← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 23

Sashe 15

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Hanifah why is men like this? Su Idan suna son abu babu mai hanasu sai amma idan kai ne ka ke son abu kai da abun ka su nuna maka fin ƙarfi”

Cikin rashin Fahimta Hanifah tace.

“Me I don't understand you, can you made your self clear please?”

Zaunawa tayi ta gaya mata komai da ya wakana tsakanin ta da Bahiyya da kuma irin rashin mutuncin da Baban Amed ya gurza mata. Ƙarshe tace.

“Kin ma san wani abun takaici Hanifah? I'm 6weeks pregnant, cikin ɗoki yace min dole zai zaɓi wata ƙasar mai daɗi muje muyi renon cikin a can har na haife sai mu dawo na ce masa ban amince ba ya bari dai idan cikin ya kai term sai mu tafi,shine yace ya amince amma idan muka tafi sai babyn ya kai 2years zamu dawo nace na amince nima, a haka muka tsaya amma wai shine don yayimin baƙin ciki wai yanzu yake faɗamin in shirya gobe zamu bar ƙasar.”

Cikin Mamaki Hanifah tace.

“Ke ma dai Rasi kina bani mamaki wallahi yadda kike iya tolerating nonsense ɗin namiji, kuɗin sa ne? In da ace kuɗin sa ne don ya hana ba matsala ba ne...”

Wani murmushin takaici Rasi ta saki wanda yafi kuka ciwo tana girgiza kai tace.

“Hmm! Up to now you don't know men Hanifah, but bet me, one day one time sai namiji ya gurza miki watarana I promise you this, a lokacin zaki gane cewa maza maza ne kuma ba zaki iya yin komai ba a wannan lokacin, shiyasa nike gayamiki kiyi amfani da damar ki tun kina da lokacin ki”

Dariya ce ta suɓucewa Hanifah tace.

“Rasi, for get about it because wannan ranar ma ba zai taɓa zuwa ba”

“Hanifah bazan kira ki da yarinya ba, 8years in marriage kin wuce a ce baki san minene aure ba. while I don't blame you Saboda ba rayuwar auren tsantsa kike practicing ba daga ke har mijin ki baku san ma daɗin auren ba. But idan kika shirya rayuwar auren ta gaske watarana zaki ce na faɗa miki haka”

Taɓe baki Hanifah tayi tace.

“Rasi! yanzu dai duk abinda kike so nima shi nike so, tunda har Abdulfatah ya katangeki daga taimakon wannan yarinyar, me I will do that Ko don na kare miki mutuncin ki daga idon ta”

Cikin tsantsar farin ciki Maman Khadijat tace.

“Thank you, thank you Hanifah, wallahi ban san taya ya zan iya gode miki ba, thank you so much”

“Mention not Rasi, kinfi haka a wurina, tunda kin ƙi ki kore ta ya na iya, dole in so abinda kike so”

Rungume ta tayi tace.
"Naji dai, thank you matar Farooq.... Oya! Tashi muje bana so a tsaya wani jinkiri kuma kada wani abu yazo ya biyo baya”

***************

BAHIYYA

Tun ina zaune har sai da na kai ga gincirawa ba tare da na kawo komai a raina ba na zauna zaman jiranta, tunda har mijinta ne dole na san zata tsaya sai ta gama da shi sannan tayi ta tawa. To kuma ina nan zaune sai naga Ƙawarta ta shigo, hakan yasa na ƙara gyara zama domin na san dole itama sai ta bata time ɗin ta kafin ni.

Ganin har lokacin sallar Asr yayi yasa na miƙe naje na ɗoro alwala na zo na gabatar da sallah. Ina zaune Ina addu'a suka shigo tare da ƙawar ta ta.

Gaishe su na ƙara yi tare da baza kunne ina jira in ji tace na tashi mu tafi,sai dai ganin sun samu wuri sun zauna yasa ni jin wani abu ya ɗan ɗarsu a zuciyata.

“Bahiyya!”

Ɗagowa nayi na kalli Maman Khadijat nace

“Na'am”

“Tun ɗazu ina ciki da Baban Amed banki na yaƙi ya fitar da wannan kuɗin mai yawa, nayi ta gwadawa yaƙi bayar da haɗin kai shi yasa kika ga na jima ban fito ba, amma Alhamdulillah! Ga Ƙawata nan Hanifah in sha Allahu zaku tafi tare ita ce zata biya kuɗin babu wata matsala”

Rusunawa nayi inata gode musu wanda har sai dai Maman Khadijat taji tausayi na ya ƙara sarƙafe mata zuciya. A hankali tace.

“Bahiyya ba buƙatar duk wannan please, fatanmu dai shine Allah ya bata lafiya....” Sai kuma tayi murmushi tace.
“Bahiyya kin san ɗan Adam da kuɗi, tunda kuɗin nan yaƙi fita a banki na naji Zazzaɓi yazo ya kamani lokaci guda, bana jin daɗi jikina a yanzu ba zan iya fita ba, saboda haka kice ina gaida maman ku kinji ko, Allah yasa ayi cikin nasara. Tashi kuje”

Duk da cewa ban san abinda ke faruwa ba, wani irin abu naji mai sanyi ya mamaye zuciyata da gudu naje na ƙanƙame maman Khadijat ina ta rusa kuka tare da sakin sabbatunda ni kai na ban san mi nake cewa ba.

Daga haka muka tashi muka tafi a motar wadda ta kira da Hanifah.
Har muka isa asibitin ni da ita babu wanda yayi magana kowa da irin abinda ya ke saƙawa a cikin ransa.

Bayan mun isa bakin asibitin na miƙa hannu da nufin buɗe motar tace min.

“Dakata, akwai maganar da nike so muyi da ke..............”

*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA*

........... Kafeta nayi da Fitilun ganina tamkar zan karanto wani abu daga allon fuskar ta.

“Daina kallo na haka da waɗannan idanuwan naki”

Jin ta furta haka a gare ni yasa nayi saurin saukar da idanuwana ƙasa da sauri kamar yadda ta umurceni, a can ƙasan raina kuma sai naji wani iri domin kalmar tayi min kama da ta muzantawa duk da cewa ban san abinda yake ranta ba.

Mun jima shiru kafin ta iya buɗe bakinta tamkar wadda aka tilasta akan dole sai ta yi min magana tace.

“Zan biya kuɗin aikin Mahaifiyarki kamar yadda Rasi tayi miki alƙawari, but sai dai ina da wata 'ƴar ƙaramar buƙata zuwa gare ki, idan kin amince fine, zan biya ko da sun kai million ɗari ne ba tare da ɓata lokaci ba...”

Ban tsaya nauyin baki ba kaina na ƙasa tunda ba taso na kalle ta nace.

“Zanyi koma mine ne kika buƙata muddin zaki biya kuɗin aikin mahaifiyata, ita kaɗai ta ragemin a duniya sai ƙanwata”

Gyaɗa kai tayi tace.

“While, ba wani abu bane mai wahala, kawai dai zaki tayani renon ciki ne zuwa wata tara daga zaran ya fito duniya sai kiyi tafiyar ki kawai aikin ki ya ƙare...”

Cikin azama na tare numfashin ta nace

“Na amince! in don ɗan waɗannan aikin ne tabbatas na amince”

Murmushi tayi wanda har sai da na jiyo sautin sa sannan tace.

“Ki dai ƙara tunani, kije kuma ki yi shawara na baki daga nan zuwa jibi....”

Hawayen da suka zamomin abokan rayuwata ne suka fara zarya akan kuncina, girgiza kai na na fara yi ina magiya nace.

“Dan Allah Hajiya ki taimaka min, in dai akan mahaifiyata ne babu wani tunanin da zan tsaya yi, duk da yanzu cewa an ɗora ta akan magani likita ya gayamin cewa rayuwar ta tana cikin haɗari aikin nan da wuri shine maslaha, bana son in rasa mahaifiyata dan Allah ki bada kuɗin ko aikin da yafi wannan ne ni na amince miki zanyi matuƙar zaki biya mata kuɗin aikin nan, kuma zan yi ta gode miki har in koma ga Allah ba zan manta da alherin ki gare ni ba”

Ajiyar zuciya ta sauke a hakankali tace.

“Shi kenan. Gobe da safe zan zo, amma Kuma aikin namu ba a nan ƙasar zamu zauna ba ƙasar waje ne zamu tafi”

Daga haka naji ƙofofin motar sun ce ƙitt! Alamar cewa sun buɗe daga nan na buɗe tare da ƙara yi mata godiya na sauka cikin tsantsar farin ciki na shige cikin asibitin.

Ina shiga na cimma Malama ta kawo abinci kamar kullum,Daman bayan ta taso daga makaranta idan mai aikin ta tagama girki sai ta shirya ta wuto asibitin tare da abincin.

Spoon ne riƙe a hannun Nuhaira tana bawa mama da ke jingine jikin pillow abinci a hankali tana mai ƙureta da kallo. Jin sallama ta yasa duk suka juyo, Nuhaira da malama suna rige rigen tambaya ta ina na shige duk yinin yau, domin ban faɗamusu in da zanje ba.

Da sauri naje na karɓi spoon daga hannun Nuhaira nace.

“Bani spoon ɗin Nuhaira, duk yinin yau ban hidimta mata da komai ba, bani ko wannan ladar na samu.”

A hankali na shiga bata abincin tana mai kafeni da ido wanda nasan ko bata furta ba itama tambaya ta take daga ina nake.

Kauda kanta da tayi shi ya bani tabbacin cewa abincin ya ishe ta daman ba wani abun kirki ta ke ci ba. Ruwa na bata sannan na tambaye ta ko akwai abinda ta ke buƙata, girgiza kanta tayi alamar ba komai sannan na miƙe na tattara kayan na dawo.
Gajen haƙuri ne yasa malama sake jefomin tambayar daga ina na ke.

Zaunawa nayi ina mai sakin sassanyar murmushi na kalli malama nace.

“Malama kin san daga ina na ke kuwa?”

Tsuromin na mujiyarta tayi tare da girgiza kanta alamar a'a.

Nace.
“Gidan Maman khadijat naje”

Cike da mamaki tace.

“Gidan Maman Khadijat Bahiyya! Kina nufin gidan Hajiya Rasi'a?”

Gyaɗa kaina nayi nace.
“Eh malama. Wallahi ko da na bar asibitin nan ɗazu bansan ina na nufa ba, sai daga baya tunanin zuwa gidanta ya ɗarsu a zuciyata....”

Nan na shaida musu duk yadda nayi da maman Khadijat da kuma wadda muka zo tare da nufin gobe zata zo ta biya kuɗin aikin baki ɗaya.

Kabbara Nuhaira ta ɗauka tare da zuwa ta ƙanƙameni ta saki wani kukan farin ciki tana mai faɗin

“Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! Haƙiƙa dukkan wani tsanani yana tare da sauƙi Aunty Bahiyya da yardar ubangiji, waɗan nan mutane Allah ubangiji ya saka musu da mafificin alkairi. Amin.”

A hankali Mama ta runtse idon ta hawaye na sauka daga gefen kuncin ta, bakinta sai motsawa yake tana ta jera kabbara da yabo da nuna godiya a wurin Allah.
Malama itama rungume ni tayi cikin farin ciki tace.
Chapter 15 · 0% Book details