← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 23

Sashe 14

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gefen yagalallen hijabi na na saka na share sabbin hawayen da suka gangaro min nace.

“Dan Allah Mama ki daina zancen mutuwar nan, wallahi a duk lokacin da kika ambaci mutuwa ki na mugun ɗaga min hankali. Shekara ɗayar nan da mukayi babu Baba ki duba yadda Rayuwa tayi mana juyin masa, Ina ga ace kema babu ke, duk kika tafi ki ka barmu Mama baki yi mana adalci ba, wallahi baki yi muna adalci ba, Ina kike so muje....”

A hankali Mama tace.

“Kayya Bahiyya! Ta Allah ai itace haƙƙun...”

Hannun ta na riƙe na kalleta nace.

“Na sani Mama, amma in sha Allah ba zaki mutu ba, sai mun samu kuɗin aikin nan an yi miki kin tashi da yardar Allah”

"Allah yasa haka Bahiyya, na gode, Allah yayi muku albarka”

“Amin Mama, dan Allah ki daina godiyar nan Mama”

Wani irin ƙarfi ne naji ya shige ni, duk wata yunwar da nikeji naji ta bar ciki na, miƙewa nayi ba tare da na san ina na nufa ba na fito daga cikin asibitin nayo kan titi. Lokaci guda tunani ya harɓa a ƙwakwalwa ta na cewa in tafi gidan Maman Khadijat mana, ai sati ɗaya ne tace zata yi nasan yanzu ta isa dawowa ko ban samu duka ba na ɗan rage wani abu ai zai fi.

Kai tsaye na yiwa gidan Maman Khadijat tsinke, a bakin gate ɗin unguwar su aka tare ni domin ban taɓa zuwa nikaɗai ba sai tare da malama da roƙo da magiya da komai na samu aka yi nasarar yin waya gidanta jin an ambaci sunana suka barni na tafi.

Ina shiga maman Khadijat ta tsuramin na mujiyarta ko ƙyaftawa babu. Bayan ta gama kallona murya a karye tace.

“Bahiyya what happened to you? Kin ganki kuwa?”

Ban tsaya nauyin baki ba na feɗe mata tun daga biri har wutsiya ban rage mata komai ba, a ƙarshe na fashe mata da kuka ina magiya nace.

“Ki yiwa Allah maman Khadijat ki taimakeni kamar yadda Allah ya taimakeki ki taimaka mana da ko nawa ne Allah ya hore miki.”

Guntun hawayen da ya sauko mata ta share tare da tasowa daga inda take zaune ta ɗago ni tsaye tace.

“share Hawayen ki Bahiyya, in sha Allah daga yau matsalar ku ta ƙare har abada, ni zan biya miki duka kuɗin in sha Allah, fatar mu ubangiji Allah ya bata lafiya yasa ayi aikin cikin nasara”

Bansan lokacin da na kai mata wata iriyar cakuma ba, na riƙe ta gam ina ta sabbatu wanda ni kaina ban san mi nike cewa ba.

Daga ƙarshe ta janye jikinta tace.

“Zauna ina zuwa yanxu”

Mai aikinta ta saka ta kawo min lafiyayyen abinci tace in cinye tana zuwa in bari ta shiga ta shirya ta fito mu tafi. Ni kam jin matsala ta tazo ƙarshe na zage na cinye abincin ras na kora da ruwan lemu.........

*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*FREE PAGE*
*BABI NA TARA*

BAHIYYA

..................... Tunda Maman Khadijat ta fito ni ke kallon ta. Kallo ne mai cike da abubuwa masu yawa waɗanda suka tsaya min a rai na masu wuyar fassarawa, ban san ma wacen irin kalar ƙauna zance ina yiwa wannan baiwar Allah ba, domin ta yi min abinda har in koma ga Mahalicci na bazan daina gode mata ba. Jin nike bayan Uwar da ta haife ni da Nuhaira babu kuma wani makusanci na kusa da zuciya ta wanda yafi ta. Allahu ya sani daman can ina ƙaunar ta sai gashi kuma yau ta yi min abin alherin da baki ma ba zai iya magantuwa ba wurin gode mata, sai dai in yi ta yi mata addu'ar gamawa da duniya lafiya don bani da wani abinda zan bata wanda yafi wannan.

“Bahiyya let's go mana, Wai mi kike tunani haka?”

Cewar maman Khadijat ganin na shagala da kallon ta duk inda ta wulga tamkar naga farin wata ɗan goma sha bakwai.

Miƙewa nayi ina mai share guntun hawaye na nace.

“Ba komai maman Khadijaht na gode sosai”

Murmushi kawai tayi ta girgiza kai tare da yin hanyar waje nima na rufa mata baya.
Motar ta muka shiga mai sanyin daɗi, dani da ita duk baya muka shiga yayin da driver ya shiga gidan gaba.

Yana cikin warming ɗin motar sai ga wata rantsatstsiyar motar ta kunno kai cikin gidan a raina ina mamarin ganin wanene wannan da zai fito a cikinta.

Da sauri naji maman Khadijat tace.
“Wait.. Wait Ishaq”

Daga haka ya kashe motar ita kuma ta sauka tana cewa.

“Bahiyya fito ku gaisa da baban Amed shine ya dawo”

Kallo ɗaya na yi masa na gasgata zancen ta domin ba ƙaramin kama suke yi da Ahmad ɗin ba, mutumin ya haɗu ba ƙarya.

Har wurin motar naje bayan ya fito na duƙa har ƙasa na shiga gaishe sa.
Cikin ɗaure fuska ya tanka min tamkar wadda akace ta yi masa wani laifin. A raina nace shi kuma kalar tasa fuskar kenan.

Komawa na yi daga nesa da su na juya fuska ta su kuma suka ci gaba da magana ƙasa ƙasa. Bayan kusan mintuna goma na ji muryar maman Khadijat tana faɗin.

“Bahiyya shigo ki jirani ina fitowa yanzu”

Ba tare da wani tunani ba na bi bayan su na shige farlourn da muke zama zaman yin kitso ina jiranta ita kuma suka shige ciki.

Ruwa taje ta kawo masa da lemu as usual tace.

“Ka fara shan ruwa tukun Baban Amed, sai muyi maganar.....”

Wayar shi ya ajiye a gefensa in da yake zaune ya kalle ta yace.

“Sweetheart ba wani ruwan da zan sha, ko na sha ruwa ba wata maganar kawai ba zaki biya wannan kuɗin ba fa gaskiya”

Cike da mamaki ta kalle shi tace.

“But baban Amed why? This poor girl need help badly, why won't I help her since Ina da yanda zanyi?”

Girgiza kansa yayi yace
“Rasi, to tell you the truth the money is too much....”

Cikin nuna ɓacin rai tace.
“But it's my money not yours, I have every right over my wealth...”

Cikin mamaki yace

“Oh! Is that So? You are telling me that is your money not mine...”

Sai yanzu ta fahimci katoɓarar da ta aika ta, cikin sigar rarrashi ta zauna a ƙasa tare da dafa ƙafar sa tace.

“Abdulfatah, na sani cewa ni da abinda duk na mallaka mallakin ka ne, I beg you in the name of God, ka barni in taimakawa mutanen nan dan Allah...”

Ajiyar zuciya ya sauke ya kalle ta yace.

“Rasi'atu, ban hana ki taimaka mata ba, but kuɗin ne sunyi yawa Rasi, 10 million fa, Haba! Da Allah bai sa naga text ɗin na yi saurin garzayowa na zo gidan ba da shikenan sai kije ki narka wannan uwar dukiyar ga wasu mutane waɗanda ma ni ban san su ba..”

“Baban Amed idan kai baka san su ba ai ni na san su, kuma manzon Allah (S. A. W) ya faɗamana a cikin hadith ɗinsa mai girma cewa duk wanda ya korewa ɗan uwansa wani baƙin cikin duniya Allah zai kore masa nasa baƙin cikin ranar gobe alƙiyama. So miye a cikin ten million Baban Amed, ni kaina nafi ƙarfin ta balle kai..”

“Sadaƙallahul Azim! Malama Rasi, ki fahimta, ni fa bance kada ki taimake ta ba, cewa kawai nayi kuɗin yayi yawa and I'm serious about it, zaki iya bata tunda ga 100k har 500k idan kuma ya fi haka to ban amince ba.”

Cikin karyewar zuciya tace.

“Abdulfatah kasan mi manzon Allah (S. A.W) yace ? ;cewa yayi ko wace irin al'umma tana da kalar ta ta fitinar, amma ni fitinar al'umma ta, itace dukiya. Idan ba fitinar dukiya ba miye a ciki don na biya musu kuɗi? Kafi ƙarfinsu na fi ƙarfinsu, Don mun bayar da 10 million miye a ciki Baban Amed??”

Miƙewa yayi yace.

“Mun gama magana Rasi, ban amince ba idan har ni kin yarda mijin ki ne shugaban ki ne”

Wani irin kuka ne ya kubce mata mai ban takaici da baƙin ciki, wai maza miye suka dauki kan su ne? Shi da yake yin duk abinda ya ga dama da kuɗin sa ta taɓa yi masa shamaki a kai ne?

Har ya kai ƙofa da sauri ta waiga tace.

“Baban Amed Kaji tsoron Allah, wannan yarinyar suna da buƙatar taimako, ba wani abin saɓa shari'a ne zan yi ba, ceton rai ne zanyi, Allah ya ga zuciya na da niyyana. Matuƙar muna da rai to jarabawa ba zai taɓa ƙare mana ba kar kayi mamakin hukuncin ubangiji kaima ya zama na ya jarabce ka ta wani hanyar da kake neman wani taimako wanda kai kuma kuɗi basu iya yi maka magani to sai ka yi yaya kenan..?” ko kuma ace Ɗanka Amed ko 'ƴarka Khadijat suna neman wani taimak....”

Cikin ƙaraji yace.

“Stop it! Stop it Rasi'at, kada ki tsaya ki nemawa kan ki zunubi akan wani dalilin ki na banza da wofi har yasa ki kai ga ɓatamin raina in yi abinda bai kamata ba. Na ce ban amince ba, ban amince ba! That's final. And pack all your things we are leaving this country tomorrow morning as early as possible”

Daga haka ya juya ya wuce abin sa ba tare da ya sake bata damar furta ko da kalma ɗaya ba.

Kuka ta ke sosai tamkar ranta zai fita. Wannan abun sam bai yi mata daɗi ba,Abdulfatah bai kyau ta mata ba, to ta ya ya ma zata iya fuskantar yarinyar nan da wannan mummunar magana? Tace mata mijinta ya hana ta ko ya ya?
Bayan ta gama darzar kukan ta mai isar ta ta gama duk wani saƙe saƙen ta taga cewa babu wata mafita dole ta miƙe jiki a saɓule ta fito zuciyarta na wani irin tuƙuƙi tamkar an ɗora ta akan tuƙubar tsire.

Tana shiga farlourn ta suka yi ido biyu da Hanifah. Take taji wani sabon kuka ya ƙwace mata, da gudu taje ta yi hugging ɗinta murya a raunane tace.
Chapter 14 · 0% Book details