← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 23

Sashe 6

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari ƙarfe goma na safe a gidan Madinah tayi masa kamar yadda ya tsara.
Zaunawa yayi kusa da ita ya ɗora kansa akan gefen shoulder ɗinta for almost 15mnt relaxing him self from all the stress that he's going through. He used to feel safe and secure when ever he's with his amazing Grandma.
Sai da ya jima a haka Daga baya yayi taking deep breath sannan ya ɗago ya kalle ta yace.

“madinah zaki zo tare dani wurin taya Hanifah murna?”

Murmushi tayi tace.

“Satin nan ne gaba ɗaya busy nake gaskiya, kawai ka faɗa mata ina gaishe da ita ina mata fatan nasara”

“Owk!, zata ji in sha Allah. Ki tashi ki samamin wani abin yunwa ni keji”

“To ai kai ne baka sanar dani zuwan naka ba da yanzu ka isko komai a shirye, amma karka damu yanzun nan in sha Allah zaka samu abinda kaci”

Tashi tayi ta nufi kitchen shi kuma ya wuce ɗakin ta ya kwanta a kan gadonta.
Dakatar da masu aikinta tayi akan su bata wuri idan ta kambala sai su dawo su gaba da abinda suke.

**************

BAHIYYA

  Kamar yadda Malama Rabi ta alƙawartamin, kwatsam muna zaune da safe ina niƙa kamar kullum Nuhaira na kan sana'ar ta ta kayan miya ta shigo tace min. Ina Mama na ce mata tana ɗaki, ɗakin ta wuce ni ban ji mi suka tattauna akai ba kawai dai mama ta kira ni tace in zo maza in shirya mu tafi zanyi wa wata hajiya kitso da lalle ita da 'ƴa' ƴan ta. Nan da nan na shirya muka tafi.

Duk yadda naji ana ambatar kyau irin na garin babban birnin Abuja ban taɓa zaton kyaun shi da tsarin shi ya kai haka ba sai yau.

Gidan ma da muka shiga da Malama Rabi tunda uwata ta haife ni ban taɓa gani gida irin wannan ba. Ya haɗu iya haɗuwa ya tafi da Imani na.
A yadda naga tsarin cushion ɗin parlorn da abinda ke cikinsa a baki-baki na ɗan ɗosana ɗuwawu na zuciya ta sai bugu take tamkar ace kyat in zura da gudu.
Munfi kusan minti talatin sannan naga wata ƙofa ta buɗe wata kyakkyawar matashiyar mata ta fito wadda aƙalla zatayi arba'in zuwa arba'in da biyar tare da yara mata guda uku mabiyan juna, farare tas masu kyau da su anyi musu parking dogon gashin su da yasha gyara.

Da sauri na sauka ƙasa kamar yadda naga malama Rabi tayi nace.
"Ina kwana”

Zaunawa tayi tana mai sakin tattausan murmushi ta kalleni tace.

“Lafiya lau, kece mai Lallen kenan”

Ɗan ƙara yin ƙasa da kaina nayi nace.
“Eh nice”

Matar ta kalli Malama Rabi tace.
“To Malama sai ta fara musu Lallen ina zuwa yanzu, Ku koma can Main parlour kuyi a can”

Tashi mukayi kamar yadda tace muka koma wurin da tayi mana umurni, ware ido nayi da kyau na ƙarewa Parlourn kallo a raina nace masu kuɗi sunji daɗin su yanzu shi wannan Parlourn daban da wancan kuma a nan zamuyi zaman lalle.

“Bahiyya Ki haɗa Lallen ki fara kin san lokaci ba wahala yayi nisa”

Aikin lalle Indai na saka kaina nan da nan nike zane sa in tashi domin ni daman ina da zahin nama wurin yin abu.
Kafin kace mi har na gama tsantsare su da Lalle, kuma a yadda naga  yaran na farin ciki shi ya tabbatar min da cewa lallen ba ƙaramin  burgesu yayi ba. Ina gama musu nayi sallahr zuhr aka kawo abinci mai rai da lafiya naci nayi hani'an sannan na hau yarfa musu kitso, Ina cikin yi musu kitson ne wasu yara maza suka shigo guda biyu matasa haka ganin kamannin su da yaran da nike wa kitso shi ya tabbatar min da cewa yayyunsu ne.

Ɗayan wucewa yayi ya buɗe wata ƙaramar locker ya ɗauki takardu ya fice shi kuma ɗayan ya tsaya yana ta santin lallen wadda naji ya kira da Nimrah yana tsokanarta.

Bayan an kambala komai na wanke musu lallen matar ta fito tana ta godiya tace itama da bada ita ba amma dan Allah zuwa Friday ta kawo ni in zo in yi mata domin ta yaba da aiki na yafi burge ta fiye da na Maryam. Kasancewar yamma ta riga tayi dole zamu tafi gida.

Kuɗi ta ƙundula ta bani tare da kaya a wata ledar shopping, sannan ta bani wasu kuɗin daban ta ce min 5k ne kuɗin kayan lallen da na siyo cikin mamaki nace mata ai kuɗin bai kai haka ba tace to in tafi kawai komai ta bani bata biya ba domin yaran ta sunyi kyau sosai. nayi mata godiya sosai muka dawo gida. Bayan mun shigo gida nabawa malama Rabi kuɗi tace min a'a in riƙe duka nawa ne itama ta sallameta. Nuhaira uwar kaɗaɗi ita ta buɗe ledar bayan Malama ta tafi. Turmin atamfa ne da kayan cusmetics masu tsada na 'ƴan gayu. Kuɗin kuma da ta ban daban dubu ashirin ne cif. Mamaki ya kasa ɓoyuwa akan fuskokinmu musamman Mama, zunzurutun dubu ashirin da biyar kai tsaye kamar tsintuwa. Addu'a tayi ta min ni dai Nuhaira tana yi mana fatan alheri wanda hakan ba ƙaramin daɗi yake min ba.

*************

Jumeirah Lakes Towers (JLT)
Dubai, UAE.

  Ranar Friday itace wadda ta kasance ranar ƙaddamar da center Hanifah kamar yadda tayi buri.
    Wurin ya ƙayatu iya ƙayatuwa fiye da yadda bata zata ba, Daddy ya shirya mata taro wanda har a cikin ranta taji ta ƙayatu ainun sannan kuma ya fitar da ita kunyar baƙin ta. Babu abinda zata cewa daddy sai godiya................

*OUM-AMEER *
💝 *BAHIYYA* 💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*AMINA IBRAHIM*
(OUM-AMIR)
*WATTPAD:*
*@UMMU-AMEER*
*PAID BOOK 500*
*3132703269*
*FIRST BANK*
*AMINA IBRAHIM*
*08068974831*

*FREE PAGE*
*BABI NA BIYAR*

............... A makare ya iso wurin shiyasa bai samu haɗuwa da ita ba sai a filin taron. Tunda ta tunkaro shi ya kasa ɗauke idon sa a kanta domin ba ƙaramin kyau ta masa ba. Wata arniyar Maroon Red carpets gown ce mai jela a baya a jikinta wadda ta bi jikinta ko ina ta manne tamkar an bita da fenti, an yi mata tsaga daga guiwar ƙafarta ta ta dama a ta gaba zuwa ƙasa, wuyan rigar V shaped ne yayin da ɗayan hannun rigar yake dogo duk an bishi da tsagu sai kuma ɗayan aka yi shi guntu cure da chipom. Gashin kanta kuma yasha gyara wanda aka nannaɗe wuri ɗaya a bayan ƙeyar kanta. Ta sha kyau sosai mutane sai yabawa suke. Daga inda Mahi yake zaune yana hango ta ji yake ranshi yana mishi wani iri, wai wannan matar Farooq ce, wai nan ita musulma ce mai sallolli guda biyar, kuma ƙarin abin haushin ma wai ga iyayenta a wurin duk suna kallon ta kuma ko a jikin su, sai kuma ya juya ya kalli dressing ɗin mamar ita kanta da kuma ƙanwar ta Hamrah kawai sai naga yayi murmushi tare da girgiza kai a ranshi yace wata Wayewar dai in dai haka take Allah ya tsare mu da ita.

Murmushi suka sakarwa juna ita da Farooq ɗin ta , a hankali ya tare ta tare da bata wani hurt hugging a hankali cikin shauƙi ya ɗora soft lips ɗinsa akan bare neck ɗin Hanifah yayi kissing ɗinta sannan yayi taking deep breath ya shaƙi ƙamshinta Mai ɗadi sannan ya janye ya saita idanuwansa a nata a hankali ya furta mata.

“ I so much miss you Hanifah, without you my life is going to be miserable. You look very beautiful and adorable wife, I'm really proud of you, Ina yi miki fatan nasara da fatan albarka ga duk abinda kika sa ma gaba Indai na alkaiiri ne, Grand Ma Itama tace in faɗa miki haka”

Hawayen farin cikin da suka gangaro mata ne tayi saurin sharewa tare da jin daɗin Kalaman mijinta with so much happiness tace.

“Thank you Farooq, you are the best husband ever, I really appreciate, a yanzu na gama sakankancewa da cewa duk abinda ka ke min da zuciya ɗaya kake yinsa a matsayi na na matarka, ka bani matsayin da ba kowa ne irin namiji ne ya ke iya bawa matar sa ba, I'm proud of you for being my lovely and caring husband, ban san ta ya zan iya gode maka ba....”

Ɗan yatsan sa ya ɗora akan lips ɗin ta yace.
"Shhh! kullum ni kawai abinda ni ke so Hanifah muddin zaki ƙaunace ni ki So ni, ni hakan ma is ok for me. I love you”

Hugging ɗin shi tayi tana murmushi tace.

“I love you so much Farooq”

Kawai ji sukayi ɗakin ya ɗauki tafi raf-raf-raf. Ana ihu ana yi musu kirari. Bayan like 20mnt haka aka gama shirya komai, aka shiga gudanar da ƙayataccen bukin yadda ya kamata.

Farooq bai san Mahi na wurin ba sai bayan da aka gama taron duk rabin mutane sun watse sannan ya gansa kawai yana masa murmushi. Ba ƙaramin mamaki ya bawa Farooq ba har bai san lokacin da yace.

“Mahi you are the most crazy friend in this world, when did you arrived here?”

Dariya Mahi yayi yace.
“While tunda Baban Soyayya ya kama Hanifah ya riƙe ta kamar zai cinye ta”

“Mahi I have every right because she's my wife, so don't judge me, kayi Abinda ya shafe ka”

Hannayensa ya ɗaga sama yana dariya yace.
“I rest my case”

Murmushi Farooq yayi yace.
"Better.” sai kuma ya sake kallon Mahi ɗin yace.
“ And thank you for coming, I really appreciate your presence.”

“Kafi haka a wurina Farooq, Ina Hanifah murna...”

Da sauri Farooq ya ɗaga masa Hannu tare da ciro wayar sa a pocket ɗin sa yace.

" Wait! Let me call her she's around here Sai ku gaisa zai fi”

Cikin mintunan da ba su gaza sha biyar ba ta iso wurin. Hannunta ta saƙala cikin wuyan hannun Farooq tana murmushi ta kalli Mahi tace.

" Mahi welcome”

Murmushi yayi yace.

“Congratulations Mrs Mai-gishiri, Allah ya sanya alheri yasa rai aka yiwa, ya kuma ƙaro dimɓin nasarori”

“Amin, thank you Mahi”

Daga haka ta juya ta ci gaba da sallamar baƙin ta. Su ma su Farooq ɗin daga nan suka wuce wurin nasu yi.
Chapter 6 · 0% Book details