Sashe 8
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Da farko ina baka haƙuri Farooq, kasan wasu matan basu san abinda ya kamata ba sai an lurar da su suke ganewa, kayi haƙuri Kayi ta lallaɓata kana nuna mata hanya in sha Allah watarana zata fahimce. Abu na biyu kuma shawarar da zan baka nasan ba lallai ne tayi daidai da ra'ayin ka ba, amma Ina mai baka shawara zama a haka ba zai sa ku samu ci gaba a rayuwar auren ku matuƙar ba haihuwa kuka yi ba, wato Farooq ina so kasan wani abu, ɗaukar cikin ɗanka da mace zata yi har ta haife shi yana ƙara muku bonding da kafa wata ƙauna ta musamman ko don 'ƴa' ƴan nan. Duk wannan borin da take yi maka daga zaran kun in sha Allah zaku samu fahimtar juna da ita, sannan kuma Farooq ko don tsohuwar nan ya kamata ka tausaya mata ta samu yaran da zatayi wasa da su kafin ta koma ga Mahaliccin ta, zata yi matuƙar farin ciki. Dan Allah kayi tunani Farooq I'm not forcing or commanding, ni kawai Mai bayar da shawara ne. Yara farin ciki ne, rahama ne Farooq.”
“Sannan abu na gaba Farooq, Wayewar Hanifah tayi yawa, wallahi idan baka yi wasa ba sai kun shiga wutar Jahannama domin kuwa ku musulmai ne, kasani a cikin Alƙur'ani mai girma Allah yace ku tsare kawunan ku da iyalanku daga shiga wuta. Farooq ji irin shigar fitsarar da matarka take yi ta gaisa da wannan namijin ta rungumi wannan namijin duk da sunan wayewa. Ka riƙa yiwa matarka nasiha kana gayama ta gaskiya domin ku tsira ranar gobe alƙiyama”
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA SHIDA*
Jingina bayan sa yayi a jikin cushion ɗin tare da lumshe idanunsa relaxing himself yana digesting shawarar da Mahi ya basa.
Shi kuwa Mahi ganin ya ƙi ce masa komai yasa ya miƙe tsaye yace.
“Ni zan tafi I'm leaving to Ghana in sha Allah, kai kuma sai ka shirya kayi scheduling time ɗinda zaka gana da mutanen nan da na faɗa maka sun iso tun shekaranjiya, sunce ba za su gana da kowa ba sai kai”
Daga haka ya juya ya fice daga gidan.
Farooq kuwa yafi hour a haka duk wanda ya gansa zaiyi tunanin cewa bacci yake nan ko ba baccin da yake kawai matsalolin gidan sa yake ta lissafi yana neman hanyar warware su.
Miƙewa yayi ya shiga ɗakin da Madinah ta ke, gefen window ya sameta tana tsaye tana kallon waje amma ganin quick action ɗinta tana goge Hawaye ya tabbatar masa da cewa kuka take, cikin mamaki yace.
“Wai Madinah minene? Why have you been crying since yesterday ? da na san cewa tilas taki ki amsamin tamboyoyin zai sa ki yi ta kuka da na haƙura kawai,ko dai akwai wani abin ne bayan wannan ? Please idan har kina da wata damuwa just tell me”
Matsawa yayi in da ta ke tsaye ya rungumeta cikin nuna kulawa yace.
“Madinah Farukun ki ne idan akwai wani abu dan Allah ki faɗamin, idan ina ganin ki kina kuka zuciya ta ba zata iya daurewa ba”
Murmushi tayi tace.
“Haba ba fa komai, kawai dai tunawa da nayi da Azizat da Modu ne yasa zuciya ta ta kasa daurewa”
Cikin tausayawa yace.
“Nasan ba zan taɓa fahimtar yadda kike ji ba domin ke kika rayu tare da su ke kika san zafin su da muhimmancin su a rayuwar ki, to amma ni kuma da na san ke kaɗai ce rayuwa ta dole zan damu idan kina cikin wata damuwa, kiyi haƙuri”
“Na gode Umar”
Sake tambayar ta yayi yace.
“But Grand Ma, is that only my Mom you gave birth to?”
Gyaɗa kai tayi alamar eh sannan tace.
“Bayan haihuwar Azizat nan ma wata Azal ɗin ce ta sake faɗamana ni da Modu, bayan wata shida da haihuwar ta na je wajen wani spiritualist shima daga garin mu Enugu ya fito na san shi tun daga gida, buƙata ta na faɗa shi akan ina son maganin tsayar da haihuwa kafin yarinya ta ta girma saboda bana so inyi ciki da goyo, ya tambayeni sunan Mijina da kuma sunan da na canja nima na faɗa mishi, daga nan ya tashi ya shiga wani bukka sai da ya ɗauki lokaci ya fito ya ce min an gama aiki,aikin na binnewa a cikin ƙasa saboda haka duk lokacin da na ke buƙatar haihuwa in zo daga zaran an to ne shikenan. Hmmm! Faruku ban sake komawa wurin mutumin nan ba sai da Azizat ta cika shekara biyar cif a duniya, ko da naje na riski labarin da har in koma ga Mahalicci na ba zan manta da shi ba, domin kuwa ko da naje mutumin ya mutu shekara biyu da suka wuce, wurin nashi ma gaba ɗaya an rushe shi anyi gini kamar bai zauna a wurin ba. Kuma asirin an riga an binne sai idan an tone zan iya sake haihuwa, to kaji yadda mahaifiyarka ta kasance a gare ni ita kaɗai, nayi kuka nayi kuka har na gode Allah na riga na aikata kuskuren da ba zai gyaru ba, a duk lokacin da naga abokanan hulɗa ta da yara fiye da uku huɗu sai na ji zuciya ta ta tsinke in yi ta kuka ina istigfari. Hakan yasa ni da kakan ka muka ɗauki son duniya muka ɗorawa Azizat bayan ta mutu kusan zaucewa na kusa yi, hakan yasa da soyayyar kaka da jika da kuma soyayyar mahaifiyarka duk muka haɗa muka baka har Modu ya mutu ya bar mu daga ni sai kai”
A labarin jiya da ta bashi bai ji abinda ya girgiza shi irin na yau ba, haƙiƙa ya tausayawa wannan tsohuwar matuƙa.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su bayan some minutes ya ce.
"I'm so sorry Grand Ma”
Murmushi tayi tace.
“thank you. Ka je ka shirya ka zo ka kai ni gidan Victoria nayi mata alƙawarin watan watarana zan zo tare da kai idan damar hakan ta samu”
“Wace Victoria?”
“She's my old friend since from child hood we were from the same state”
"OK.”
Bayan ya gama duk abinda yake suka shirya around 12:00pm suka bar gidan.
Sun samu tarba mai kyau gidan da suka je, sai 4pm suka dawo.
Madinah tayi hakan ne domin ta rage masa damuwar da take damun sa, Mahi yayi mata duk bayanin da yake ciki to amma ba zata shiga al'amarin gidan sa ba, zata dai taya shi da addu'ar da ta saba yi masa kullum, kuma shi ma bai damu da ya sanar mata ba saboda duk lokacin da ya mata lodging wani complain tsakanin shi da Hanifah sai dai ta ba shi haƙuri tace yayi haƙuri Hanifah yarinya ce watarana zata daina.
A haka tayi ta ɗau ke masa hankali suna yawon kai ziyara na tsawon kwanaki daga baya kuma ya warware ya koma Office, amma Kullum kwanan duniya da matarsa yake kwana a rai da ita yake tashi.
***********
BAHIYYA
A 'ƴan watannin nan na samu kuɗi ba laifi domin Malama Rabi ta sama min customers da nike wa aikin lalle da kitso sun fi a ƙirga kuma kowa da kalar irin biyan da yake min na karamci. Hakan yasa muka haɗa kuɗi kusan dubu saba' in Mama ta baiwa Malama akan mu tafi tare a samu makaranta private dai dai da matsayin mu a sanya Nuhaira kafin zuwa wata shekara ni kuma a biya min kuɗin WAEC.
A ta dalilin rashin samun Baba Maharazu a waya shine sanadiyyar da Malama ta shiga gaba gaba aka yiwa Nuhaira komai har uniform har komai ya kama kuɗi dubu saba'in da huɗu termly kuma Dubu ashirin da biyu. Ss1 to Ss3.
Malama ta kasance maƙociyar mu ce tunda muka dawo nan garin Kaduna Road suka haɗu da Mama, da ita da mijinta duk malaman makaranta ne suna da yara huɗu, bariki ba kamar gida ba ne namiji zai bar matarsa ita ma ta fita ta nema domin su taru su rufawa juna asiri matuƙar zata iya, hakan yasa Malama bayan aikin koyarwa ta shiga hulɗa da mutane daban daban tana kai kayan mata cikin gari da kuma sauran State tana kuma da shago ƙofar gidanta. Ta iya kanta sosai shiyasa duk yadda kake tana iya zama da kai tana kuma da kirki irin nata.
Sanadiyyar komawar Nuhaira school yasa aiki ya taru ya min yawa ni da Mama in kuma na fita cikin gari ita kaɗai tayi ta wahala shiyasa na nema mata almajiri mai taimaka mata.
Yauma haka nayi ta bada kayan miya idan an kawo niƙa kuma in tashi in yi domin Mama ta ɗan fita unguwa, ƙarfe uku nayi na yamma na shirya na fita islamiyya nabarwa Sharifu almajiri sauran aikin kafin Nuhaira ta dawo daga school domin sai uku da rabi suke tasowa kafin ta iso gida kuma huɗu tayi shiyasa take zuwa islamiyya yanzu a makare.
Ko da muka shigo gida ana kiran sallar magrib ganin banga mama a waje ba na shiga ɗaki na tadda ta kwance a duƙunƙune da sauri muka isa gareta ni da Nuhaira muna rige rigen tambayarta mike damun ta,ko iya ɗaga kanta ba tayi hakan yasa hankalinmu ya tashi sosai na cakumota da ƙarfi nace.
“Mama mi ne ne? Mi ya same ki?”
Sai tin zuciyar ta ta shiga nuna min da hannu alamar nan ne yake mata zafi. Cikin ruɗewar kuka nace.
“InnaLillahi! Wannan ciwon zuciyar ya matsa miki Mama. Tashi ki daure mu tafi chemist, yau da ke zan tafi domin ya duba ki.... Nuhaira ɗauko mata hijabi da mukulli mu tafi”
Da sauri Nuhaira tayi yanda nace muka rufe gidan a hankali muka lallaɓa da ita wanda ko a chemist ɗin kasa zaunawa tayi sai da na zauna ta kwanta a jiki na. Tambaya ta mutumin yayi mike damunta.
“Sannan abu na gaba Farooq, Wayewar Hanifah tayi yawa, wallahi idan baka yi wasa ba sai kun shiga wutar Jahannama domin kuwa ku musulmai ne, kasani a cikin Alƙur'ani mai girma Allah yace ku tsare kawunan ku da iyalanku daga shiga wuta. Farooq ji irin shigar fitsarar da matarka take yi ta gaisa da wannan namijin ta rungumi wannan namijin duk da sunan wayewa. Ka riƙa yiwa matarka nasiha kana gayama ta gaskiya domin ku tsira ranar gobe alƙiyama”
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA SHIDA*
Jingina bayan sa yayi a jikin cushion ɗin tare da lumshe idanunsa relaxing himself yana digesting shawarar da Mahi ya basa.
Shi kuwa Mahi ganin ya ƙi ce masa komai yasa ya miƙe tsaye yace.
“Ni zan tafi I'm leaving to Ghana in sha Allah, kai kuma sai ka shirya kayi scheduling time ɗinda zaka gana da mutanen nan da na faɗa maka sun iso tun shekaranjiya, sunce ba za su gana da kowa ba sai kai”
Daga haka ya juya ya fice daga gidan.
Farooq kuwa yafi hour a haka duk wanda ya gansa zaiyi tunanin cewa bacci yake nan ko ba baccin da yake kawai matsalolin gidan sa yake ta lissafi yana neman hanyar warware su.
Miƙewa yayi ya shiga ɗakin da Madinah ta ke, gefen window ya sameta tana tsaye tana kallon waje amma ganin quick action ɗinta tana goge Hawaye ya tabbatar masa da cewa kuka take, cikin mamaki yace.
“Wai Madinah minene? Why have you been crying since yesterday ? da na san cewa tilas taki ki amsamin tamboyoyin zai sa ki yi ta kuka da na haƙura kawai,ko dai akwai wani abin ne bayan wannan ? Please idan har kina da wata damuwa just tell me”
Matsawa yayi in da ta ke tsaye ya rungumeta cikin nuna kulawa yace.
“Madinah Farukun ki ne idan akwai wani abu dan Allah ki faɗamin, idan ina ganin ki kina kuka zuciya ta ba zata iya daurewa ba”
Murmushi tayi tace.
“Haba ba fa komai, kawai dai tunawa da nayi da Azizat da Modu ne yasa zuciya ta ta kasa daurewa”
Cikin tausayawa yace.
“Nasan ba zan taɓa fahimtar yadda kike ji ba domin ke kika rayu tare da su ke kika san zafin su da muhimmancin su a rayuwar ki, to amma ni kuma da na san ke kaɗai ce rayuwa ta dole zan damu idan kina cikin wata damuwa, kiyi haƙuri”
“Na gode Umar”
Sake tambayar ta yayi yace.
“But Grand Ma, is that only my Mom you gave birth to?”
Gyaɗa kai tayi alamar eh sannan tace.
“Bayan haihuwar Azizat nan ma wata Azal ɗin ce ta sake faɗamana ni da Modu, bayan wata shida da haihuwar ta na je wajen wani spiritualist shima daga garin mu Enugu ya fito na san shi tun daga gida, buƙata ta na faɗa shi akan ina son maganin tsayar da haihuwa kafin yarinya ta ta girma saboda bana so inyi ciki da goyo, ya tambayeni sunan Mijina da kuma sunan da na canja nima na faɗa mishi, daga nan ya tashi ya shiga wani bukka sai da ya ɗauki lokaci ya fito ya ce min an gama aiki,aikin na binnewa a cikin ƙasa saboda haka duk lokacin da na ke buƙatar haihuwa in zo daga zaran an to ne shikenan. Hmmm! Faruku ban sake komawa wurin mutumin nan ba sai da Azizat ta cika shekara biyar cif a duniya, ko da naje na riski labarin da har in koma ga Mahalicci na ba zan manta da shi ba, domin kuwa ko da naje mutumin ya mutu shekara biyu da suka wuce, wurin nashi ma gaba ɗaya an rushe shi anyi gini kamar bai zauna a wurin ba. Kuma asirin an riga an binne sai idan an tone zan iya sake haihuwa, to kaji yadda mahaifiyarka ta kasance a gare ni ita kaɗai, nayi kuka nayi kuka har na gode Allah na riga na aikata kuskuren da ba zai gyaru ba, a duk lokacin da naga abokanan hulɗa ta da yara fiye da uku huɗu sai na ji zuciya ta ta tsinke in yi ta kuka ina istigfari. Hakan yasa ni da kakan ka muka ɗauki son duniya muka ɗorawa Azizat bayan ta mutu kusan zaucewa na kusa yi, hakan yasa da soyayyar kaka da jika da kuma soyayyar mahaifiyarka duk muka haɗa muka baka har Modu ya mutu ya bar mu daga ni sai kai”
A labarin jiya da ta bashi bai ji abinda ya girgiza shi irin na yau ba, haƙiƙa ya tausayawa wannan tsohuwar matuƙa.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su bayan some minutes ya ce.
"I'm so sorry Grand Ma”
Murmushi tayi tace.
“thank you. Ka je ka shirya ka zo ka kai ni gidan Victoria nayi mata alƙawarin watan watarana zan zo tare da kai idan damar hakan ta samu”
“Wace Victoria?”
“She's my old friend since from child hood we were from the same state”
"OK.”
Bayan ya gama duk abinda yake suka shirya around 12:00pm suka bar gidan.
Sun samu tarba mai kyau gidan da suka je, sai 4pm suka dawo.
Madinah tayi hakan ne domin ta rage masa damuwar da take damun sa, Mahi yayi mata duk bayanin da yake ciki to amma ba zata shiga al'amarin gidan sa ba, zata dai taya shi da addu'ar da ta saba yi masa kullum, kuma shi ma bai damu da ya sanar mata ba saboda duk lokacin da ya mata lodging wani complain tsakanin shi da Hanifah sai dai ta ba shi haƙuri tace yayi haƙuri Hanifah yarinya ce watarana zata daina.
A haka tayi ta ɗau ke masa hankali suna yawon kai ziyara na tsawon kwanaki daga baya kuma ya warware ya koma Office, amma Kullum kwanan duniya da matarsa yake kwana a rai da ita yake tashi.
***********
BAHIYYA
A 'ƴan watannin nan na samu kuɗi ba laifi domin Malama Rabi ta sama min customers da nike wa aikin lalle da kitso sun fi a ƙirga kuma kowa da kalar irin biyan da yake min na karamci. Hakan yasa muka haɗa kuɗi kusan dubu saba' in Mama ta baiwa Malama akan mu tafi tare a samu makaranta private dai dai da matsayin mu a sanya Nuhaira kafin zuwa wata shekara ni kuma a biya min kuɗin WAEC.
A ta dalilin rashin samun Baba Maharazu a waya shine sanadiyyar da Malama ta shiga gaba gaba aka yiwa Nuhaira komai har uniform har komai ya kama kuɗi dubu saba'in da huɗu termly kuma Dubu ashirin da biyu. Ss1 to Ss3.
Malama ta kasance maƙociyar mu ce tunda muka dawo nan garin Kaduna Road suka haɗu da Mama, da ita da mijinta duk malaman makaranta ne suna da yara huɗu, bariki ba kamar gida ba ne namiji zai bar matarsa ita ma ta fita ta nema domin su taru su rufawa juna asiri matuƙar zata iya, hakan yasa Malama bayan aikin koyarwa ta shiga hulɗa da mutane daban daban tana kai kayan mata cikin gari da kuma sauran State tana kuma da shago ƙofar gidanta. Ta iya kanta sosai shiyasa duk yadda kake tana iya zama da kai tana kuma da kirki irin nata.
Sanadiyyar komawar Nuhaira school yasa aiki ya taru ya min yawa ni da Mama in kuma na fita cikin gari ita kaɗai tayi ta wahala shiyasa na nema mata almajiri mai taimaka mata.
Yauma haka nayi ta bada kayan miya idan an kawo niƙa kuma in tashi in yi domin Mama ta ɗan fita unguwa, ƙarfe uku nayi na yamma na shirya na fita islamiyya nabarwa Sharifu almajiri sauran aikin kafin Nuhaira ta dawo daga school domin sai uku da rabi suke tasowa kafin ta iso gida kuma huɗu tayi shiyasa take zuwa islamiyya yanzu a makare.
Ko da muka shigo gida ana kiran sallar magrib ganin banga mama a waje ba na shiga ɗaki na tadda ta kwance a duƙunƙune da sauri muka isa gareta ni da Nuhaira muna rige rigen tambayarta mike damun ta,ko iya ɗaga kanta ba tayi hakan yasa hankalinmu ya tashi sosai na cakumota da ƙarfi nace.
“Mama mi ne ne? Mi ya same ki?”
Sai tin zuciyar ta ta shiga nuna min da hannu alamar nan ne yake mata zafi. Cikin ruɗewar kuka nace.
“InnaLillahi! Wannan ciwon zuciyar ya matsa miki Mama. Tashi ki daure mu tafi chemist, yau da ke zan tafi domin ya duba ki.... Nuhaira ɗauko mata hijabi da mukulli mu tafi”
Da sauri Nuhaira tayi yanda nace muka rufe gidan a hankali muka lallaɓa da ita wanda ko a chemist ɗin kasa zaunawa tayi sai da na zauna ta kwanta a jiki na. Tambaya ta mutumin yayi mike damunta.