← Book details Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 28

Sashe 11

Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Muryar Mary na rawa ta ‘’in ki na yiwa Allahu ki yi hakuri Madame , kwankwatsi (rantsuwa) na tuba, dan Allah kada ki yanke min suma ta’’ cike da mamaki ta ce ‘’yo ba ki so a yanke na ki shine ki yanke na wata, aradu kwal kwabo zan mi ki ma kuwa, Iya Dije ruk’e min hannun ta’’ ganin Iya Dije ta yo kan ta, ta saurin sauke hannayen ta k’asa, ta na ji ta na gani Malama ta sai ta almakashi bisa d’an gunjin ta, ta daidaici rabin gashin cikin hikimar raba kan gida biyu, ta fara cire na sama sama. Dake Malamar ma ta na fama da mugun ta, sai da ta karb’i sabuwar rezar hannun Iya Dije, ta kwashe rabin gashin Mary tas sannan hankalin ta ya kwanta.
Fuskar Mary ba k’aramin muni ta yi ba da kai rabi kwakwaido rabi kwal kabo, ko da yake dama yaya bare sarki ya aiko. Dan kunya da takaici ta kasa ko da motsi bare ta iya d’aga idanun ta ta kalli jama’a, d’alibai ba su fasa ihu da sowa ba, musammam da malamar ta ce ayiwa Marry ihu, su ka d’auka ‘’ihu dube ta kwakwaido da kwal kabo’’ Malam Hashim ne ya matso gaba, in da ya kira Shedigyal da Sikanti, ya had’a har maryam ya kwace kallabin muk’amin su, ya kuma jaddada hukunci mai tsanani ga duk d’alibar da aka k’ara kamawa da makami ba tare da kwakkwaran daliliba, ko da kuwa reza ne.

Farin ciki gun d’alibai be musaltuwa, dan kuwa kurace ta mutu, sun huta. Gimbiya kuwa tuni ta sha jinin jikin ta ganin yanda Aisar yayi ruwa yayi tsaki bisa ga lamarin, batun akwai wani abu tsakanin Bintu d’iyar bayi da Malam Aisar tun daga wajan ya fara shawagi tsakanin d’alibai. Har aka sallame su Mary ba ta iya tashi daga tsugunnan da ta yi ba, sai da yan aji shida su tada ita, nan ta saki kukan da dama ya tsaya k’ark’ashin mak’oshin ta, ba ta ta6a jin ta tsani kan ta ba kamar ranar ba. Ko da ya ke ba ita kad’ai ba duka yan aji shidan ma hakan ta ke. Sauran d’aliban kuwa yau ta ke sallah, dan kuwa abin da aka yiwa Bintu gaba ta kai dan sun sami sakewa da wa tayawa, a ranar Bintu ta yi farin jini sai san barka ake yi mata, hatta Gimbiya a ranar sai da ta sarara mata.

🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
​FIKRA WRITER'S ASSOCIATION​

🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪

ZUWA GA MASOYA "BINTU 'DIYAR BAYI" INA MAI NEMAN AFUWAN KU NA JINKIRIN SHAFI NA GABA DA ZA A SAMU, HAR ZUWA JUMA'A SABODA WANI UZIRI BABBA DA YA SHAFI WANI KARATUN DA NA KE. MADALLAH DA KU. SIDIYA CE KE MU KU FATAN ALKHAIRI🤝

©Khadija Sidi.....✍🏼

0⃣9⃣

Ranar da su ka gama jarabawa da yammaci, ana gobe za su tafi gida, Gimbiya Binta ta ce da Bintu ta raka ta wajan Aisar, dan ta ga idan su na tare ne kad’ai ya ke d’an sakar mata fuska. Sanye ta ke cikin doguwar riga ta alfarma kalar ja, dake Gimbiyar fara ce ba karamin kar6ar ta kalar ta yi ba, ita kan ta Bintu sai da ta yaba da kyawun Gimbiya cikin ran ta. Bintu kuwa kayan su na bayi ne jikin ta, kan ta tufke da kallabi, jin Gimbiya ta ce za su gun Aisar ya ta ware kallabin dan ya dan rufe mata jiki, amma duk da haka iya ka wuyar ta ya ya tsaya, gashi ita ba mayafi gare ta ba.

Gimbiya tafe Bintu na biye da ita ba su zame koina ba sai ofishin malamai. Malaman duka ba sa nan, daga Aisar sai wani malami da su ke kira Malam Sunusi, shi ma d’in su na shiga ya na fita. Malam Aisar da ke zaune bisa kujera ga teburi gaban sa ya na rubuce rubuce, sanye cikin wannan shigar ta sa dai, ko da ya d’aga ido ya ga su Bintu sai ya dakatar da rubutun da ya ke ya na mai aikawa Bintu murmushi. Ita kuwa ta kau da kai karda Gimbiya ta gani ta shiga uku.

‘’assalama’alaikum warahamatullah’’ sallamar Gimbiya kenan gare shi, ya amsa da ‘’wa’alaikum salam’’ Bintu kamar munafuka sai 6uya ta ke bayan Gimbiya ma sallamar ta masa a tak’aice, ya amsa ya na mai k’arawa da ‘’Bintun Sa’ayrasa, ya ki ke 6uya ne, fito sarari mana’’ Gimbiya ta juyo ta watsa mata harara. Jiki a sanyaye, kan ta sunkuye Bintu ta fito sarari. A sannan Malam Aisar ya lura da shigar da ta yi, sai dai duk sanda ya ke ganin ta da irin shigar be tab’a ganin ta sa riga k’arama wacce ta kama ta kamar ta yau ba, gashi zani ne d’aure jikin ta kuma ya fi fitar da surar mace, dad’in dad’awa kuma gashi Bintu ba kad’an ba duk da dai yarinya ce.

Nan da nan su ka nemi fara’ar da ke fuskar Aisar su ka rasa, har sai da Bintu ta tsargu ta d’an ja da baya, Aisar na mai d’auke kai da barin kallan ta ya ce ‘’dole ki 6uya mana, tin da kin hito(fito) yawo ba mayafi da irin wanga shigar!’’ Bintu ta sunkuyar da kai ta na mai tunanin ko dai ya manta da tsayuwar Gimbiya a wajan ne ko me? Allah ya sa kar ya ja mata jaraba. Gimbiya na kallan ikon Allah cikin ran ta fad’i ta ke ‘’aikin banza kyaramuwa tsaftar yaye!’’, Aisar be gushe ba ya k’ara da ‘’kul kar ki k’ara hita(fita) haka ko da a masarautar ku ne!’’ Bintu ta amsa da ‘’toh’’

Gimbiya ya ce ta ce "Monsieur Ina wuni’’ ba tare da ya kalle ta ba ya ce ‘’lafiya’’ ganin haka ta ce da Bintu ‘’Gide hita (fita) waje ki yi jira na....’’ be jira amsar Bintu ba yayi saurin katse Gimbiya ta hanyar fad’in ‘’idan kin hita ki wuce d’aki kar ki tsaya waje da wanga shiga ta ki, idan kin gama kya same ta ca’’
Cikin sauri Bintu ta bar wajan ta na mai hamdalar ceton ta da Allah yayi. Bayan fitar Bintu maimakon ya tsaya ya saurari Gimbiya sai ya cigaba da rubuce rubucen sa, kamar be ma san ta na wajan ba. Kamar za ta juya sai dai ta d’aure ta ce ‘’Malam gobe za mu koma gida’’ ba tare da ya d’ago ya kalle ta ba amsa mata ‘’sai aka yi yaya?’’ Gimbiya ta d’an cije le6e kafin ta ce ‘’dama zuwa na yi na maka sallama, na kuma gayyace ka zuwa masarautar mu idan da hali’

‘’na gode da sallamar, sai dai masarautar ta ku ce ban da lokaci’’ amsar da ya bata kenan. Kana Gimbiya ta dad’a gwada sa’ar ta ta hanyar fad’in ‘’dama wai ina nufin in ka sami lokaci.....’’
‘’ban da wannan lokacin’’ ya katseta ya na mai kafe ta ido. Ganin haka Gimbiya ta cije le6e ta na mai hamdalar korar Bintu da ta yi da yanzu gaban ta Aisar zai mata wannan cin fuskar. Fuuu ta juya ta fice ba tare da ta sake tankawa ba. Sai da ya ga ta fita ya aja rubutun ya na mai jan tsaki, takaicin sa na ganin ta na masa yawo da Bintu haka babu mayafi, ko wani kare da biri ya kalla! ‘’ba dan karancin shekarun wangad’iya ba, wallahi ba d’iyar bayi, ko d’iyar bola ce sai na aure ta! Amma ba komai lokaci ne ni Aisar mai hakurin jira ne’’ furicin Aisar kenan azahiri ya na mai jadda batun kawo kanwar sa Maryam makarantar ko ba komai ta ke saka Bintu a hanya. Tsaki ya sake ja ya na mai tura rubutun da ya ke gefe dan kuwa lamari in dai akan Bintu ne ya na jagula masa lissafi.

Komawar Gimbiya Binta d’aki kan Bintu ta sauke takaicin ta, laifukan na Bintu da yawa ciki har da ta na sane ta bita gun Aisar babu mayafi tsabagen ta na so ta yi masa tallar jikin ta, an fad’a mata shi d’an iska ne? Ta ji dad’in yanda ya yiwa Bintu kurar kare, da kuma ta ce ta jira ta waje shi ne ta bi umarnin uban ta ta koma d’aki.

Aiki tuk’uru ta saka ta wanda tun da Bintu ta zo duniya ba ta tab’a yin irin shi ba, hatta kayan ta da ke wanke a goge sai da ta sa Bintu dad’a wankewa da guga, dare yayi kuma ta tura ta lungu cikin sauro, nan Bintu ta kwana ta na mai adduar Allah ya sa iya haka hukuncin Gimbiya ya tsaya, ba za ta aiwatar da alkawarin sakawa a cire ta daga makarantar ba.

Washagari da ruwan sama aka tashi, motocin Sa’ayrasa na d’aya daga cikin motocin da su fara isowa. Sai da ruwa ya d’an tsaya sannan bayi da fadawa su ka taimakawa Bintu wajan kwasar kayan Gimbiya, har ya rage akwaitin karfen Bintu kad’ai ya rage a d’akin. Ita kuwa Gimbiya yar sarki mai dole kuma ta na jira a take mata baya zuwa mota, haka Bintu ta na ji ta na gani ta bar akwatin na ta su ka takawa Gimbiya.
Chapter 11 · 0% Book details