Sashe 16
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Haƙiƙa kin cika jajirtaciyya 'ƴa mai nagarta Bahiyya, kin saka kaifin hankali da basira wanda ni kaina tunanin hakan bai zo min ba, Hajiya Rasi'a mace ce mai taimako sosai, gaba ɗaya Allah ya mantar da ni da tunanin zuwa wurin abokan hulɗarki. Mungode mata sosai in sha Allah zan je har gida na yi mata godiya...”
Dariya ce ta suɓuce min bayan tunawa da Yarjejeniyar mu ni da Hajiya Hanifah na kalli malama nace.
“To amma kun san wani abu? Ita wannan hajiya Hanifah ɗin sai da mukayi wani sharaɗi a tsakanin mu, cewa wai zan taya ta renon cikinta idan ta haihu sai in dawo gida, nace mata ba matsala, wai harda cewa naje nayi shawara, ban san lokacin da na saka mata kuka ba, nace ba wata shawara ni na amince kawai tazo ta biya mana kuɗin.”
Cikin mamaki Malama tace
“ renon ciki kamar yaya? Ke da ba mijin ta ba taya zaki taya ta renon ciki? Kuma na san dai tana da masu aiki birjik duk basu ishe ta ba sai ke?”
A wauta irin tawa ban kawo komai a raina ba nace.
"Malama kin san halin masu kuɗin nan shegen son jikin tsiya ne da su, kuma mijin dole ya fita wurin sabgoginsa na yau da kullum, to wata ƙila ko ruwa tafi so a bata a baki, ni kuma ba ruwa ba ko wanka tace in yi mata wallahi tsab zan iya ina ruwana..”
Dariya Nuhaira ta fashe da ita tace.
"Kai Aunty Bahiyya wanka fa?”
Nima dariyar nayi nace.
" Wallahi Nuhaira da gaske na ke, ko wanka ta ce in riƙa yi mata zan yi matuƙar buƙata ta zata biya, biyan buƙata ai yafi dogon buri. Su masu kuɗin nan kawai idan tsabar jin daɗi yayi musu yawa haukacewa ma su ke, har a rasa mima za'a yi da kuɗi”
Murmushi Malama tayi tace.
“Abu ɗaya muke fata, Allah ya sa ayi aikin nan cikin nasara ya tashi kafaɗunta ”
Duk muka amsa da amin.
***************
HANIFAH
Bayan fitowa ta daga motar wani farin ciki ne ya lulluɓeta domin ba ƙaramar sa'a ta taka ba. Ainahin dalilin zuwanta gidan Rasi'a shine; bayan fitowar ta daga asibitin Nicholas direct office ɗin Farooq ta wuce cike da farin ciki ta sa mesa ta shaida masa yadda suka yi. Nan fa suka hau daru yace shi sam bai yarda ace Christian ce zata ɗaukar masa cikin ɗansa ba, ai addinin mu ya faɗamana cewa tun a ciki yaro yake fara koyon abubuwa kafin ya fito duniya, kuma ya kan ɗauko halayya da ɗabi'u saboda haka ba zai yi farin ciki ba ace wai ɗansa zai fito daga tsatson da addinin su bai zo ɗaya ba. Matuƙar tana so ya amince to ba zai yarda ayi dashen ɗansu a mahaifar Agnes ba, sai dai a fasa. Wuta sukayi sosai da shi. Ƙarshe cikin fushi ta baro Office ɗin direct ta nufi gidan Aminiyarta Rasi'a don ta koka mata matsalar ta sannan ta nemi shawarar ta akan ina ya kama ta a samo wadda za'a yi wannan aikin da ita. Kwatsam cikin sa'a sai gashi tayi katari da wannan damɓarwar tsakanin Rasi da Mijin ta. Cikin ƙwarewa da iya kanta ta jefi tsuntsu biyu da dutse Ɗaya.
Tasan idan ta faɗawa Rasi manufarta akan Bahiyya a yanda taga tana ƙaunar yarinyar nan ba zata amince ba, amma cikin ruwan sanyi gashi buƙatar ta zata biya. Addu'a take a cikin ranta Allah ya tabbatar da tafiyar su a gobe ɗin shi kenan itakam hankalin ta kwance.
Bayan ta gama nazare - nazarenta ta umurci drivernta akan ya nufi hanyar gida.
Tana shiga cikin sa'a kuwa taci karo da farooq ɗin ya dawo, masallaci ya wuce bai dawo ba sai bayan sallar Isha.
Har ɗaki ta samesa bayan ya fito daga wanka tayi murmushi ta ce.
“Welcome!”
Shima murmushin ya mayar mata yace.
“Thank you Hanifah. Ina kika je ne? Na je har office ɗin ki bakya nan?”
Murmushi tayi tace.
“Ina da wani sauran hutu ne bayan nasan cewa ban cika maka muradin ka ba. Na je neman matar kamar yadda ka buƙata...”
Runtse idanunsa yayi tare da girgiza kai yace.
“Hanifah! Hanifah! You are there stressing your self. Ni fa abun ma ya fara fita daga kaina...”
Cikin shagawaɓewa tace.
“But I have already found the woman, musulma Mai addini kamar yadda ka buƙata. Dan Allah Farooq ka karɓi abun nan da zuciya ɗaya please”
Kafaɗar sa ya ɗaga tare da ware hannayensa alamar shi kenan.
Hugging ɗinsa tayi tare da narke masa tana sakar masa sabbatu, shi kuma daman can in dai Hanifah zata biye sa to yafi ƙaunar wannan rayuwar soyayyar fiye da komai a duniya . Duk son sa da abinci haka suka lalace a wurin suna ta abu ɗaya.
***************
BAHIYYAH
Firah muka sha sosai muna ta tsara yadda zamuyi da likita kamar yadda ya faɗa mana cewa da zaran an samu kuɗin zai shige mana gaba a shirya yi mata aikin. Mama ma jefi jefi ta kan ɗan sako bakinta kaɗan. Gaba ɗaya da ka kalle mu kasan cewa cikin kashi saba'in kashi talatin na daga cikin damuwar mu ya tafi da ikon Allah.
Sai da aka gama sallar Isha mijin malama yazo ya gaida Mama, malama ta faɗa mishi abinda ake ciki ya nuna farin cikin sa yayi mana addu'a sannan suka fita zuwa gida.
A bakin get ɗin asibitin na tsaya nace.
“Malama dama akwai maganar da nike so in sanar miki.”
Tsayawa tayi shi Kuma uncle Idris yayi gaba wurin mashin ɗinsa ya tsaya jiran mu.
Kallon ta nayi tare da marairece murya na riƙe hannun ta nace.
"Malama akwai abinda na ɓoye ban faɗa muku ba. Matar tace ba a ƙasar nan zatayi renon cikin ba kuma dole in amince in tafi tare da ita, to na san idan na faɗa kai tsaye hankalin Mama na iya tashi ni kuma bana son abinda zai ɗaga mata hankali a halin yanzu”
Jinjina kai Malama tayi alamar abin babba ne tace.
"Dole kuma sai tare da ke Bahiyya? Anya zan yarda da wannan matar kuwa?”
Cikin magiya nace.
“Malama dan Allah kada ki ce a'a please, wallahi nayi imani ba zata cutar dani ba, gobe fa da kanta tace zata zo nan, kuma na faɗa miki babbar Aminiyar maman Khadijat ce idan har ba ta kirki ba ce maman Khadijat ba zata haɗani da ita ba. Malama wannan hanyar ita kaɗaice hanyar da zan iya ceto rayuwar mahaifiya, ba zan iya bari wannan damar ta wuce ni ba, domin idan Mama ta mutu wallahi ni kaina rayuwata tazo Ƙarshe, kawai abinda nike so da ke shi ne ki tayani da addu'a kuma ki kula min da Mama ta da Ƙanwata, shekara kamar kwana ce take cikin Ikon Allah zaki ga shekara ta zagayo, in sha Allah kuma zaku same ni mai kiyaye wa”
Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace.
“Bahiyya duk don saboda mahaifiyar ki kika yarda da ɗaukar wannan kasadar, dole zan kirashi da kasada domin ba ki san ina zaki ba kuma baki san mi zaki tarar ba, amma koma minene ina miki fatan tsarin ubangiji a duk inda kike, tunda har saboda mahaifiyarki kika ɗauki wannan nauyin in sha Allah ubangiji zai saka miki da abinda baki yi tsammani ba domin uwa ta sha gaban komai da albarkar ta zaki yi nasara a rayuwar gwagwarmayar ki in sha Allah. Zan kira Hajiya Rasi'a zuwa gobe in sha Allah domin in ƙara tabbatarwa daga gareta”
Rungume ta nayi ina hawaye nace.
"Na gode sosai Malama, kema in sha Allahu ke da mijin ki, tsaya mana da kuka yi sai ubangiji ya saka muku ta inda baku zata ba, domin da ace ubangiji bai haɗamu da ku ba ban san wace irin rayuwa zamu faɗa ba.”
" Ba komai Bahiyya ki koma ciki, dare yayi sai da safe in sha Allah, go be ma ba zan fita school ba, nan zan zo in sha Allah sai muga yadda za'a yi”
Daga haka mukayi sallama suka wuce ni kuma na koma ciki...........
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*MI KI KE JIRA NE ER UWA DA HAR YANZU BAKI YI PAYMENT BOOK ƊIN BAHIYYA BA??? ZANEN ƘADDARAR SU NE ZAI SOMA DAGA LOKACINDA AKA DASA SPERM ƊIN FAROOQ DA ƘWAN HANIFAH A MAHAIFAR BAHIYYA WANDA AKE KIRA SURROGACY A KIMIYANCE.WAI MIYE DALILIN SURROGACY ƊIN NE? DALILIN RASHIN LAFIYA NE?? A'A!! DUNIYA CE KAWAI TAYIWA HANIFAH DAƊI TAKE GANIN ITA SAM BA ZATA IYA HAIHUWA BA DOMIN DAUKAR CIKI DA HAIHUWA DA RENO SUNA CANJA HALLITAR MACE. SHI KUMA FAROOQ HAIHUWA YA KE SO, TO FA!! SHINE TA YANKE WANNAN SHAWARAR SABODA TA NEMAWA MIJIN TA FARIN CIKI, YAYINDA BAHIYYAH TA FAƊA KOMAR HANIFAH IDO RUFE TANA NEMAN KUƊIN DA ZA'A YIWA MAHAIFIYARTA AIKI, TO WANE ALFANU HANIFAH ZATA CIMMAWA? SHIN HAƘAR TA KUWA ZATA CIMMA RUWA KO KUMA TAYI SHUKA NE A IDON MAKWARWA????? KU BIYO NI IN SHA ALLAH TAFIYAR BABU DANA SANI*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA SHA ƊAYA*
BAHIYYA
Kwana nayi ina abu ɗaya wato tunani da zullumi, gaba ɗaya jin nike can ƙasan zuciyata na karaya domin tunda nike ban taɓa nisa da iyayena ba ko sau ɗaya sai yau da na amince da ƙudurin wannan matar, ba wai ina nadamar hakan ba ne a'a, nisantar ahlina da zanyi shine ya tsaya min a rai. Taya zan iya rayuwa babu Mama a tare dani har na tsawon shekara ɗaya? Wace irin rayuwa zan tarar a can? Wai ƙasar waje kamar yadda naji ta faɗa, Hmm!.
Abubuwan da suka yi ta cizon ƙahon zuciyata kenan gashi ina Allah Allah gari ya waye ni dai in ga an biya kuɗin aikin nan an yi mata a lokacin ne hankalinmu zai kwanta.
Kiran sallahr Farin ko a masarrafar sauraro na ya sauka, da sauri na miƙe na ɗoro alwala na zo bayan na kambala raka'atanul Fajr na zauna na yi ta addu'ar samun nasarar aikin Mama da kuma zaɓin mafi alkairi a cikin rayuwar da zanyi ta shekara ɗaya.
Dariya ce ta suɓuce min bayan tunawa da Yarjejeniyar mu ni da Hajiya Hanifah na kalli malama nace.
“To amma kun san wani abu? Ita wannan hajiya Hanifah ɗin sai da mukayi wani sharaɗi a tsakanin mu, cewa wai zan taya ta renon cikinta idan ta haihu sai in dawo gida, nace mata ba matsala, wai harda cewa naje nayi shawara, ban san lokacin da na saka mata kuka ba, nace ba wata shawara ni na amince kawai tazo ta biya mana kuɗin.”
Cikin mamaki Malama tace
“ renon ciki kamar yaya? Ke da ba mijin ta ba taya zaki taya ta renon ciki? Kuma na san dai tana da masu aiki birjik duk basu ishe ta ba sai ke?”
A wauta irin tawa ban kawo komai a raina ba nace.
"Malama kin san halin masu kuɗin nan shegen son jikin tsiya ne da su, kuma mijin dole ya fita wurin sabgoginsa na yau da kullum, to wata ƙila ko ruwa tafi so a bata a baki, ni kuma ba ruwa ba ko wanka tace in yi mata wallahi tsab zan iya ina ruwana..”
Dariya Nuhaira ta fashe da ita tace.
"Kai Aunty Bahiyya wanka fa?”
Nima dariyar nayi nace.
" Wallahi Nuhaira da gaske na ke, ko wanka ta ce in riƙa yi mata zan yi matuƙar buƙata ta zata biya, biyan buƙata ai yafi dogon buri. Su masu kuɗin nan kawai idan tsabar jin daɗi yayi musu yawa haukacewa ma su ke, har a rasa mima za'a yi da kuɗi”
Murmushi Malama tayi tace.
“Abu ɗaya muke fata, Allah ya sa ayi aikin nan cikin nasara ya tashi kafaɗunta ”
Duk muka amsa da amin.
***************
HANIFAH
Bayan fitowa ta daga motar wani farin ciki ne ya lulluɓeta domin ba ƙaramar sa'a ta taka ba. Ainahin dalilin zuwanta gidan Rasi'a shine; bayan fitowar ta daga asibitin Nicholas direct office ɗin Farooq ta wuce cike da farin ciki ta sa mesa ta shaida masa yadda suka yi. Nan fa suka hau daru yace shi sam bai yarda ace Christian ce zata ɗaukar masa cikin ɗansa ba, ai addinin mu ya faɗamana cewa tun a ciki yaro yake fara koyon abubuwa kafin ya fito duniya, kuma ya kan ɗauko halayya da ɗabi'u saboda haka ba zai yi farin ciki ba ace wai ɗansa zai fito daga tsatson da addinin su bai zo ɗaya ba. Matuƙar tana so ya amince to ba zai yarda ayi dashen ɗansu a mahaifar Agnes ba, sai dai a fasa. Wuta sukayi sosai da shi. Ƙarshe cikin fushi ta baro Office ɗin direct ta nufi gidan Aminiyarta Rasi'a don ta koka mata matsalar ta sannan ta nemi shawarar ta akan ina ya kama ta a samo wadda za'a yi wannan aikin da ita. Kwatsam cikin sa'a sai gashi tayi katari da wannan damɓarwar tsakanin Rasi da Mijin ta. Cikin ƙwarewa da iya kanta ta jefi tsuntsu biyu da dutse Ɗaya.
Tasan idan ta faɗawa Rasi manufarta akan Bahiyya a yanda taga tana ƙaunar yarinyar nan ba zata amince ba, amma cikin ruwan sanyi gashi buƙatar ta zata biya. Addu'a take a cikin ranta Allah ya tabbatar da tafiyar su a gobe ɗin shi kenan itakam hankalin ta kwance.
Bayan ta gama nazare - nazarenta ta umurci drivernta akan ya nufi hanyar gida.
Tana shiga cikin sa'a kuwa taci karo da farooq ɗin ya dawo, masallaci ya wuce bai dawo ba sai bayan sallar Isha.
Har ɗaki ta samesa bayan ya fito daga wanka tayi murmushi ta ce.
“Welcome!”
Shima murmushin ya mayar mata yace.
“Thank you Hanifah. Ina kika je ne? Na je har office ɗin ki bakya nan?”
Murmushi tayi tace.
“Ina da wani sauran hutu ne bayan nasan cewa ban cika maka muradin ka ba. Na je neman matar kamar yadda ka buƙata...”
Runtse idanunsa yayi tare da girgiza kai yace.
“Hanifah! Hanifah! You are there stressing your self. Ni fa abun ma ya fara fita daga kaina...”
Cikin shagawaɓewa tace.
“But I have already found the woman, musulma Mai addini kamar yadda ka buƙata. Dan Allah Farooq ka karɓi abun nan da zuciya ɗaya please”
Kafaɗar sa ya ɗaga tare da ware hannayensa alamar shi kenan.
Hugging ɗinsa tayi tare da narke masa tana sakar masa sabbatu, shi kuma daman can in dai Hanifah zata biye sa to yafi ƙaunar wannan rayuwar soyayyar fiye da komai a duniya . Duk son sa da abinci haka suka lalace a wurin suna ta abu ɗaya.
***************
BAHIYYAH
Firah muka sha sosai muna ta tsara yadda zamuyi da likita kamar yadda ya faɗa mana cewa da zaran an samu kuɗin zai shige mana gaba a shirya yi mata aikin. Mama ma jefi jefi ta kan ɗan sako bakinta kaɗan. Gaba ɗaya da ka kalle mu kasan cewa cikin kashi saba'in kashi talatin na daga cikin damuwar mu ya tafi da ikon Allah.
Sai da aka gama sallar Isha mijin malama yazo ya gaida Mama, malama ta faɗa mishi abinda ake ciki ya nuna farin cikin sa yayi mana addu'a sannan suka fita zuwa gida.
A bakin get ɗin asibitin na tsaya nace.
“Malama dama akwai maganar da nike so in sanar miki.”
Tsayawa tayi shi Kuma uncle Idris yayi gaba wurin mashin ɗinsa ya tsaya jiran mu.
Kallon ta nayi tare da marairece murya na riƙe hannun ta nace.
"Malama akwai abinda na ɓoye ban faɗa muku ba. Matar tace ba a ƙasar nan zatayi renon cikin ba kuma dole in amince in tafi tare da ita, to na san idan na faɗa kai tsaye hankalin Mama na iya tashi ni kuma bana son abinda zai ɗaga mata hankali a halin yanzu”
Jinjina kai Malama tayi alamar abin babba ne tace.
"Dole kuma sai tare da ke Bahiyya? Anya zan yarda da wannan matar kuwa?”
Cikin magiya nace.
“Malama dan Allah kada ki ce a'a please, wallahi nayi imani ba zata cutar dani ba, gobe fa da kanta tace zata zo nan, kuma na faɗa miki babbar Aminiyar maman Khadijat ce idan har ba ta kirki ba ce maman Khadijat ba zata haɗani da ita ba. Malama wannan hanyar ita kaɗaice hanyar da zan iya ceto rayuwar mahaifiya, ba zan iya bari wannan damar ta wuce ni ba, domin idan Mama ta mutu wallahi ni kaina rayuwata tazo Ƙarshe, kawai abinda nike so da ke shi ne ki tayani da addu'a kuma ki kula min da Mama ta da Ƙanwata, shekara kamar kwana ce take cikin Ikon Allah zaki ga shekara ta zagayo, in sha Allah kuma zaku same ni mai kiyaye wa”
Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace.
“Bahiyya duk don saboda mahaifiyar ki kika yarda da ɗaukar wannan kasadar, dole zan kirashi da kasada domin ba ki san ina zaki ba kuma baki san mi zaki tarar ba, amma koma minene ina miki fatan tsarin ubangiji a duk inda kike, tunda har saboda mahaifiyarki kika ɗauki wannan nauyin in sha Allah ubangiji zai saka miki da abinda baki yi tsammani ba domin uwa ta sha gaban komai da albarkar ta zaki yi nasara a rayuwar gwagwarmayar ki in sha Allah. Zan kira Hajiya Rasi'a zuwa gobe in sha Allah domin in ƙara tabbatarwa daga gareta”
Rungume ta nayi ina hawaye nace.
"Na gode sosai Malama, kema in sha Allahu ke da mijin ki, tsaya mana da kuka yi sai ubangiji ya saka muku ta inda baku zata ba, domin da ace ubangiji bai haɗamu da ku ba ban san wace irin rayuwa zamu faɗa ba.”
" Ba komai Bahiyya ki koma ciki, dare yayi sai da safe in sha Allah, go be ma ba zan fita school ba, nan zan zo in sha Allah sai muga yadda za'a yi”
Daga haka mukayi sallama suka wuce ni kuma na koma ciki...........
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*MI KI KE JIRA NE ER UWA DA HAR YANZU BAKI YI PAYMENT BOOK ƊIN BAHIYYA BA??? ZANEN ƘADDARAR SU NE ZAI SOMA DAGA LOKACINDA AKA DASA SPERM ƊIN FAROOQ DA ƘWAN HANIFAH A MAHAIFAR BAHIYYA WANDA AKE KIRA SURROGACY A KIMIYANCE.WAI MIYE DALILIN SURROGACY ƊIN NE? DALILIN RASHIN LAFIYA NE?? A'A!! DUNIYA CE KAWAI TAYIWA HANIFAH DAƊI TAKE GANIN ITA SAM BA ZATA IYA HAIHUWA BA DOMIN DAUKAR CIKI DA HAIHUWA DA RENO SUNA CANJA HALLITAR MACE. SHI KUMA FAROOQ HAIHUWA YA KE SO, TO FA!! SHINE TA YANKE WANNAN SHAWARAR SABODA TA NEMAWA MIJIN TA FARIN CIKI, YAYINDA BAHIYYAH TA FAƊA KOMAR HANIFAH IDO RUFE TANA NEMAN KUƊIN DA ZA'A YIWA MAHAIFIYARTA AIKI, TO WANE ALFANU HANIFAH ZATA CIMMAWA? SHIN HAƘAR TA KUWA ZATA CIMMA RUWA KO KUMA TAYI SHUKA NE A IDON MAKWARWA????? KU BIYO NI IN SHA ALLAH TAFIYAR BABU DANA SANI*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA SHA ƊAYA*
BAHIYYA
Kwana nayi ina abu ɗaya wato tunani da zullumi, gaba ɗaya jin nike can ƙasan zuciyata na karaya domin tunda nike ban taɓa nisa da iyayena ba ko sau ɗaya sai yau da na amince da ƙudurin wannan matar, ba wai ina nadamar hakan ba ne a'a, nisantar ahlina da zanyi shine ya tsaya min a rai. Taya zan iya rayuwa babu Mama a tare dani har na tsawon shekara ɗaya? Wace irin rayuwa zan tarar a can? Wai ƙasar waje kamar yadda naji ta faɗa, Hmm!.
Abubuwan da suka yi ta cizon ƙahon zuciyata kenan gashi ina Allah Allah gari ya waye ni dai in ga an biya kuɗin aikin nan an yi mata a lokacin ne hankalinmu zai kwanta.
Kiran sallahr Farin ko a masarrafar sauraro na ya sauka, da sauri na miƙe na ɗoro alwala na zo bayan na kambala raka'atanul Fajr na zauna na yi ta addu'ar samun nasarar aikin Mama da kuma zaɓin mafi alkairi a cikin rayuwar da zanyi ta shekara ɗaya.