Sashe 20
Bintu Diyar Bayi Ce Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baba na mai duban ta ya saki murmushin takaici, kana ya ce
‘’ke kuma d’iyar wacece? Ko in ce ke wacece a Masarautar nan da ga ke har d’iyar ta ki?’’
Inna ta yi shiru, ganin haka Baba ya k'ara
'’shirun da ki ka yi ya tabbatar min da kin tuna ashefa ku bayi ne, dan haka ba ku da ‘yanci, ki ma godewa Allah da ya sa amrar da ita ya ce zai yi ba bada ita zai yi sadaka ko sad’aka ba, gide ke dai kin cika butulu. Toh ki saurare ni da kyau gobenan za a zo a tafi da Bintu ga babban gida, hallo dangin ki d’aya ba a yarda kin shedawa ba, yo to ina bayi ina wasu dangi ma in ban da ba'a"
Kuka Inna ta saka ta na fad’in ‘’wannan zalinci da ke shirin aikata min da wanga yarinya Allah shi isar mana’’
Ciki Baba ya shige kafin ya lek’o da kan sa ta assabari ya furta ‘’je ki tari Magajin Gabasawa ki sheda masa, yo to ba ni na kar zoman ba, rataya aka bani’’
Ita kuwa Bintu da ke jiyo su daga d'aki zuciya ne kad'ai ba ta had'iya ba, tunani ta ke ina ma Aisar ya na kusa ya kawo ma ta d'oki yanda ya [truncated by WhatsApp]®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣8⃣
Kamar dai yanda Baba ya ce, da sassafe sai ga Jakadiya da amintaccin bayin Hajja Kilishi sun dokowa Inna sammako. Dan takaici Inna d’auke kan ta yi dan kuwa ta kasa bud’e baki ta ce da Bintu ta fito ta bisu.
Tun da Bintu ta ji sallamar su ta shige bayan kofa ta yi zaman ta, duk da ta ji buk’atar Jakadiya amma k’yememe ta k’i fitowa. Ana haka Baba ya fito ya rufe Inna da fad’a
‘’Magajin Gabasawan za ki yi wa musu ko kuwa Jakadiya? Iye Yagana? Gide ban san tsaurin idanu fa! Yo to yau ko ke Magajin Gabasawa ya ce zai aura sauki zan yi bare ma wanga d’iya, aikin banza aikin hofi! Ta na ina wai? Gide Bintu hito ki bi su in ba haka ba ina make ke! kwankwatsi ma kuwa!’’
Jakadiya na murmushi ta ce
"Mahuta bi su a hankali, ai tsakanin uwa da d’iya sai Allah bare kuma ace za a raba su rana a tsaka, bi su a sannu Mahuta, in ban da ke da abin ki Uwar bayi wanga lamari ai alheri ne aka yiwa d’iyar ki, wanga abu abin san barka?’’
Idan Inna ta tanka ko shakka babu dutse ma ya tanka, ganin haka Baba ya wuce su izuwa d’akin Bintu, ya tadda ita bayan kofa ta had’a zufa da hawaye. Fad’a ya hauta da shi, ta in da ya ke shiga ba ta nan ya ke fita ba. Amma kyememe Bintu ta k’i motsawa bare ta fito. Aikuwa da Baba ya fusata sai ya hauta da zagi, jin haka Inna ta shige d’akin da sauri dan ta san daga nan kuma abun da zai biyu baya.
Ilekuwa shigar ta kenan ta ga Baba ya d’aga hannu ya na shirin kaiwa Bintu bugu, nan da nan ta shiga tsakani, ta ce
‘’haba Malam! Ai ka ji tsoran Allah abin ga ai sai yayi yawa maye da hauka!’’
Nan fad’an Baba ya koma kan Inna, ai lalle Inna ke d’aurewa Bintu, dan haka zai fita ya dawo, in dan ya dawo ya ga Bintu gidan nan sai na lahira ya fita jin dad’i. Dan masifa da bambami ko sallama be yiwa su Jakadiya ba ya sa kai ya fice ya na kumfar baki.
Bayan fitar sa Inna ta ja hannun Bintu su ka fito tsakar gida. Inna na mai duban ta ta ce
‘’Bintu idan har ni na haife ki, toh na baki umarni ki bi su ku tahi Babban gida’’
Bintu na jin haka ta zube k’asa, hannayen ta biyu ta sa ta ruk’o k’afar Inna ta na fad’in
‘’Inna na tuba, Inna ki gafarce ni, Inna ki min afuwa, Inna kar ki ce na bisu, Inna kar ki yarda a raba ni da ke, kwankwatsi na dena 6ata mi ki rai, idan na k’ara aratta kashe ni’’
Inna na mai janye k’afafun ta daga ruk’on da Bintu ta yi mata ta ce
‘’na yafe ki duk da ba ki ta6a sa6a min ba, ke d’iya ce ta gari, dan haka ki sa Allah a ran ki shi ne kad’ai ka iya mi ki, tashi ki bisu, Allah shi fisshe ki alkairi...’’
Ta na gama fad’ar haka ta shige ciki ta na hawaye. Nan fa Bintu kuka har da birgima. Su Jakadiya su na nan suna gani sarautar Allah duk da dai su ma kukan na Bintu ya so ya d’an ta6a su.
Habibu ne ya shigo, ganin abin da ke faruwa ya shiga rarrashin Bintu, har ya samu ta yi shiru. Ya ce da su Jakadiya su yi gaba gasu nan biye da su, bara ya had’o kayan Bintu. Jakadiya ta ce ah ah ba a bukata, ita d’in ta kad’ai ake buk’ata.
Gaba su ka yi, hannun Bintu ruk’e da na Habibu, su na tafe ya na bata baki da nasiha har su ka isa kofar Babban gida. Nan ma Bintu ta ce ba ta san zance ba, Habibu be isa ya koma ya bar ta gun su Jakadiya ba. Jakadiya ta fusata ta hau Bintu da fad’a
‘’yau ina ganin walele gi6in takwaru! Gaskiya ne komai girman d’an mara kabo be isa aure ba! 'Yar tusa wacce ba ta san arziki ba! Ki na baiwa d’iyar bayi har kya wa mutane kwawarniya shiga rumbun k’ore, yo to sai ki ma Babban Bijimi musu da kwarnato in ya so a tsire ki ma ga me asara!’’
Bakin Bintu na rawa, ta saki hannun Habibu, wanda d’acin maganar Jadiya ya sa shi juyawa da sauri dan gudun kar ya maida mata ya jawowa Bintu da ma gidan su baki d’aya, ya na jiyo Jakadiya na masife Bintu yayinda ta ke hankad’a kafad’ar ta zuwa ciki, babu yanda zai yi haka ya tafi ba tare da ya sake ko waiwaye ba.
'Dakin Jakadiya aka aje Bintu, nan ta sha kukan ta, ta k’oshi dan kan ta ta yi shiru sai ajiyar zuci kawai.
Jakadiya ta shigo kana ta ce ta saka mayafi ki biyo ta, Babban bijimi na jiran zuwan su. Kallabin ta ta ware ta yafa bisa kan ta, babu musu dan kuwa taji tsoran maganar Jakadiya na za a tsire ta, ta bi bayan Jakadiya ba su zame koina ba sai turakar sarki.
In da Jakadiya ta tsaya daga waje, Bintu ta shiga daga ciki. Nan ta tadda sauran ilayan Sarki. Gimbiya Binta ba ta fasa watsawa Bintu kallan wuk’anci ba, ita kuwa Inna Salti tsabar tausayin Bintu ne cikin ran ta. Yarima Nuhu kuwa Allah kad'ai ya san tashin hankalin da ya shiga, musammam yanzu da ya ga Bintu gaban Sarki, babu makawa ya na ji yana gani Bintu za ta si6ice ma sa. Tin shigowar ta ya sa saka idanu akan ta, k’irik’iri be damu da ba shi kad’ai ne ba, bare ya damu da fassarar da za a iya masa. Ita kan ta Gimbiya Binta ta lura da irin kallan da ya kewa Bintu, har zunguran K'amariyya ta yi dan ita ma ta ganewa idon ta, bare kuma su Hajja Kilishi har da murmushin mugunta, dan kuwa ta k’i jinin Yarima Nuhu.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣9⃣
Muryar Bintu a shak’e tsabar kukan da ta yi ta kai gaisuwar ta ga Sarki. Hankali kwance, idan Sarki ya lura da sauyin yanayin da aka samu game da Bintu tsakanin ranar da ta fara zuwa gareshi da kuma zuwanta a yau, bai nuna ba don kuwa ko a jikinsa ya amsa, kafin ya k’ara da
‘’Masarautar mu na godiya ga wanga d’iya ta arziki, kasancewarki baiwa, mun baki ‘yanci, mun ‘yanta ki a yau kin tashi daga baiwa kin zama d’iya mai ‘yanci...’’
A firgice Gimbiya Binta ta kai kallonta ga Sarki ta na mai fiddo ido waje dan kuwa ba ta yi zato ba, kar dai danasani za ta yi, abun da ya fara zuwa zuciyarta kenan yayinda gaban ta ke dukan uku uku. Haka ma kowa na wajan ke kallan Bintu, wacce ta rasa me za ta yi, murna za ta yi na samin ‘yancin rayuwar ta bayan shekara goma sha biyar ta na baiwa, ko kuwa kuka za ta yi ta tashi daga baiwa, amma iyayenta na nan a bayi, tabbas ta tabbata d’iyar bayi. Hawaye ne d’aya bayan d’aya ke gangarowa daga idanun ta, murya na kakkarwa ta ke fad’in ‘’Godiya na ke ranka shi dad’e, godiya na ke Allah shi ja da ran Sarki, Alkhairin Allah ya tabbata a gare Mai Martaba’’
Yarima Nadir da ke jikin Inna Salti ne ya ce " Inna Salti me ya sa Bintu ta ke kuka?"
Hannun Inna Salti bisa le6enta ta amsa da
"Shhhh"
Wato ya yi shiru, shirun ko yayi.Yarima Nuhu wanda shi kansa ya rasa shin wai me ya ke ji a lokacin ji yayi kamar ya isa ga Bintu ya sa hannu ya share mata hawayen idanunta, ji ya ke kamar ya rok’i Sarki a bar ma sa Bintu, ko da kuwa shi ne abu na k’arshe da zai tambaya gun Sarki ya amsa masa. Yau ga Bintun arziki an zama ‘yantacciya, wannan fa shi ake kira ga k’oshi fa ga kuma kwanan yunwa.
‘’ke kuma d’iyar wacece? Ko in ce ke wacece a Masarautar nan da ga ke har d’iyar ta ki?’’
Inna ta yi shiru, ganin haka Baba ya k'ara
'’shirun da ki ka yi ya tabbatar min da kin tuna ashefa ku bayi ne, dan haka ba ku da ‘yanci, ki ma godewa Allah da ya sa amrar da ita ya ce zai yi ba bada ita zai yi sadaka ko sad’aka ba, gide ke dai kin cika butulu. Toh ki saurare ni da kyau gobenan za a zo a tafi da Bintu ga babban gida, hallo dangin ki d’aya ba a yarda kin shedawa ba, yo to ina bayi ina wasu dangi ma in ban da ba'a"
Kuka Inna ta saka ta na fad’in ‘’wannan zalinci da ke shirin aikata min da wanga yarinya Allah shi isar mana’’
Ciki Baba ya shige kafin ya lek’o da kan sa ta assabari ya furta ‘’je ki tari Magajin Gabasawa ki sheda masa, yo to ba ni na kar zoman ba, rataya aka bani’’
Ita kuwa Bintu da ke jiyo su daga d'aki zuciya ne kad'ai ba ta had'iya ba, tunani ta ke ina ma Aisar ya na kusa ya kawo ma ta d'oki yanda ya [truncated by WhatsApp]®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣8⃣
Kamar dai yanda Baba ya ce, da sassafe sai ga Jakadiya da amintaccin bayin Hajja Kilishi sun dokowa Inna sammako. Dan takaici Inna d’auke kan ta yi dan kuwa ta kasa bud’e baki ta ce da Bintu ta fito ta bisu.
Tun da Bintu ta ji sallamar su ta shige bayan kofa ta yi zaman ta, duk da ta ji buk’atar Jakadiya amma k’yememe ta k’i fitowa. Ana haka Baba ya fito ya rufe Inna da fad’a
‘’Magajin Gabasawan za ki yi wa musu ko kuwa Jakadiya? Iye Yagana? Gide ban san tsaurin idanu fa! Yo to yau ko ke Magajin Gabasawa ya ce zai aura sauki zan yi bare ma wanga d’iya, aikin banza aikin hofi! Ta na ina wai? Gide Bintu hito ki bi su in ba haka ba ina make ke! kwankwatsi ma kuwa!’’
Jakadiya na murmushi ta ce
"Mahuta bi su a hankali, ai tsakanin uwa da d’iya sai Allah bare kuma ace za a raba su rana a tsaka, bi su a sannu Mahuta, in ban da ke da abin ki Uwar bayi wanga lamari ai alheri ne aka yiwa d’iyar ki, wanga abu abin san barka?’’
Idan Inna ta tanka ko shakka babu dutse ma ya tanka, ganin haka Baba ya wuce su izuwa d’akin Bintu, ya tadda ita bayan kofa ta had’a zufa da hawaye. Fad’a ya hauta da shi, ta in da ya ke shiga ba ta nan ya ke fita ba. Amma kyememe Bintu ta k’i motsawa bare ta fito. Aikuwa da Baba ya fusata sai ya hauta da zagi, jin haka Inna ta shige d’akin da sauri dan ta san daga nan kuma abun da zai biyu baya.
Ilekuwa shigar ta kenan ta ga Baba ya d’aga hannu ya na shirin kaiwa Bintu bugu, nan da nan ta shiga tsakani, ta ce
‘’haba Malam! Ai ka ji tsoran Allah abin ga ai sai yayi yawa maye da hauka!’’
Nan fad’an Baba ya koma kan Inna, ai lalle Inna ke d’aurewa Bintu, dan haka zai fita ya dawo, in dan ya dawo ya ga Bintu gidan nan sai na lahira ya fita jin dad’i. Dan masifa da bambami ko sallama be yiwa su Jakadiya ba ya sa kai ya fice ya na kumfar baki.
Bayan fitar sa Inna ta ja hannun Bintu su ka fito tsakar gida. Inna na mai duban ta ta ce
‘’Bintu idan har ni na haife ki, toh na baki umarni ki bi su ku tahi Babban gida’’
Bintu na jin haka ta zube k’asa, hannayen ta biyu ta sa ta ruk’o k’afar Inna ta na fad’in
‘’Inna na tuba, Inna ki gafarce ni, Inna ki min afuwa, Inna kar ki ce na bisu, Inna kar ki yarda a raba ni da ke, kwankwatsi na dena 6ata mi ki rai, idan na k’ara aratta kashe ni’’
Inna na mai janye k’afafun ta daga ruk’on da Bintu ta yi mata ta ce
‘’na yafe ki duk da ba ki ta6a sa6a min ba, ke d’iya ce ta gari, dan haka ki sa Allah a ran ki shi ne kad’ai ka iya mi ki, tashi ki bisu, Allah shi fisshe ki alkairi...’’
Ta na gama fad’ar haka ta shige ciki ta na hawaye. Nan fa Bintu kuka har da birgima. Su Jakadiya su na nan suna gani sarautar Allah duk da dai su ma kukan na Bintu ya so ya d’an ta6a su.
Habibu ne ya shigo, ganin abin da ke faruwa ya shiga rarrashin Bintu, har ya samu ta yi shiru. Ya ce da su Jakadiya su yi gaba gasu nan biye da su, bara ya had’o kayan Bintu. Jakadiya ta ce ah ah ba a bukata, ita d’in ta kad’ai ake buk’ata.
Gaba su ka yi, hannun Bintu ruk’e da na Habibu, su na tafe ya na bata baki da nasiha har su ka isa kofar Babban gida. Nan ma Bintu ta ce ba ta san zance ba, Habibu be isa ya koma ya bar ta gun su Jakadiya ba. Jakadiya ta fusata ta hau Bintu da fad’a
‘’yau ina ganin walele gi6in takwaru! Gaskiya ne komai girman d’an mara kabo be isa aure ba! 'Yar tusa wacce ba ta san arziki ba! Ki na baiwa d’iyar bayi har kya wa mutane kwawarniya shiga rumbun k’ore, yo to sai ki ma Babban Bijimi musu da kwarnato in ya so a tsire ki ma ga me asara!’’
Bakin Bintu na rawa, ta saki hannun Habibu, wanda d’acin maganar Jadiya ya sa shi juyawa da sauri dan gudun kar ya maida mata ya jawowa Bintu da ma gidan su baki d’aya, ya na jiyo Jakadiya na masife Bintu yayinda ta ke hankad’a kafad’ar ta zuwa ciki, babu yanda zai yi haka ya tafi ba tare da ya sake ko waiwaye ba.
'Dakin Jakadiya aka aje Bintu, nan ta sha kukan ta, ta k’oshi dan kan ta ta yi shiru sai ajiyar zuci kawai.
Jakadiya ta shigo kana ta ce ta saka mayafi ki biyo ta, Babban bijimi na jiran zuwan su. Kallabin ta ta ware ta yafa bisa kan ta, babu musu dan kuwa taji tsoran maganar Jakadiya na za a tsire ta, ta bi bayan Jakadiya ba su zame koina ba sai turakar sarki.
In da Jakadiya ta tsaya daga waje, Bintu ta shiga daga ciki. Nan ta tadda sauran ilayan Sarki. Gimbiya Binta ba ta fasa watsawa Bintu kallan wuk’anci ba, ita kuwa Inna Salti tsabar tausayin Bintu ne cikin ran ta. Yarima Nuhu kuwa Allah kad'ai ya san tashin hankalin da ya shiga, musammam yanzu da ya ga Bintu gaban Sarki, babu makawa ya na ji yana gani Bintu za ta si6ice ma sa. Tin shigowar ta ya sa saka idanu akan ta, k’irik’iri be damu da ba shi kad’ai ne ba, bare ya damu da fassarar da za a iya masa. Ita kan ta Gimbiya Binta ta lura da irin kallan da ya kewa Bintu, har zunguran K'amariyya ta yi dan ita ma ta ganewa idon ta, bare kuma su Hajja Kilishi har da murmushin mugunta, dan kuwa ta k’i jinin Yarima Nuhu.
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
®
✏📖
FIKRA WRITER'S ASSOCIATION
🐪🐫BINTU 'DIYAR BAYI CE!
🐪🐪🐫🐪
🐪🐫🐪🐫🐪🐫
🐪🐫🐪🐫🐪🐫🐪
GARGA'DI
KUNGIYA MAI SUNA A SAMA, BATA YARDA WANI KO WATA YA MAYAR DA DUK WANI LABARI MAI 'DAUKE TAMBARIN SUNAN TA IZUWA DOCUMENT BA, YIN HAKA KARYA DOKA NE, WANDA HAKAN KA IYA JAWO YANKEWAR LABARIN. DAN ALLAH MU KIYAYE.
©Khadija Sidi.....✍🏼
1⃣9⃣
Muryar Bintu a shak’e tsabar kukan da ta yi ta kai gaisuwar ta ga Sarki. Hankali kwance, idan Sarki ya lura da sauyin yanayin da aka samu game da Bintu tsakanin ranar da ta fara zuwa gareshi da kuma zuwanta a yau, bai nuna ba don kuwa ko a jikinsa ya amsa, kafin ya k’ara da
‘’Masarautar mu na godiya ga wanga d’iya ta arziki, kasancewarki baiwa, mun baki ‘yanci, mun ‘yanta ki a yau kin tashi daga baiwa kin zama d’iya mai ‘yanci...’’
A firgice Gimbiya Binta ta kai kallonta ga Sarki ta na mai fiddo ido waje dan kuwa ba ta yi zato ba, kar dai danasani za ta yi, abun da ya fara zuwa zuciyarta kenan yayinda gaban ta ke dukan uku uku. Haka ma kowa na wajan ke kallan Bintu, wacce ta rasa me za ta yi, murna za ta yi na samin ‘yancin rayuwar ta bayan shekara goma sha biyar ta na baiwa, ko kuwa kuka za ta yi ta tashi daga baiwa, amma iyayenta na nan a bayi, tabbas ta tabbata d’iyar bayi. Hawaye ne d’aya bayan d’aya ke gangarowa daga idanun ta, murya na kakkarwa ta ke fad’in ‘’Godiya na ke ranka shi dad’e, godiya na ke Allah shi ja da ran Sarki, Alkhairin Allah ya tabbata a gare Mai Martaba’’
Yarima Nadir da ke jikin Inna Salti ne ya ce " Inna Salti me ya sa Bintu ta ke kuka?"
Hannun Inna Salti bisa le6enta ta amsa da
"Shhhh"
Wato ya yi shiru, shirun ko yayi.Yarima Nuhu wanda shi kansa ya rasa shin wai me ya ke ji a lokacin ji yayi kamar ya isa ga Bintu ya sa hannu ya share mata hawayen idanunta, ji ya ke kamar ya rok’i Sarki a bar ma sa Bintu, ko da kuwa shi ne abu na k’arshe da zai tambaya gun Sarki ya amsa masa. Yau ga Bintun arziki an zama ‘yantacciya, wannan fa shi ake kira ga k’oshi fa ga kuma kwanan yunwa.