintu irin mutanen nan ne wanda sam ba su da warin jiki, sai ga ta ta yi baya da sauri ta na mai toshe hanci ‘’Kin ji yanda ki ke bugawa ki na hamami kuwa? Har ki ce ba kya buk’ata? Shi kan shi Malam Aisar d’in wannan hamamin na ki ya ji shi ya sa ya ce na tambaya ko ki na da buk’atar turaren.’’
Kamar daga sama ta ji ya ce ‘’Bintu hankalin ki ba ya aji na!’’ ta yi firgit ta dawo cikin hankalin ta ta na mai cire hannun ta daga tagumin da ta yi. Ganin idanun kowa kan ta, ga hannun wasu daga cikin yan ajin har da Gimbiya d’age ya sa Bintu kai duban ta ga Aisar, in da shi kuma ya maimaita mata umarnin da ya ba su. Da saurin ta ta d’aga na ta hannun sama sannan ya ce su aje hannun na su. Wata har da fad’in "wash hanuna" a hankali yanda Aisar ba zai jiyo ta ba.
Bintu ba ta tsorata ba sai da ta ga Gimbiya ta juyo ta watsa mata harara. Wani mugun yawu ta had’iya tuni hantar cikin ta ta kad’a. Malam Aisar kuwa be gushe ba ya cigaba da "shin wa zai fad’a min lokacin da gabar ta samo asali?’’ d’aya daga cikin su ta amsa da "gabar ta samo asali ne tun kaka da kakanni amma anfi dangan ta shi da lokacin mulkin sarki Abdulrahaman III na masarautar Faburusa’’ Malam Aisar ya ce a tafa mata sannan ya sake tambayar hanyoyin da ya dace a bi domin kawo karshen gaba tsakanin k’asa da k’asa ko masarauta da masarauta. Dalibai da yawa su ka d’aga hannu, amma ga mamakin kowa sai ji su ka yi ya ambaci sunan "Bintu’’
‘’Wayyo shi dai sai ya fad’awa kowa ya san sunana ko menene haka?’’ ihun da Bintu ta kurma cikin ran ta kenan. Gaba d’aya ajin idanu su ka zubo mata yayinda ta tashi a hankali murya kamar ba nata ta ba, ta furta abun da ya fara zuwa bakin ta "auratayya tsakanin masarautar’’ nan fa aji aka kwashe da dariya, Zahira ta ce "auratayya tsakanin bayi, d’iyar bayi ta auri dan bayi.....’’ aka dad’a sa dariya.
Kunya ta rufe Bintu kamar ta shige k’ark’ashin kujera ta 6uya. "shiru!’’ Aisar ya daka musu tsawa. Aji yayi shiru kamar wanda ruwa ya shanye, ran malam ya 6aci. ‘’wata mara tarbiya ce ta yi wannan maganar?’’ ya tambaya a fusace. Aka rasa mai bashi amsa, har sai da ya sake maimaitawa sannan Zahira ta tashi tsaye gwiwa a sanyaye. Bintu ya duba ya umarce ta da ta zauna kafin ya koma ga Zahira. Ya ce da yan aji kowa ya dube ta, shin ita yar wata yanki ce. Ta na zumb’ure zumb’ure ta amsa da ‘’Niamey’’ kai ya girgiza kan ya ce ‘’Niamey na alawadar da masu hali da kalimi irin na ki, kalamai ne irin na marasa tarbiya wanda su ka tashi a watse, lalle idan har Jamhuriyar Nijar na da yan k’asa irin gaba tsakanin yankuna ba zai tab’a yankewa ba, fitar min daga aji kuma kar ki sake shigowa in har ni ne cikin ajin’’ Zahira ta wuce fuuuu za ta fita ya ce ‘’dube ta k’azama kawai’’ kunya ya rufe ta ta fice da sauri.
Jikin kowa yayi sanyi, tin ba ma Bintu ba. Aisar kuwa be sake cikakken minti goma ba ya fice da ga ajin,dan kuwa tabbas d’aliban makarantar na fama da rashin tarbiya na gaske. Surutai kuwa ta sha wajan yan aji, daga mai fad’in "kun ji yanda ya ke kiran sunan ta kuwa?’’ sai mai fad’in ‘’ta yaya ya san sunan ta bayan be ta6a tambayar sunayen mu ba?’’ ita kuwa Bintu kai ta kifa bisa teburi dan Allah kad’ai ya san masifun da ke gudana cikin zuciyar Gimbiya, ta san yau kam sai yanda aka yi da ita wai d'an daudu a kabari.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
0⃣5⃣
Bayan an tashi daga makaranta, ko kallan ta Gimbiya Binta ba ta yi ba ta ta wuce gaba ita da Ruqayya, Bintu na rawar jiki rik’e da jakar Gimbiya ta bi bayan su. Ba su zame koina ba sai d’akin su in da su ka tadda Zahira na jiran su dan gasawa Bintu gurasa danya a hannu.
Zagaye Bintu su ka yi tsakiyar d’aki, sai ta fad’a musu yanda aka yi Aisar ya san ta yasan sunanta da har ya ci mutuncin Zahira saboda ita. Bintu na raba idanu ta ce ‘’Dan Allah Gimbiya ki min afuwa, aradu shi da kan sa ya tambayi sunana........’’
Ji ka kake tas! Gimbiya ta kwashe ta da marin da sai da Bintu ta ga wuta a idonta, a gigice ta sa hannu bisa kuncin ta na mai fashewa da kuka. Gimbiya ba ta gushe ba ta ce " Yar iska! A shekarun ki har kin iya karuwanci?!!!’’ Ta sa k'afa ta shure Bintu. "Yo dama ana raba bayi da karuwanci ne Gimbiya?’’ Rukayya ce ta ara ta yafa. Zahira ta k’ara da, "Wallahi tunda ki ka sa mutum kamar Aisar ya ci mutuncina sai kin yabawa aya zak’inta."
Ita dai Bintu ta kasa magana, kanta durk’ushe, sautin kuka kad’ai ke iya fita daga bakinta. Gimbiya ta ce ko dai ta fad’a mu su yanda aka yi ya san ta har ya tambayi sunan ta ko ta kira waya fada a zo a mayar da ita Sa’ayrasa. Jin haka haka nan da nan Bintu ta shaida musu komai. Duka da mari babu wanda ba ta sha ba. A fad’ar Gimbiya don tasan tana da k’udirin auren Aisar ya sa ta ke masa shisshigi dan ta 6ata ta wajan shi, toh wallahi ta yi kad’an, duk randa ta yarda wani abu ya k’ara shiga tsakanin su ta tabbatar ranar zaman ta a wannan makarantar ya k’are. "Godiya nake Gimbiya’’ a
Abinda ke fita daga bakin Bintu kenan har su ka k’araci masifar su, su ka tafi d’akin Zahira.
Bintu na zaune inda suka bar ta, ta had’e kai da gwiwa in ban da ajiyar zuciya babu abun da ta ke, sai ga Iya Dije ta shigo da sallamar ta. Ganinta Bintu ta yi saurin gyara zama ta na mai k’ok’arin goge hawayen da ke fuskar ta gudan kar Iye Dije ta gani. Cike da mamaki Iye Dije ta ce "Bintu lafiya? Me ya sa ki kuka haka? Ya na ga idonki d’aya ya kumbura?’’ "Ba na jin dad’i ne Iya Dije, ciwon kai da ido na ke’’ Bintu ta yiwa Iya Dije k’arya gudun abun da zai je ya dawo. Cikin nuna tausayawa Iya Dije ta ce " Ayya Allah ya sauwake, na ce dai kin je kilinik (clinique, karamin asibitin makarantar) an duba ki ko?’’ Kai Bintu ta girgiza alamar ah ah, sannan ta k’ara da ‘’Ba sai na je ba, ina da magani, idan na sha shikenan."
Kallan ta Iya Dije ta ke kamar mai nazarin wani abu, kafin daga bisani ta ce ‘’Toh Allah ya sauke.’’ Ta ja wata yar kujera ta zauna sai a sannan Bintu ta lura da ledar hannunta, a gaban Bintu ta aje ledar kan ta tambaya "Shin al’adar ta ki ta d’auke ne?’’ Cikin nuna jin kunya Bintu ta girgiza kai alamar ah ah. Iya Dije ta ce "Ai bakomai, dama daga kwana d’aya har zuwa kwanaki goma sha biyar yakan iya kai wa. Dama batun turaren ne, Malam Aisar ya ba ni kud’i, sanin ba a bari dalibai su fita daga makaranta yasa na yi karambani na siyo miki’’ Ta sa hannu cikin ledar sai gashi ta fito da kwalaban turare har guda uku, ta aje gaban Bintu ta na fad’in ‘’Kinga wannan Danduwala ne, ga kuma Kafin-kafin, ga Binta Sudan duka na ki ne." Ta k’arasa maganar tana mai washe hak'ora don tasan ba k'aramin gwanin ta ta yiwa Bintu ba, duk da dai rabin kud’in da Aisar ya bata a aljihun ta ya k'are.
Bud’ar bakin Bintu sai cewa ta yi "Iye Dije na gode amma dan Allah ki mayar masa, aradu ba zan iya karb'a ba, ba na so’’ ‘’La'ilaha illallahu!" Fad’in Iye Dije ta na mai tafa hannu "Ku ga yarinya za ta watsan k'asa a ido! Ba kya so a na wani dalili? Iyye?!!!’’ Ta yi tambayar ta na mai fidda idanu ganin Bintu na shirin kwance mata zani a kasuwa, don kuwa karya da gaskiya ta had’a ta fad’awa Aisar kan buk’atun Bintu, haka ya bata kud’i CFA na gugan CFA har (10000 CFA), fiye da rabin kud’in ta kashe. Bintu ta rasa amsar da za ta bata, ta tsinci kanta tana mai fad’in ‘’Na ga ba na buk’ata ne Iya Dije.’’
Ba ta ankara ba sai ganin Iya Dije ta yi ta d’aga hannunta tana mai k’ok’arin cusa hancin ta k’ark’ashin hammatar Bintu. Da sauri Bintu ta ja da baya ta na k’ok’arin kwatar kanta, fad’i ta ke ‘’Iye Dije ya haka?” Iya Dije kuwa duk da babu abinda ta shak’a na wari daga jikin Bintu don kuwa Bintu irin mutanen nan ne wanda sam ba su da warin jiki, sai ga ta ta yi baya da sauri ta na mai toshe hanci ‘’Kin ji yanda ki ke bugawa ki na hamami kuwa? Har ki ce ba kya buk’ata? Shi kan shi Malam Aisar d’in wannan hamamin na ki ya ji shi ya sa ya ce na tambaya ko ki na da buk’atar turaren.’’