← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 23

Sashe 19

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari ko har ƙofar gida wata haɗaɗɗar mota tazo tayi parking wanda kallo ɗaya zaka yi mata ka tabbatar cewa ba daga ƙaramin gida ta fito ba. Tsayuwar Motar da zatayi sanadin canja alƙiblar tafiya ta a idon 'ƴan unguwar mu zuwa sayar da jikina domin karuwanci na biyawa Mama na kuɗin aikin lalurar ta bayan sun san bamu da wannan kuɗin bamu da dalilin su.

Kuka na ke sosai tare da riƙiƙƙe Mama tamkar raina zai fita, yayin da Malama da sauran' ƴan uwa da masu da zuciya ɗaya da masu yi don munafurci suka tsaya suna ta bamu baki, suna neman jin tushen maganar ina zanje. Wanda har suka ƙaraci gulmar su suka gama babu wanda yace musu ga inda zani.

Har na shiga motar sai kuma na fito da gudu na zo jikin mama na ƙara fashewa da kuka ina faɗin.

“Mama dan Allah dan girman Allah Mama ki tsare shan maganin ki a kan lokaci akan kuma ƙa'ida, duk sanda kika ji matsala Nuhaira ta rakaki asibiti mama, kuma ki yimin alƙawarin cewa ba zaki sake shiga wata damuwa ba har abada, ko da ace bamu da kowa mu uku Mama mun wadaci kanmu, a haka muna farin ciki sosai, ki kula da Nuhaira Mama.....”

Daga nan kuma na juyo ga Nuhaira na rungume ta nace.

“Ke ƙanwata marar jin magana da baccin safen da bana so dan Allah ki kula da kanki sosai, ki kula da Mama kinji ko, nayi miki alƙawarin zan saya miki duk abinda kika ce kina so, kamar gobe ne zaku ga na dawo, in sha Allahu”

Daga haka na wuce direct na shige motar ina ta ɗaga musu hannu tamkar wata ƙaramar yarinya har suka ɓacewa gani na.
Bayan mun fito kan Titi malama ta hau ƙara yi min nasiha saboda tare muke ita zata rakani zuwa gidan Hanifah domin su ƙara tabbatarwa cewa a hannu nagari nike.
Nan na roƙe ta cewa dan Allah mu fara bi ta gidan Maman Khadijat in ƙara yi mata godiya kafin na tafi, sai gashi ko munyi nasarar zuwa gidan amma bata nan kamar yadda masu gadi suka shaida mana. Daga nan drivern ya fito ya juya akalar mota zuwa gidan Hanifah.

Tun daga farkon unguwar na fara kalle Kalle domin wannan ba kamar sauran unguwanni ba ce, duk yadda nike ganin unguwar su Maman Khadijat da mugun kyau wannan unguwar ta cuna mata, tamkar ba'a Najeriya ka ke ba, Gate ne gasu nan kala kala, idan mun wuce wannan mu kai ga wannan, ga kaki nan kala da kala duk a matsayin masu gadi.

Ban ƙara tsinkewa da al'amarin ba sai da muka shiga cikin tamfatsetsen gidan kacokam na ƙara tabbatarwa kai na da cewa Lallai yau ni Bahiyya zan shiga wata duniya ta daban.

Kallon malama nayi kamar yadda itama naga take kallo na tare da yimin alama cewa mu fita.

Jiki na take ya hau karkarwa tamkar ana kiɗamin mazari ta dalilin tozali da nayi da wasu shirga shirgan samudawa waɗanda babu alamun wasa a tare da su sun ƙaƙƙame tamkar wasu sandararrun gunku na................

                             *OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

               *BY*
*AMINA IBRAHIM*
  *(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*FREE PAGE*
     *BABI NA GOMA SHA UKU*

........... Wani ƙayataccen falour ne na alfarma akayi mana masauki muka zauna, ni dai ko a nan a darare ni ke zaune, Malama ce ma naga ta saki jiki sai aikin kalle kalle take.

Jiga jigan hotuna ne kala da kala ita dai Matar gidan kallo daya nayi mata a wani hoton na gane ta, sai dai hotunan maza ne biyu na gani ba zance ga mai gidan ba.

Bayan malama ta gama ƙare musu kallo ta kalle ni cikin mamaki tace.

“Bahiyyah kin san nan ko gidan waye?”

Girgiza kai na kawai nayi alamar ban sani ba.

Gyaɗa kai tayi tana mai ƙara jinjina girman al'amarin tace.

“Daman farkon tozali na da ita raina ya bani cewa kamar ita sai dai girma da matsayi irin wanda take da shi shine ya hana zuciya ta amincewa da cewa ita ce, to ashe ita ɗin ce. Babbar 'ƴar kasuwa ce, ita ce mammallakiyar Ɗan-Ali Decor and Event wanda ake ji da shi a faɗin ƙasar nan wanda bata jima da sake buɗe reshenta a United Arab Emirate ba,Mahaifinta shahararre ne kuma sananne yanzu haka Ambassador ne a ƙasar Cairo , mijinta kuma Umar Farooq mai gishiri shima shahararre ne kuma sannan ne a faɗin waje da kewaye Bahiyya,shi jika ne ɗaya tilo ga Madinat shahararriyar mai kamfanin Almadinah textile and more da ke da rassa daban daban a faɗin ƙasar nan da kewaye....”

Ajiyar Zuciya ta sauke sannan ta kalle ni jiki sanyaye tace.
“Ban san wace kalar ƙaddarar ce ta haɗaku ba Bahiyya,Don wannan haɗuwar taku da ƙaddara zan kira ta, na san ba don tana neman komai daga gare ki ba sai dai don tayi niyyar ta taimaka miki kawai because you have nothing to pay her in return, banga abinda zaki bata ba a duniyar nan domin tafi ƙarfin ki ta ko ina, in ma masu aiki ta ke nema nasan dole sai masu kwalin karatu mai zurfi don ko a gidan hajiya Rasi'at da bata kai ta ba suma haka tsarin su ya ke. Allah ne kaɗai masanin abinda yake zuciyarta akan neman ki da tayi ɗin nan har na tsawon shekara ɗaya, abinda zan faɗa miki na ƙarshe shi ne Bahiyyah ki tsare mutuncin ki komai wuya komai tsanani, ki yi musu biyayya daidai yadda zaki iya.”

Gyaɗa kaina nayi tare da jinjina girman lamarin a kaina nace.

"In sha Allah Malama zan kiyaye”

Zaman mu a nan munfi 2hours, bayan an cika mu da kayan ciye ciye abinci kala da kala muka ci muka ƙoshi sannan daga baya sai ga wata matashiyar mata da hausarta bata fita sosai ta zo tace mu tashi mu biyo ta. Haka muka yita bin ta mu shiga nan mu wuce nan ko ina gwanin burgewa tamkar duniyar da ba'a mutuwa a cikin ta, sai daga ƙarshe muka isa wani parlour na alfarma mai wani sanyi da ƙamshin rahama mai kwantar da zuciya.

Ko a nan ma sai da muka shafe kusan mintuna talatin sannan sai gata ta iso cikin takun ta na ƙasaita da girma na manyan mata ta samu wuri cikin ɗaya daga cikinsu cikin lumtsatstsun kujerunta ta hakimce.
Tuni ni da Malama muka shiga miƙa gaisuwa ni kuma a zuciyata ina ta mamakin yadda malama ta wani baje a ƙasa tana faman kwasar gaisuwa yayinda ni na san cewa itace ya kamata ace ta gaidata domin ko bata haife ta ba saura kiris.

Murmushi tayi sannan ta kalli Malama tace.
“Na gode”

Murmushin itama Malama tayi tace.
“Ba komai Hajiya, Daman cewa nayi bari na rakota domin in ƙara tabbatar da cewa a hannu na gari zata faɗo, Allah ubangiji ya baki lafiya ya kuma zaunar da ku lafiya”

Murmushi Hanifah ta sake yi hannun ta riƙe da wayar ta tana latsawa ba tare da ta kalle ta ba tace.

“Kar ki damu In sha Allah babu wata damuwa”

“To nayi murna da jin haka, ni zan koma sai Allah ya sake haɗamu da alheri”

Daga haka Malama ta miƙe nima na yunƙura da nufin miƙewa tayi saurin dakatar da ni tace in zauna ba sai na rakata ba, amma fir na ƙi saurarenta Sai da na biyo ta har mota, kaya ne ake ta tula mata niƙi niƙi Wai gashi nan in ji Hajiya, Malama kuma daga gefe sai faman ƙara jaddada min take cewa in bi matar nan sau da ƙafa bata da wata matsala, a raina har abin ya soma bani Mamaki ni dai toh kawai nike kira mata har ta shige mota ta wuce. Hawayen da suka silalo min na goge tare da yin sauri na bi bayan matar nan da ta ɗazu domin ba lallai ne na sake maida kaina wurin ba.

Wani irin tsoro ne ya dirar min a zuciya ta wanda ban san dalilin hakan ba, ko don yanzu ya rage parlourn daga ni sai ita ne Oho! Tunda na zauna bata sake kallon in da nike ba tamkar Allah bai yi ruwana a wurin ba haka tayi min wanda sam banji daɗin hakan ba, ko ba komai atleast ya kamata tace min wani abu don ta nuna tasan cewa ina wurin kai ko kallona tayi ni hakan ya wadatar, amma tayi da ni kashi duk ɗaya wanda maman Khadijat baya daga cikin halayyar ta, shiyasa ni ke sonta.

Ba abin da nike sai tubka da warwara ni kaɗai a cikin zuciya ta, daga ƙarshe na ɓige da tunanin Mama da Nuhaira wanda ba san lokacin da Hawaye suka shiga kwaranya daga cikin idanuwa na ba. Bayan na gama hawayena na tsayar da su don kaina, sai na sake ɗago kaina da nufin sake kallon wannan ishashshiyar matar sai dai wurin wayam ba kowa ban san lokacin da ma ta tashi tayi tafiyar ta ba, wasu sabbin hawaye ne suka sake zubomin raina ya hau wani ƙuna kamar in tashi in tafiya ta gida. Ina nan na zuba ma sarautar Allah ido sai ga wannan matar ta ɗazu ta sake dawowa ta kalle ni da sakin fuska tace.

"Oya ta shi ki biyo ni”

Ba musu na tashi na bita tamkar wasu akala da raƙumi har muka kai wata killatattar ƙofa haka duk a cikin rufi ɗaya. Shiga tayi nima nabi bayan ta.

Parlour ne mai kyau wanda ke ɗauke da set ɗin cushion ash and black, komai na parlourn haka kalar take komai an jerashi a tsari. Baki na saki kawai ina bin ko ina da kallo kamar wata wawiya.....

“Nan shi ne in da zaki zauna...”
Chapter 19 · 0% Book details