Sashe 12
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta na shiga mota ta juya da niyar komawa ta d’auk akwaitin na ta, Gimbiya ta tsiyar da ita ta hanyar daka mata tsawa ‘’gide ina kuma za ki?’’ dan a zatan ta wajan Aisar Bintu za ta. Ko da Bintu ta fad’a mata cewar akwatin ta za ta d’auko, minti gama kacal Gimbiya ta bata idan ba haka ba za ta taka zuwa Sa’ayrasa da k’afar ta. Hanyar da za ta kai ta ga d’akin na su Bintu ta kalla, ko zuwa bakin kofar b’angarn sai ya fi minti goma bare kuma ga hawa bene ga nauyin kaya. ‘’ki nan tsaye ne? idan kin fasa ma iya tafiya’’ furucin Gimbiya cike da tak’ama.
Cikin hanzari Bintu ta ce ‘ tuba na ke ran Gimbiya shi dad’e’’ kafin ta tafi da sauri, sai da ta tabbata ta wuce ganin su Gimbiya sannan ta arta a na kare. Ta na ji wasu na ‘’fad’in ku kauce ta fara gudun na ta na masifa’’ har dariya ake mata ita kuwa ba ta san suna yi ba. Haurawa ta yi ta d’auki akwaitin ta bisa kan ta. Ta fito daga sashin kwanan na su kenan kamar daga sama ta ji an d’auke ma ta akwatin daga kayin ta.
A tsorace ta juya sai ga Aisar sanye dai da shigar nan nasa, amma yau fara ya sa, idanun sa rufe da gilashi, hannun sa ruk’e da wata leda mai d’an girma cikin nuna damuwa ya ce ‘’wanga ya yiwa d’iya mace nauyi’’ cikin kokawa Bintu ta ce ‘’dan Allah ka yi min rai ka bani na tafi, aradun Allah minti goma kacal Gimbiya ta ba ni’’ maimakon ya bata, sai ma dad’a ruk’e akwaitin yayi kafin ya ce ‘’idan kuma ki ka k’ara fa? K’ak’a za ta yi?’
Idanun Bintu na mai kawo ruwa ta ce ‘’aradu tahiyar su za su yi su bar ni a nanniya (wallahi tafiya za su yi su bar ni a nan)’’ Aisar na mai murmushi ya ce ‘’idan su ka tahi shikenan sai na tahi da ke gidan mu hankali kwance’’ ganin za ta sa masa kuka ya ce ‘’shhh..wasa na ke mi ki’’ akwatin ya aje k’asa sannan ya ciro zoben hannun sa ya mik’a mata ya na mai fad’in ‘’kan ki tafi ga ajiya ta Bintu, ina so ki aje min duk sanda mu ka sake had’uwa zan kar6a’’
Cikin saurin ya bar ta tafi, ba tare da ta kawo komai cikin ran ta ba ta sa hannu ta karb’a ta na mai k’ok’arin cusa zuben cikin zanin ta,ya ce ‘’ah ah a yatsar ki na ke so ki saka, nan ya na iya fad’uwa’’ ba musu ta fara k’ok’arin zira zuben, duk da ya so ya mata yawa ta samu ya shiga yatsar tsakiyar hannun ta na dama. Ta yunk’ura za ta d’au akwatin kenan Aisar ya riga ta cikin zafin nama, ya wuce gaba abun sa, da sauri ta bi bayan sa ta na mai fad’in ‘’ Monsieur ka bani akwatin dan Allah’’ shiru ya mata, dake Aisar mutum ne mai kuzari, nan da nan su ka isa ga motocin Sa’ayrasa. Bintu sai karanto adduoin da ta koyo makarantar allo ta ke dan neman tsari daga masifar Gimbiya, dan ba ita kad’ai ba ma kallo da zund’e da ta sha wajan sauran d’alibai ma sai Allah, musammam yan aji shida da dama sun gama tsanar ta, yau ga Aisar Gaddafi Nur yayi dakon akwaitin d’yar bayi. Shi kuwa gogan na ta ko a jikin sa wai an mintsli kakkausa.
Suna isa ya sakar mata murmushin da ita kan ta Bintu ba ta san na menene ba, ita dai ta na ganin sabon salo kiran sallah da husir, kana ya ce ‘’wata motar Gimbiya za ta shiga’’ Bintu ta amsa da ‘’ai Gimbiya ta na cikin waccar motar’’ ta masa nuni ga motar da Gimbiya ke ce. Aisar ya kai kallan sa ga motar, ko da yayi ido hud’u da Gimbiya, duk da 6acin ran da ta shiga ganin Aisar d’auke da akwatin Bintu, sai da ta tsinci kan ta ta na mai sakarwa Aisar sakon murmushi. Yayi saurin maido da kallan sa ga Bintu ya na mai fad’in ‘’ba Gimbiyar ki na ke magana akai ba, Gimbiyar Aisar na ke nufi, wata motar za ki shiga?’’
Cike da mamaki Bintu ta amsa masa da ‘’iyye? Na’am? Ni Bintu?’’ kai ya girgiza mata, jiki a sanyaye ta masa nuni dai ga motar da Gimbiya ke ciki, kana ya ce da direba(driver) ya ce ‘’Aboki na bud’e min bayan motar na aje kayan ko’’ jin haka Bintu ta yi saurin fad’in ‘’waccar motar ta baya za a aje kayan’’
Aisar ya ce ‘’toh gidan gaba ko baya ina ki ke zama?’’ ta na hango Gimbiya ta na girgiza kai har da kwafa, ta na mai duban Bintu ta ce ‘’a juri kai zuga gabas, wataran ta zo da ruwa’’ maimakon Bintu ta bashi amsar sai kawai ta kai hannun ta ga murfin motar da niyar bud’ewa, yayi saurin tsaiyar da ita, ya b’ud’e da kan sa, Bintu ta shiga, ita kan ta ta san ta wuce gona da iri. Ledar ya aje bisa cinyar ta, ba tare da ya rufe motar ba ya ce da direban ya fito kai akwaitin Bintu cikin motar da ake ajewa. Direban ya so yi masa musu, amma ko da suka had’a ido da Aisar ya ga waye gaban shi tini ya fito yayi yanda aka saka shi.
Aisar ya ce ‘’ki gaida gida ki gaida yan gidan Bintu, sai kin ji daga gare ni’’ kai kawai Bintu ta iya gyad’a masa, yayin da ya mayar da murfin mota ya rufe. Direba ya dawo ya tada mota har su ka fita be dena kallan motar da Bintu ke ciki ba, ji ya ke kamar ya bi bayan su.
Da fitar su, ta baya ta ji Gimbiya ta kifa mata mari, ta na mai fad’in ‘’shegiyar kaya!dama wajan shi ki ke san zuwa sai da jiki na ya ban!’’ kuka Bintu ta saka, fad’i ta ke ‘’ki yi min rai Gimbiya, tuba na ke, ba wajen shi na je ba a hanya mu ka had’u, idan karya na kai arratta kashe ni’’
Tas! Ta dad’a kwashe ta da mari ‘’shi ne har da d’aukar d’an akurkin ki ko? Kai direba tsayar motan nan! Direba ya ja ya tsaya, sauran motocin ma tuni suka faka gefe guda ganin na Gimbiya ma ya faka. Ledar hannu Bintu ta fizge ta na bud’e, mayafai ne manya masu kyan gaske har guda goma. Tsaki Gimbiya Binta ta ja yayinda ta sauke gilashin motar ta na ji ta na gani ta wulga mayafan waje, kan idanun Bintu haka su ka sauka cikin ruwan sama da ya kwanta a gefen titi, sannan ta ce ‘’Direba mayar da d’iyar bayin nan cikin bayi sa’annin iyayen ta’’ Direba ya dubi Bintu da ke faman kuka ya ce ‘’yo to ai sai ki hito ko?’’
Bintu na k’ok’arin fitowa ta ji Gimbiya ta ce ‘’ke da wanga ecole har abada! aradu ma kuwa!’’ da ma dai ko ba ta fad’a ba Bintu ta san ta faru ta k’are ramamme ya zagi maye. Haka ta na mai fad’in ‘’ina tuba’’ amma Gimbiya ta mata kunne uwar shegu, yayinda direba ya raka Bintu izuwa motar bayi a wulak’ance. Nan su ka d’auki hanyar masarauta Bintu na mai bakin ciki da fad’uwar gaba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐪🐫
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen2⃣)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣1⃣
Bayan Bintu ta ci abinci, ta watsa ruwa, Inna ta shiga ta same ta kwance ta na hutawa. Ganin Inna ya sa ta tashi zaune, Inna na murmushi ta ce "Gide na aza kwana ki ke(na zaci bacci ki ke)’’
Kai Bintu ta girgiza mata, cike da farin cikin yau ga ta da Innarta, ta ce ‘’A falke na ke Inna (ido na biyu Inna)’’ Nan ta zauna kusa da ita in da ta fara mata tambayoyi game da makaranta kamar dai yanda ta saba. Jin Bintu ta ce komai lahiya lau, bai hana Inna fad’in ‘’Ki dai k’ara hakuri da takwarar ta ki, na ce dai lafiya lau ku ke zaune ko?’’
Da har Bintu za ta fad’a mata halin da ake ciki, sai ta fasa don kuwa ta san halin Inna da sa abu a rai, sai cewa ta yi ‘’Lahiya lumi.”
"Ngla zauro, Ala barraaz3( da kyau Allah ya yi albarka)" Fadin Inna ta na mai dafa kan Bintu. Bintu ba ta gushe ba ta yiwa Inna tambayar da ya tsaya cikin ranta, ta ce
‘’Inna me ke faruwa ne?’’ Kai Inna ta girgiza sannan ta ce ‘’Wannan annobar ta duk shekara ita ta sake bayyana Bintu.’’
Gaban Bintu ya fad’i ta na mai dafe k'irji ta ce ‘’Fari?’’(Annobar yunwa, sanadiyar k'arancin ruwan sama)
‘’Aradu ma kuwa, wanga ma ai tafi ta kowacce shekara, talakawa mu na cikin wani hali, dussa ma da za a bawwa awaki gagaran mu yake, hatsin da ki ka ga ina tankad’ewa na gidan sarki ne, Allah ya sa ya shigo ta hannuna, na sami dussar ko ba komai ma sami na karin kumallo, na dare kuma ma ci ragowar babban gida.’’ Cewar Inna.
‘’Innalillahi wainna ilaihi rajiun’’ Fad'in Bintu kenan yayinda zufa ya shiga keto mata. Inna na mai girgiza kai ta ce ‘’Abunda mu ke ta fad’a kenan ‘yar nan’’
kana Bintu ta ce ‘’Yo to Inna me zai hana mu nemi taimako wajan sauran masarautar? Ai na ga ba laifi k’asar mu dai akwai abinci ga taimakon juna’’
Inna ta ce ‘’Uhum ina ne ba a nema ba? Su ma ai sun gaji, yau da gobe ya wuce gaban wasa ai, ridda karya kuka tatsa’’ Zuciyar Bintu d’aya ta furta ‘’Fabarusa fa.....’’
Da sauri Inna ta doke bakinta, hannun Bintu bisa bakinta, Inna na mai zare ido ta ce ‘’Kul ashirni zanne(rufa min asiri), shiga uku takabar sarakuwa!(sirika) Kar ki sake ambatan yankin ga dan Allah, kin manta bakar gabar da ke tsakanin mu, ahir ba da ni ba saka lallen kaza!’’
Cikin hanzari Bintu ta ce ‘ tuba na ke ran Gimbiya shi dad’e’’ kafin ta tafi da sauri, sai da ta tabbata ta wuce ganin su Gimbiya sannan ta arta a na kare. Ta na ji wasu na ‘’fad’in ku kauce ta fara gudun na ta na masifa’’ har dariya ake mata ita kuwa ba ta san suna yi ba. Haurawa ta yi ta d’auki akwaitin ta bisa kan ta. Ta fito daga sashin kwanan na su kenan kamar daga sama ta ji an d’auke ma ta akwatin daga kayin ta.
A tsorace ta juya sai ga Aisar sanye dai da shigar nan nasa, amma yau fara ya sa, idanun sa rufe da gilashi, hannun sa ruk’e da wata leda mai d’an girma cikin nuna damuwa ya ce ‘’wanga ya yiwa d’iya mace nauyi’’ cikin kokawa Bintu ta ce ‘’dan Allah ka yi min rai ka bani na tafi, aradun Allah minti goma kacal Gimbiya ta ba ni’’ maimakon ya bata, sai ma dad’a ruk’e akwaitin yayi kafin ya ce ‘’idan kuma ki ka k’ara fa? K’ak’a za ta yi?’
Idanun Bintu na mai kawo ruwa ta ce ‘’aradu tahiyar su za su yi su bar ni a nanniya (wallahi tafiya za su yi su bar ni a nan)’’ Aisar na mai murmushi ya ce ‘’idan su ka tahi shikenan sai na tahi da ke gidan mu hankali kwance’’ ganin za ta sa masa kuka ya ce ‘’shhh..wasa na ke mi ki’’ akwatin ya aje k’asa sannan ya ciro zoben hannun sa ya mik’a mata ya na mai fad’in ‘’kan ki tafi ga ajiya ta Bintu, ina so ki aje min duk sanda mu ka sake had’uwa zan kar6a’’
Cikin saurin ya bar ta tafi, ba tare da ta kawo komai cikin ran ta ba ta sa hannu ta karb’a ta na mai k’ok’arin cusa zuben cikin zanin ta,ya ce ‘’ah ah a yatsar ki na ke so ki saka, nan ya na iya fad’uwa’’ ba musu ta fara k’ok’arin zira zuben, duk da ya so ya mata yawa ta samu ya shiga yatsar tsakiyar hannun ta na dama. Ta yunk’ura za ta d’au akwatin kenan Aisar ya riga ta cikin zafin nama, ya wuce gaba abun sa, da sauri ta bi bayan sa ta na mai fad’in ‘’ Monsieur ka bani akwatin dan Allah’’ shiru ya mata, dake Aisar mutum ne mai kuzari, nan da nan su ka isa ga motocin Sa’ayrasa. Bintu sai karanto adduoin da ta koyo makarantar allo ta ke dan neman tsari daga masifar Gimbiya, dan ba ita kad’ai ba ma kallo da zund’e da ta sha wajan sauran d’alibai ma sai Allah, musammam yan aji shida da dama sun gama tsanar ta, yau ga Aisar Gaddafi Nur yayi dakon akwaitin d’yar bayi. Shi kuwa gogan na ta ko a jikin sa wai an mintsli kakkausa.
Suna isa ya sakar mata murmushin da ita kan ta Bintu ba ta san na menene ba, ita dai ta na ganin sabon salo kiran sallah da husir, kana ya ce ‘’wata motar Gimbiya za ta shiga’’ Bintu ta amsa da ‘’ai Gimbiya ta na cikin waccar motar’’ ta masa nuni ga motar da Gimbiya ke ce. Aisar ya kai kallan sa ga motar, ko da yayi ido hud’u da Gimbiya, duk da 6acin ran da ta shiga ganin Aisar d’auke da akwatin Bintu, sai da ta tsinci kan ta ta na mai sakarwa Aisar sakon murmushi. Yayi saurin maido da kallan sa ga Bintu ya na mai fad’in ‘’ba Gimbiyar ki na ke magana akai ba, Gimbiyar Aisar na ke nufi, wata motar za ki shiga?’’
Cike da mamaki Bintu ta amsa masa da ‘’iyye? Na’am? Ni Bintu?’’ kai ya girgiza mata, jiki a sanyaye ta masa nuni dai ga motar da Gimbiya ke ciki, kana ya ce da direba(driver) ya ce ‘’Aboki na bud’e min bayan motar na aje kayan ko’’ jin haka Bintu ta yi saurin fad’in ‘’waccar motar ta baya za a aje kayan’’
Aisar ya ce ‘’toh gidan gaba ko baya ina ki ke zama?’’ ta na hango Gimbiya ta na girgiza kai har da kwafa, ta na mai duban Bintu ta ce ‘’a juri kai zuga gabas, wataran ta zo da ruwa’’ maimakon Bintu ta bashi amsar sai kawai ta kai hannun ta ga murfin motar da niyar bud’ewa, yayi saurin tsaiyar da ita, ya b’ud’e da kan sa, Bintu ta shiga, ita kan ta ta san ta wuce gona da iri. Ledar ya aje bisa cinyar ta, ba tare da ya rufe motar ba ya ce da direban ya fito kai akwaitin Bintu cikin motar da ake ajewa. Direban ya so yi masa musu, amma ko da suka had’a ido da Aisar ya ga waye gaban shi tini ya fito yayi yanda aka saka shi.
Aisar ya ce ‘’ki gaida gida ki gaida yan gidan Bintu, sai kin ji daga gare ni’’ kai kawai Bintu ta iya gyad’a masa, yayin da ya mayar da murfin mota ya rufe. Direba ya dawo ya tada mota har su ka fita be dena kallan motar da Bintu ke ciki ba, ji ya ke kamar ya bi bayan su.
Da fitar su, ta baya ta ji Gimbiya ta kifa mata mari, ta na mai fad’in ‘’shegiyar kaya!dama wajan shi ki ke san zuwa sai da jiki na ya ban!’’ kuka Bintu ta saka, fad’i ta ke ‘’ki yi min rai Gimbiya, tuba na ke, ba wajen shi na je ba a hanya mu ka had’u, idan karya na kai arratta kashe ni’’
Tas! Ta dad’a kwashe ta da mari ‘’shi ne har da d’aukar d’an akurkin ki ko? Kai direba tsayar motan nan! Direba ya ja ya tsaya, sauran motocin ma tuni suka faka gefe guda ganin na Gimbiya ma ya faka. Ledar hannu Bintu ta fizge ta na bud’e, mayafai ne manya masu kyan gaske har guda goma. Tsaki Gimbiya Binta ta ja yayinda ta sauke gilashin motar ta na ji ta na gani ta wulga mayafan waje, kan idanun Bintu haka su ka sauka cikin ruwan sama da ya kwanta a gefen titi, sannan ta ce ‘’Direba mayar da d’iyar bayin nan cikin bayi sa’annin iyayen ta’’ Direba ya dubi Bintu da ke faman kuka ya ce ‘’yo to ai sai ki hito ko?’’
Bintu na k’ok’arin fitowa ta ji Gimbiya ta ce ‘’ke da wanga ecole har abada! aradu ma kuwa!’’ da ma dai ko ba ta fad’a ba Bintu ta san ta faru ta k’are ramamme ya zagi maye. Haka ta na mai fad’in ‘’ina tuba’’ amma Gimbiya ta mata kunne uwar shegu, yayinda direba ya raka Bintu izuwa motar bayi a wulak’ance. Nan su ka d’auki hanyar masarauta Bintu na mai bakin ciki da fad’uwar gaba.
🐫🐪🐫🐪🐫🐪🐫
Copied By
HAYATU BABA ZUBAIRU
(admin
Hayat hausa novels
Hausa novels and fashion
Cool novel, makeup and kitchen1⃣
AND
Cool novel, makeup and kitchen2⃣)
WHATSAPP NO:
+2347039625239
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣1⃣
Bayan Bintu ta ci abinci, ta watsa ruwa, Inna ta shiga ta same ta kwance ta na hutawa. Ganin Inna ya sa ta tashi zaune, Inna na murmushi ta ce "Gide na aza kwana ki ke(na zaci bacci ki ke)’’
Kai Bintu ta girgiza mata, cike da farin cikin yau ga ta da Innarta, ta ce ‘’A falke na ke Inna (ido na biyu Inna)’’ Nan ta zauna kusa da ita in da ta fara mata tambayoyi game da makaranta kamar dai yanda ta saba. Jin Bintu ta ce komai lahiya lau, bai hana Inna fad’in ‘’Ki dai k’ara hakuri da takwarar ta ki, na ce dai lafiya lau ku ke zaune ko?’’
Da har Bintu za ta fad’a mata halin da ake ciki, sai ta fasa don kuwa ta san halin Inna da sa abu a rai, sai cewa ta yi ‘’Lahiya lumi.”
"Ngla zauro, Ala barraaz3( da kyau Allah ya yi albarka)" Fadin Inna ta na mai dafa kan Bintu. Bintu ba ta gushe ba ta yiwa Inna tambayar da ya tsaya cikin ranta, ta ce
‘’Inna me ke faruwa ne?’’ Kai Inna ta girgiza sannan ta ce ‘’Wannan annobar ta duk shekara ita ta sake bayyana Bintu.’’
Gaban Bintu ya fad’i ta na mai dafe k'irji ta ce ‘’Fari?’’(Annobar yunwa, sanadiyar k'arancin ruwan sama)
‘’Aradu ma kuwa, wanga ma ai tafi ta kowacce shekara, talakawa mu na cikin wani hali, dussa ma da za a bawwa awaki gagaran mu yake, hatsin da ki ka ga ina tankad’ewa na gidan sarki ne, Allah ya sa ya shigo ta hannuna, na sami dussar ko ba komai ma sami na karin kumallo, na dare kuma ma ci ragowar babban gida.’’ Cewar Inna.
‘’Innalillahi wainna ilaihi rajiun’’ Fad'in Bintu kenan yayinda zufa ya shiga keto mata. Inna na mai girgiza kai ta ce ‘’Abunda mu ke ta fad’a kenan ‘yar nan’’
kana Bintu ta ce ‘’Yo to Inna me zai hana mu nemi taimako wajan sauran masarautar? Ai na ga ba laifi k’asar mu dai akwai abinci ga taimakon juna’’
Inna ta ce ‘’Uhum ina ne ba a nema ba? Su ma ai sun gaji, yau da gobe ya wuce gaban wasa ai, ridda karya kuka tatsa’’ Zuciyar Bintu d’aya ta furta ‘’Fabarusa fa.....’’
Da sauri Inna ta doke bakinta, hannun Bintu bisa bakinta, Inna na mai zare ido ta ce ‘’Kul ashirni zanne(rufa min asiri), shiga uku takabar sarakuwa!(sirika) Kar ki sake ambatan yankin ga dan Allah, kin manta bakar gabar da ke tsakanin mu, ahir ba da ni ba saka lallen kaza!’’