Sashe 9
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye na share hawayena na ce.
“Ta daɗe tana complain cewa ƙirjinta yana ciwo, to duk lokacin da abin ya tasar mata sai inzo in sayi mata magani ko nan ko kuma wani wuri in bata tasha, to yau dai bama nan ko da muka dawo kuma mun cimmata a haka”
Nidai ganin nayi ya ɗauko wani abu ya ɗaura mata a hannun ta sannan ya saka wani a kunne bayan ya gama. Ya kalle ni yace min hawan jini ne da ita kuma ya hau sosai fiye da ƙima.
Cikin tsantsar mamaki ni da Nuhaira muka haɗa baki wurin kiran.
“Hawan Jini likita?”
Cikin kuka na sake cewa.
“Hawan jini ta yaya? Wane irin hawa jini dan Allah, muna zaune lafiya”
Mutumin yace.
“While, ba abin mamaki ba ne ai, musamman idan akwai wata damuwa tare da ita tana yawan tunani da rashin samun ishashshen bacci, amma...”
Sai ya juya ya hahhaɗo magunguna ya bani na kusan dubu goma sha ɗaya.
A nan ya buɗe ya bata maganin, sannan yace
“idan akwai abinda yake saka ta damuwa kuyi ƙoƙari ku ɗauke mata hankali a kai, ta riƙa samun bacci yadda ya kamata tana cin abinci mai kyau, in sha Allah zata ji sauƙi”
Daga haka na cewa Nuhaira taje gida ta ɗauko masa kuɗin shi, bayan ta dawo muka koma gida, kafin shiga bacci har mun samu taji sauƙi domin har ta tashi tayi Sallah taci abinci.
Washe gari bayan mun gama sallar Asuba muka je muka gaishe ta nayi sauri na haɗa mana break fast Nuhaira ta shirya ta fita makaranta ni kuma na kai mata abin karin nata ɗaki bayan ta ɗanci ba yawa na bata magani kamar yadda likita yace.
Bayan na kwashe kayan na dawo na zauna cikin tausasa murya na kalle ta nace.
“Mama miye yake damunki haka? Mi kike tunani da har ya sa miki hawan jini nan take? Dan Allah Mama ki gayamin”
Girgiza kanta tayi tace.
“Ni dai ban san ina da wata damuwa ba Bahiyya, gaskiya ban sani ba.....”
Cikin rashin gamsuwa da maganar ta nace.
“A'a Mama, dan Allah ki gayamin minene damuwar ki,irin wannan ciwon ba zai kama mutum ba muddin ba damuwa ce a ransa ba.”
“Ni kam bani da wata damuwa Bahiyya”
Juyin duniyar nan nayi amma Mama ta kafe tace min babu abinda yake damunta dole na hak'ura na ƙyale ta ina faɗin.
“To tunda kince ba abinda yake damunki, dan Allah ki kwantar da hankalinki idan ma akwai wani abinda ba zaki iya gayamin ba kiyi haƙuri ki cire sa a ranki, bana so mu koma wurin likitin bayan kwana biyu ya aunaki yace min ga wata damuwa, idan wani abu ya sameki Mama ban san ya zamuyi ba. Kece ƙwarin guiwar mu, kece kaɗai muke da, ke kika zama bangon jinginar mu idan wani abu ya sameki ban san in da zamu shiga ba. Mama ke ce fa kullum kike min faɗa akan in dai na damuwa, in zama mai tawakkali, yau kuma ace kece wai hawan jini ya kama, mi kika nema kika rasa? Idan ma mutuwar Baba ce ya kamata ace kin saba kamar yadda kike faɗamin Mama...”
Hawayen da suka gangaro min na share tare da Miƙewa tsaye na fita waje jin sallamar yaro ya shigo gidan namu.
Mama kuwa mirginawa tayi ta kwanta akan pillow wasu hawaye masu zafi na bin gefen kuncin ta. Haƙiƙa mutuwar Jafaru ta nakasa mata zuciya ta yadda ma bata yi tsammani ba. Idan tace tana samun wadataccen bacci tsawon shekarar nan tayi ƙarya, babu abinda take tunani sai mijinta da kuma rayuwar marayun 'ƴa' ƴan ta mata guda biyu, waɗannan mutanen da suka kashe mijinta sunyi mata illar da har ta kwanta damanta ba zata warke ba. Domin shine jigonta shiya kawo ta wannan ƙasar ta Nigeria ba tare da tasan wani mutum na daban ba bayan shi. Gashi har ya koma ga Allah ƙasar ta sa ta gagare shi komawa akan wani dalilin banza na son zuciya irin na mutanen yau. Har baro garin Gusau tayi ko zata samu sauƙi ta manta da rayuwar su ta baya amma abin ya ci tura. To kuma yanzu ga ƙarin wata matsalar ta kunno kai tunda likitan ya faɗa mata tana da hawan jini damuwar ta da fargabar ta suka ƙaru, damuwa ta ƙara baibaye ta fiye da ta baya.
Ita tsoron ta kullum idan ta mutu a wane halin rayuwar 'ya' ƴan ta za su kasance? Sannan idan suka isa aure wa zai aure su idan akaji cewar ba su da dangin uwa babu na uba suka ɗai ne su uku suke rayuwar su.
Bayan kwana biyu kamar yadda likitan yace, na shirya na cewa mama ta shirya mu koma wurin mai chemist kamar yadda yace, ƙin amincewa tayi ta kafe kai da fata tace min taji sauƙi ba sai mun koma ba. Ƙarshe ma faɗa ta rufe ni da shi wai duk laifi na ne, daman su mutanen nan matuƙar kana ziyartar su to kullum cikin kira maka matsala suke, da ace na siyo mata maganin ta tun ranar tasha da yanzu kowa na nan hankalin sa kwance, to ita babu in da za ta je ta warke.
Dole na na kama kaina na ja baki na nayi shiru na ƙyale ta, amma Ina kula da ita sosai duk wani motsin ta yana kan idona, sai dai daga baya na gano tabbas Mama bata samun bacci kamar yadda likita yace, akai akai idan na farka naje ɗakin ta zaune nike samun ta kan sallayah.
Tun daga wannan lokacin na bata shawara ta riƙa sai ta lokaci idan ma tashin zatayi na dare to ta ta shi amma ta rage ɗaukar dogon lokaci.
Haka mukaci gaba da rayuwa, Mama ta samu sauƙi sosai a gaban idanunmu kamar yadda take nuna mana idan abin ya tasar mata sai ta tafi can wani chemist ta sayi magani ta dawo gida ta ɓoye tana sha don kar mu gani hankalin mu ya tashi. Nuhaira taci gaba da karatun ta, nima ina yawon lalle na da yanzu na ƙara yawan customers.
*************
Hanifah
Ko bayan rabuwar su da Farooq sai da ta sake share wata biyu da sati biyu a Dubai sannan ta wuce Egypt ta sake yin sati biyun ta masu kyau sannan ta dawo.
Duk iya yanda Farooq ya ɗauki fushi da ita kasa daurewa yayi dole ya dawo kiranta a waya yana jin muryarta amma bai taɓa tambayar ta cewa ina take ba, mi take yi ko yaushe zata dawo. Iyaka suyi wayar su idan sun ƙare su kashe. Sau biyu tafiya tana kama shi zuwa Dubai bai taɓa attempting na cewa ya je wurinta ba. Ya ƙyale ta har lokacin da ta ga dama ta dawo don kan ta.
Ko da ta iso ma baya ƙasar yana Saudiyya tare da Madinat sun je aikin Umrah sai da tayi kwana huɗu da dawowa sannan ya dawo.
Tare da Madinah suka shigo gidan, tunda yayi rashin lafiyar nan ta zo bata koma Kaduna ba. Cikin murna tazo ta tare shi tana faɗin.
“Welcome”
Kamar wanda yake mafarki haka yayi hugging ɗin ta back yace.
“Am i dreaming?”
Dariya tayi tace.
“No! Not at all. Is your Hanifah”
Ƙara riƙe ta yayi gam a jikin shi yana faɗin.
“Welcome back home my love”
“Thank you”
Ganin Madinah yasa tayi saurin janye jikin ta taje gareta with soft smile on her face ta bata side hug tace.
“Welcome Grand Ma”
Cikin Kalaman hikima Madinah tace.
“Thank you Hanifah. Da fatan an dawo lafiya”
Hanifah tace
“Lafiya lau Grand Ma”
Madinah tace
“Ya kasuwa? Ya familyn ki? Da fatan komai lafiya?”
Hanifah tace
“Everything is fine, my family are doing good”
“That's nice to hear.”
Madinah tace tare da kama hanyar zuwa masaukinta,luggage ɗin ta da suke hannun shi da kanshi ya wuce har ɗakin ya kai mata, daman tun a mota da suka sauka ya hana kowa ɗaukar kayan yace aikin shi ne saboda haka shi zai kwashe kayan.
Yana fitowa ya zarce ɗakin shi ya je yayi wanka ya shirya itama Hanifah da sauri taje ta sake yin wanka ta shirya cikin riga da wando da suka amshi fatar ta sukayi raɗau, sai wata hular net da ta saka ta naɗe kanta da ita tayi matuƙar kyau. Daman kuma kafin ta shiga ciki sai da ta saka Nafisat cook ɗinta cewa ta shiryawa Farooq table kafin su fito.
Ta riga shi fitowa hakan yasa ta wuce ɗakin shi direct ta sa meshi ya gama shiryawa yana tsaye jikin window yana kallon waje, hannayensa soke a cikin trouser pocket ɗin shi.
A hankali taje ta rungume shi ta baya tare da ɗora kanta a bayan shi tayi lamo, dukkan su babu wanda yacewa kowa komai tsawon lokaci suna a haka. Sai daga baya ta ja numfashi a hankali sannan cikin pleading tone tace.
“I'm sorry. I'm very sorry for what I did. I know that I hurt you, but what ever it is you are....”
Da sauri ya birkito ta ya rufe bakin ta da nasa yayi kissing ɗinta passionately sannan ya janye ya kalle ta cikin shauƙi yace.
“karki damu ni komai ya riga da ya wuce a wurina Hanifah”
Murmushi tayi tace.
“Thank you. Muje kaci abinci Nafisat ta gama shirya table”
Ba musu ya bi ta suka je suka zauna zaman cin abinci, yana cikin ci ya ji an kira sallahr magrib a masallacin gidan sa, da sauri ya miƙe yace.
“Hanifah an kira sallah, ya kamata ace na bar cin abincin nan har in dawo daga isha”
Kallon shi tayi tace.
“To kabari ka ƙarasa mana tunda ka fara”
Hanyar waje ya nufa yana faɗin.
“No, Idan na dawo after isha prayer sai ki sa a sama min wani abin”
Daga haka ya wuce ya barta. Zaman sa tare da Madinat wannan karon ya sa shi ya ɗan canza sosai, domin a lokutan baya Sallah a jam'i bata wani dame shi ba musamman idan yana gida. Amma yanzu ya dage sosai har asubahi yana fita.
“Ta daɗe tana complain cewa ƙirjinta yana ciwo, to duk lokacin da abin ya tasar mata sai inzo in sayi mata magani ko nan ko kuma wani wuri in bata tasha, to yau dai bama nan ko da muka dawo kuma mun cimmata a haka”
Nidai ganin nayi ya ɗauko wani abu ya ɗaura mata a hannun ta sannan ya saka wani a kunne bayan ya gama. Ya kalle ni yace min hawan jini ne da ita kuma ya hau sosai fiye da ƙima.
Cikin tsantsar mamaki ni da Nuhaira muka haɗa baki wurin kiran.
“Hawan Jini likita?”
Cikin kuka na sake cewa.
“Hawan jini ta yaya? Wane irin hawa jini dan Allah, muna zaune lafiya”
Mutumin yace.
“While, ba abin mamaki ba ne ai, musamman idan akwai wata damuwa tare da ita tana yawan tunani da rashin samun ishashshen bacci, amma...”
Sai ya juya ya hahhaɗo magunguna ya bani na kusan dubu goma sha ɗaya.
A nan ya buɗe ya bata maganin, sannan yace
“idan akwai abinda yake saka ta damuwa kuyi ƙoƙari ku ɗauke mata hankali a kai, ta riƙa samun bacci yadda ya kamata tana cin abinci mai kyau, in sha Allah zata ji sauƙi”
Daga haka na cewa Nuhaira taje gida ta ɗauko masa kuɗin shi, bayan ta dawo muka koma gida, kafin shiga bacci har mun samu taji sauƙi domin har ta tashi tayi Sallah taci abinci.
Washe gari bayan mun gama sallar Asuba muka je muka gaishe ta nayi sauri na haɗa mana break fast Nuhaira ta shirya ta fita makaranta ni kuma na kai mata abin karin nata ɗaki bayan ta ɗanci ba yawa na bata magani kamar yadda likita yace.
Bayan na kwashe kayan na dawo na zauna cikin tausasa murya na kalle ta nace.
“Mama miye yake damunki haka? Mi kike tunani da har ya sa miki hawan jini nan take? Dan Allah Mama ki gayamin”
Girgiza kanta tayi tace.
“Ni dai ban san ina da wata damuwa ba Bahiyya, gaskiya ban sani ba.....”
Cikin rashin gamsuwa da maganar ta nace.
“A'a Mama, dan Allah ki gayamin minene damuwar ki,irin wannan ciwon ba zai kama mutum ba muddin ba damuwa ce a ransa ba.”
“Ni kam bani da wata damuwa Bahiyya”
Juyin duniyar nan nayi amma Mama ta kafe tace min babu abinda yake damunta dole na hak'ura na ƙyale ta ina faɗin.
“To tunda kince ba abinda yake damunki, dan Allah ki kwantar da hankalinki idan ma akwai wani abinda ba zaki iya gayamin ba kiyi haƙuri ki cire sa a ranki, bana so mu koma wurin likitin bayan kwana biyu ya aunaki yace min ga wata damuwa, idan wani abu ya sameki Mama ban san ya zamuyi ba. Kece ƙwarin guiwar mu, kece kaɗai muke da, ke kika zama bangon jinginar mu idan wani abu ya sameki ban san in da zamu shiga ba. Mama ke ce fa kullum kike min faɗa akan in dai na damuwa, in zama mai tawakkali, yau kuma ace kece wai hawan jini ya kama, mi kika nema kika rasa? Idan ma mutuwar Baba ce ya kamata ace kin saba kamar yadda kike faɗamin Mama...”
Hawayen da suka gangaro min na share tare da Miƙewa tsaye na fita waje jin sallamar yaro ya shigo gidan namu.
Mama kuwa mirginawa tayi ta kwanta akan pillow wasu hawaye masu zafi na bin gefen kuncin ta. Haƙiƙa mutuwar Jafaru ta nakasa mata zuciya ta yadda ma bata yi tsammani ba. Idan tace tana samun wadataccen bacci tsawon shekarar nan tayi ƙarya, babu abinda take tunani sai mijinta da kuma rayuwar marayun 'ƴa' ƴan ta mata guda biyu, waɗannan mutanen da suka kashe mijinta sunyi mata illar da har ta kwanta damanta ba zata warke ba. Domin shine jigonta shiya kawo ta wannan ƙasar ta Nigeria ba tare da tasan wani mutum na daban ba bayan shi. Gashi har ya koma ga Allah ƙasar ta sa ta gagare shi komawa akan wani dalilin banza na son zuciya irin na mutanen yau. Har baro garin Gusau tayi ko zata samu sauƙi ta manta da rayuwar su ta baya amma abin ya ci tura. To kuma yanzu ga ƙarin wata matsalar ta kunno kai tunda likitan ya faɗa mata tana da hawan jini damuwar ta da fargabar ta suka ƙaru, damuwa ta ƙara baibaye ta fiye da ta baya.
Ita tsoron ta kullum idan ta mutu a wane halin rayuwar 'ya' ƴan ta za su kasance? Sannan idan suka isa aure wa zai aure su idan akaji cewar ba su da dangin uwa babu na uba suka ɗai ne su uku suke rayuwar su.
Bayan kwana biyu kamar yadda likitan yace, na shirya na cewa mama ta shirya mu koma wurin mai chemist kamar yadda yace, ƙin amincewa tayi ta kafe kai da fata tace min taji sauƙi ba sai mun koma ba. Ƙarshe ma faɗa ta rufe ni da shi wai duk laifi na ne, daman su mutanen nan matuƙar kana ziyartar su to kullum cikin kira maka matsala suke, da ace na siyo mata maganin ta tun ranar tasha da yanzu kowa na nan hankalin sa kwance, to ita babu in da za ta je ta warke.
Dole na na kama kaina na ja baki na nayi shiru na ƙyale ta, amma Ina kula da ita sosai duk wani motsin ta yana kan idona, sai dai daga baya na gano tabbas Mama bata samun bacci kamar yadda likita yace, akai akai idan na farka naje ɗakin ta zaune nike samun ta kan sallayah.
Tun daga wannan lokacin na bata shawara ta riƙa sai ta lokaci idan ma tashin zatayi na dare to ta ta shi amma ta rage ɗaukar dogon lokaci.
Haka mukaci gaba da rayuwa, Mama ta samu sauƙi sosai a gaban idanunmu kamar yadda take nuna mana idan abin ya tasar mata sai ta tafi can wani chemist ta sayi magani ta dawo gida ta ɓoye tana sha don kar mu gani hankalin mu ya tashi. Nuhaira taci gaba da karatun ta, nima ina yawon lalle na da yanzu na ƙara yawan customers.
*************
Hanifah
Ko bayan rabuwar su da Farooq sai da ta sake share wata biyu da sati biyu a Dubai sannan ta wuce Egypt ta sake yin sati biyun ta masu kyau sannan ta dawo.
Duk iya yanda Farooq ya ɗauki fushi da ita kasa daurewa yayi dole ya dawo kiranta a waya yana jin muryarta amma bai taɓa tambayar ta cewa ina take ba, mi take yi ko yaushe zata dawo. Iyaka suyi wayar su idan sun ƙare su kashe. Sau biyu tafiya tana kama shi zuwa Dubai bai taɓa attempting na cewa ya je wurinta ba. Ya ƙyale ta har lokacin da ta ga dama ta dawo don kan ta.
Ko da ta iso ma baya ƙasar yana Saudiyya tare da Madinat sun je aikin Umrah sai da tayi kwana huɗu da dawowa sannan ya dawo.
Tare da Madinah suka shigo gidan, tunda yayi rashin lafiyar nan ta zo bata koma Kaduna ba. Cikin murna tazo ta tare shi tana faɗin.
“Welcome”
Kamar wanda yake mafarki haka yayi hugging ɗin ta back yace.
“Am i dreaming?”
Dariya tayi tace.
“No! Not at all. Is your Hanifah”
Ƙara riƙe ta yayi gam a jikin shi yana faɗin.
“Welcome back home my love”
“Thank you”
Ganin Madinah yasa tayi saurin janye jikin ta taje gareta with soft smile on her face ta bata side hug tace.
“Welcome Grand Ma”
Cikin Kalaman hikima Madinah tace.
“Thank you Hanifah. Da fatan an dawo lafiya”
Hanifah tace
“Lafiya lau Grand Ma”
Madinah tace
“Ya kasuwa? Ya familyn ki? Da fatan komai lafiya?”
Hanifah tace
“Everything is fine, my family are doing good”
“That's nice to hear.”
Madinah tace tare da kama hanyar zuwa masaukinta,luggage ɗin ta da suke hannun shi da kanshi ya wuce har ɗakin ya kai mata, daman tun a mota da suka sauka ya hana kowa ɗaukar kayan yace aikin shi ne saboda haka shi zai kwashe kayan.
Yana fitowa ya zarce ɗakin shi ya je yayi wanka ya shirya itama Hanifah da sauri taje ta sake yin wanka ta shirya cikin riga da wando da suka amshi fatar ta sukayi raɗau, sai wata hular net da ta saka ta naɗe kanta da ita tayi matuƙar kyau. Daman kuma kafin ta shiga ciki sai da ta saka Nafisat cook ɗinta cewa ta shiryawa Farooq table kafin su fito.
Ta riga shi fitowa hakan yasa ta wuce ɗakin shi direct ta sa meshi ya gama shiryawa yana tsaye jikin window yana kallon waje, hannayensa soke a cikin trouser pocket ɗin shi.
A hankali taje ta rungume shi ta baya tare da ɗora kanta a bayan shi tayi lamo, dukkan su babu wanda yacewa kowa komai tsawon lokaci suna a haka. Sai daga baya ta ja numfashi a hankali sannan cikin pleading tone tace.
“I'm sorry. I'm very sorry for what I did. I know that I hurt you, but what ever it is you are....”
Da sauri ya birkito ta ya rufe bakin ta da nasa yayi kissing ɗinta passionately sannan ya janye ya kalle ta cikin shauƙi yace.
“karki damu ni komai ya riga da ya wuce a wurina Hanifah”
Murmushi tayi tace.
“Thank you. Muje kaci abinci Nafisat ta gama shirya table”
Ba musu ya bi ta suka je suka zauna zaman cin abinci, yana cikin ci ya ji an kira sallahr magrib a masallacin gidan sa, da sauri ya miƙe yace.
“Hanifah an kira sallah, ya kamata ace na bar cin abincin nan har in dawo daga isha”
Kallon shi tayi tace.
“To kabari ka ƙarasa mana tunda ka fara”
Hanyar waje ya nufa yana faɗin.
“No, Idan na dawo after isha prayer sai ki sa a sama min wani abin”
Daga haka ya wuce ya barta. Zaman sa tare da Madinat wannan karon ya sa shi ya ɗan canza sosai, domin a lokutan baya Sallah a jam'i bata wani dame shi ba musamman idan yana gida. Amma yanzu ya dage sosai har asubahi yana fita.