← Book details Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 28

Sashe 13

Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ajiyar zuci Bintu ta saki tare da fad'in "Yo to Inna ai dalili ne ke sa a kama kaluluwar sarakuwa...(Dalili ke sa a kama kaluluwar sirika)"

Inna na girgiza kai ta ce "Na ce ki bar maganar ga Bintu, ba na kwawarniya shiga rumbum k'ore."

Ta na mai jinjina kai ta bar maganar, fatanta Allah ya kawo musu d'auki, Inna ta amsa mata da amin. Ranar har Bintu ta kwanta ba ta ga dawowar mahaifinta ba, dama dai idan ana cikin fari har kwana ya kan yi can fada.

***** ******
Washegari da sassafe, Bintu na bacci wata baiwa daga babban gida ta yiwa Inna sallama. Inna da ta yi zatan kiran na ta ne ta ce ‘’Allah sarki, hallau kun ji ni shiru ko?’’

Jin haka baiwa ta ce ‘’Gide kiran ga ba na ki ba Uwar bayi, wannan kira na Bintu ne daga Gimbiya Binta’’

Kafin Inna ta bata amsa, mahaifin Bintu ya fito a fusace, in da ya hau Inna da fad’a ‘’Yanzu ki na nuhin(nufin) wanga d’iya ta na nan ta na kwana(bacci) har k’arfe bakwai na safe ba ki tashe ta ba tsabagen lalacewa! Yagana anya kuwa?’’

Cikin sanyin murya Inna ta furta ‘’Ayi hakuri na ga jiya ta dawo shi ya sa...’’

‘’Yo to da hakurin ya mutu nawa ki ka biya kud’in sadaka?’’ Jin haka Inna ta ja bakinta ta yi shiru, ba ta ankara ba sai ganin Baba ta yi ya shige d’akin, haka kuma be fasa fad’an da ya ke ba, har ya iske Bintu ta yi d’ai-d’ai ta na baccin ta cikin kwanciyar hankali. Be yi la’akari da rabon da ya sa ta a ido watanni uku kenan ba, ya rufe ta da fad’a da zagi. Ita kuwa Bintu kamar a mafarki ta ke jin muryarsa, a hankali ta bud’e ido, ko da su ka had’a ido cikin magagin bacci ta furta ‘’Baba?’’

A fusace ya yi mata dak’uwa ‘’Baban ubanki! Hegiya kin saki la66a da su k'a66a ki na ta kwanan asara! Tashi maza ki wanke ido ki tahi babban gida!"

Nan da nan Bintu ta wartsake, ta na mai raribar hijabinta, ta ce ‘’Yi hakuri Baba, jiya na dawo ban ganka ba.....’
‘’Yo to ai gashi kin ganni, yar tselan uwa mai kama da kuliya’’

Ko a jikin Bintu haka ta fito Baba na biye da ita, dan kuwa idan da sabo ta saba, dan ba dan Baba shi ya haifeta ba da sai ta ce ya ma tsane ta ne gaba d’aya. Har yanzu mita Baba ya ke, ita dai Inna d’auke kan ta ta yi, ta shiga wasu sabgogin gaban ta. Baba ne ya ce da baiwa mai jiran Bintu ta je ta ce ga Bintun nan ta tafe. Ta na fad’in ‘’Madallah’’ ta kama hanyar ta tafi.

Buta Bintu ta d’auka ta kewaya bayi, da ta fito ta sa dakakken gawayi da gishiri ta wanke hakoran ta, sannan ta wanke fuska. Baba da ke tsaye gefe ya na jira ya ce ‘’Maza kama hanya ki yi gaba’’

‘’Malam na ce a bari ta yi karin kumallo ko?’’ Fad’in Inna cike da nuna damuwa’
‘’Kayya! Wani kari kuma Gimbiya ta yi kira? Ke rabu da ita, idan kin dawo kya yi karin, wuce ki tafi’’ Cyewar Baba.
Silifa ruwan d’orawa ta sanya a k’afar ta, har za ta fita Inna ta ce ta tsaya su tafi tare. Amma Baba ya ce babu wannan maganar, karshen ta ma ya yanke hukuncin raka Bintu da kan sa. Haka ya sa ta ta gaba, ya na biye da ita, duk wanda su ka gani a hanya sai ta tsaya sun gaisa da Baba, a haka har ya kai ta ga filin sukuwa, sanna ya juya ya koma gida.

Tafiyar Baba ke da wuya Bintu ta hangi Yerima Nuhu tare da tawagar sa bisa doki, ganin su ya sa Bintu d'aga k’afa ta na mai adduar Allah Ya sa kar su cimma ta, amma ina Allah bai amsa addu'arta ba, domin kuwa ganinta ya sa Yerima dukan bayan dokinsa da dorinar hannun sa a hankali, hakan ya sa dokin k’ara sauri haka tawagar ta shi wanda ya kunshi abokan sa guda hud’u, nan da nan sai ga su gaban Bintu su na mai tada k’ura yayinda su ke jan linzamin dawakan dan su sami su tsaya.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

ZUWA GA K'AWATA HYK, SAKON KI NA ARZIKI YA ISO GARE NI, NA KUMA CE AMEN HAR DA KE. NA GODE KWARAI, MADALLAH DA KE, SIDIYA CE KE MIKI FATAN ALKHAIRI🤝

©Khadija Sidi.....✍🏼

1⃣0⃣

*WAIWAYE ADON TAFIYA*

Wanene Sarki Sule Inuwa Magaji?

Shi ne Sarki na ishirin bisa gadan mulkin Sa’ayrasa. Ya hau kujerar mulki a shekara ta (1984), bayan Sarki Inuwa Magaji mai rasuwa, lokacin ya na da shekara arba’in a duniya. Allah ya azurta shi da ‘ya’ya goma sha takwas, ya birne takwas saura goma a raye, maza takwas, mata biyu.

Mata hud’u ya aura, uwargidansa marigayiya Hajja Fatima Abdu, wacce ta rasu bayan shekara d’aya da hawar sa mulki, wajan haihuwar Gimbiya Binta. Haka kuma ita ta haifawa sarki yara takwas, kasancewar auren saurayi da budurwa su ka yi da Mai martaba, ‘ya’yan ta su an manya duk da dai yawanci ba su yi tsahon rai ba dan sai da ta birne hud’u kafin ta samu masu zama guda hud’u. Yerima Inuwa mai shekara talatin, yayi aure har da yara uku, Yerima Nuhu shekara ishirin da biyar, Gimbiya K'amariyya mai shekara ishirin da haihuwa sai kuma Gimbiya Binta .

Sai kuma matar shi ta biyu Hajja Salame wacce ake kira Hajja Kilishi, ita Allah be nufe ta da haihuwa ba. Sai ta uku Hajja Maimunatu ana kiran ta Uwar fada, yaran ta biyu, Hassan da Hussain wanda su ke sa'annin Gimbiya K’amariyya sa kuma amaryar wacce ta ke kanwa ce gun Hajja Fatima Abdu, aka d’aura masa bayan rasuwar sa mai suna Masarriya, ana kiran ta da Inna Salti(wacce za ta haihu da yawa), yaran ta hud’u, duka maza. Sun had'a da Yerima Hamza wanda shi ne babba mai shekara goma sha uku, sai mai bin sa Yerima Abdallah dan shekara goma, na ukun Yerima Ahmadu, shekara takwas sai autan ta Yerima Nadir mai shekara biyar a duniya.

Kasancewar ‘ya’yan sa mata biyu kacal a duniya da kuma soyayyar da ya ke yiwa uwar su, ya d’auki san duniya ya d’aura ma su, musammam K’amariyya wacce kamar ta d’aya da mahaifiyar ta kamar kabo da kabo. Hakan shi ya zame babban rauni ga Sarki Sule.

***** ******
Sai da su ka shige tsaunika da duwatsu, suna mai ketare yankuna da dama ta sahara, kafin su hau mik'ak'k'iyar hanyar da za ta sada su da Sa’ayrsa. Ta babbar kofar wanda ake yiwa lak’ani da kofar Magaji Babba su ka shiga yanki. Rana ne sosai kwallewa a yankin daga gani ka san ruwa be sauka baw, kamar ma ruwan sama be sauka a yankin ba bana. Jama’ar gari kowa sabgar gaban sa ya ke, daga masu zuwa ko dawowa daga kasuwa, sai masu zuwa gona, mata wasu da goyo wasu da yara a hannu su na ta hidimar su, ya yara su ma ba a bar su a baya ba, su ma da na su sabgar irin ta yara.

Babban abun da Bintu ta lura da shi, shine rashin annushuwa da kuzari na jama’ar yankin, ba kamar yanda ta saba ganin jama’ar yankin cikin farin ciki da annashuwa ba.

‘’Shin ko dai akwai wani abu da ke faruwa wanda ba mu da masaniya akai?’’ Tambayar da ta ke yiwa kan ta kenan, amma gudun magana ya sa ta kasa kada baki ta tambayi sauran bayi ‘yan uwan ta, har su ka kai ga kofar fada.

Ta k’ofar gabas su ka shiga fada, wanda dama in dai iyalan sarki ne ta nan su ke shiga.

Nan da nan jama’ar fada su ka fito tarban Gimbiya, ciki har da k’annan Gimbiyar wato Yerima Hassan da Yerima Husaini, Yerima Abdallah da kuma Yerima Hamza. Murna da farin ciki gun su kuwa ba a cewa komai.

Ana cikin wannan yanayin ne Bintu ta fito ta, bayan ta d’au d’an akwatin k'arfen ta, ta ja gefe babu wanda ya lura da ita bare a damu da halin damuwa da ta ke ciki. Ganin Gimbiya ta fito, da sauri ta k’arasa cikin bayi yan uwan ta, in da su ka zube domin kai gaisuwa ga su Yerima, sannan bayi su ka taka mu su baya su ka shege izuwa fada.

Bintu na durk’ushe ba ta tashi ba ta ji an tab’a kafad’ar ta, a hankali ta d’aga ido, tuni murmushi ya maye fuskar ta yayin da ta tashi tsaye ta na mai rungume yayan ta Habibu. Cikin farin ciki ya ce ‘’Kauna(kanwa) mu na ta ke kewan ki, tin ba ma Inna ba, yo kawo akwaitin na ki mu tahi ko?’’

Saboda murna Bintu kasa magana ta yi, sai kawai mik’a masa akwaitin ta yi. Akwaitin ya d’auka, ya na ruke da hannun ta su ka wuce sashin su na bayi. A hanya ya ke tambayar ya yaga idanun ta sun yi jajur haka? Ta ce da shi idanun na ta ke ciwo shi ya sa. Ya ce da ita ta dai sha magani dai ko? Ya kara da Allah ya sauwake.

'Bangaran su na bayi b’angare ne mai d’auke da sashi-sashi na gidajen bayi. Gidan su Bintu wanda ya ke na uku cikin jerin gidajen bayi, gida ne ginin k’asa, mai d’auke da d’akuna uku da falo, sai kuma d’akin dafa abinci da kuma 6and'aki guda d’aya.

"Dakunan biyu a cikin falo su ke, na ukun kuma tsakar gida ya ke kusa da dak’in girki, in da 6and'aki ke daga can gefe daf da soro. Ba wani girma ne da tsakar gidan ba haka zalika d'akunan, idan ana zafi da kyar su ke iya bacci, musammam yanayi irin wanda su ke ciki a yanzu, ruwa be sauka a yankin ba. Falon na su kuma babu komai ciki daga daga ciminti sai tabarma.
Chapter 13 · 0% Book details