Sashe 23
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Bayan na gama salloli na na daɗe ina Addu'a daga bisani na tashi na kwanta akan gadon, ganin bacci ya kasa ɗaukata yasa na tashi na janye labulen kantamemin windown na tsaya a kai, Ina ta kallon sabuwar duniyar da tsinci kaina a ciki. Daga kallon sararin samaniya ne kaɗai zaka gane cewa duhun dare ne, amma daga ka mayar da kallon ka ƙasa zaka ga hasken Fitilu mabanbanta masu walwali da ɗauke hankali suna ta aikin bada haske, ga motoci suna wucewa gwanin burgewa.
*************
FAROOQ
Bayan ya kambala duk wani muradinsa na daren yau, zaunawa yayi ya janyo system ɗin sa yana duba aikin da Mahi ya tura masa tun daren jiya.
Yana cikin aiki ne ta turo ƙofar ta shigo, sanye take cikin wasu night wears masu bala'in santsi da walwali pink color, kallon ta yayi tare da sakin murmushi yace.
“You look beautiful dear”
Haye jikin sa tayi tana murmushi itama tace.
“Really?”
Lumshe idanuwansa yayi yace.
“Yeah!. So can we get down to business? I'm always ready and available for that...”
Dariya tayi tace.
"Nifa wani zubin sai inga kwata kwata baka da kunya at all”
Zaro ido yayi da mamaki kwance a fuskar sa yace.
“Oh! A haka kika ɗauki abin Hanifah? Don't forget that you are my wife,I mean my Halal, to miye abin rashin kunya a ciki bayan sunnah ce mai ƙarfi, ni dai matuƙar za'a bani to zan karɓa in yi godiya ba da wasa ba....”
Miƙewa tayi ta koma kan gadonsa ta kwanta tana faɗin.
"That's not what brought me here, Wallahi a matuƙar gajiye ni ke, kawai ina so in faɗamaka mungama arrangement da Doctor Nicho gobe zamuje hospital ɗin.....”
Wayarsa ce tayi ƙara da sauri ya ɗaga tare da sakin murmushi duk da cewa baya gabanta. Sallama ya fara mata sannan ya gaishe ta daga can ɓangaren tace.
“Faruku ya kuka isa? Da fatan kuna lafiya”
Yace.
“We are fine Madinah, ya gida ya kike”
Tace.
“Komai Alhamdulillah. Allah ya taimaka ya bada sa'ar abinda aka je nema, ka gaisar da matar taka”
Cikin daɗin addu'ar ta yace.
“Amin Madinah, thank you so much, Hanifah zata ji in sha Allah”
Suna gama wayar Hanifah ta kalle shi tace.
“Farooq what did you tell madinat??”
Cikin mamaki yace.
“What did I tell her? Kawai na gaya mata cewa we are going for a business trip for one year, and you know it cewa Madinah is an understandable and supporting woman, fatan alheri kawai tayi mana.”
"While that's good to hear...”
Daga haka ta miƙe tana zabga hamma tace.
“I'm feeling sleepy, good night love, gobe zamu tattauna ko a mota ne”
Da sauri ya kalleta kafin ta iyarda ficewa yace.
“Why! Why Hanifah? Miyasa kullum kike son ɓatamin ne, ko tausayi na bakya yi, Hanifah sex is life....”
Da sauri ta saka hannunta ta toshe kunnen ta tare da yin waje da sauri tana dariya.
Kallon ta kawai yake har ta ɓacewa ganin sa. Ya ma rasa wane kalar tunanin zaiyi akan Hanifah, she's always always busy, Bayan Kuma yasan auren su shine kan gaban komai, amma idan zai kwana ya na faɗa mata ba zata amince ba,gani take kawai wannan kawai ra'ayin sa ne.
**************
BAHIYYA
Ganin duhun dare da wayewar gari da kuma tafiyar lokaci a agogon bangon da ke manne a ɗakin kaɗai ke nuna min shigowar dare da wayewar gari. Wani abu ne ajiye a side bed drawer Kamar alarm yake bugawa daga zaran lokacin sallah yayi sai ya fara kiran sallah.
Nafi kwana goma ban sanya kowa a ido na ba, tun ranar da muka zo ban sake ganin ko ɗaya daga cikin su ba. Abinci ne kawai wannan kukun ke kawo min ko wane lokaci wanda tun bana iya ci har yanzu dole na koyawa kaina don dole gudun yunwa amma kam shan madara da cin nama bana wasa da shi.
Fatar jiki na sai ƙara sheƙi ta ke tana ƙara luwui luwui tsabar hutu da shan sanyin AC mai daɗi. Can ƙasan zuciyata kuma kewar Mama ce ta addabeni, idan abin yayi min yawa har kuka nake. Ga kaɗaici duk yabi ya ishe ni, tashoshin da ke cikin wannan TV ɗin duk ba masu daɗi bane kamar na gida Nigeria. Shiyasa ban damu da kunna TVn ba.
.......... Ina tsaye jikin window kamar kullum ina kalle kalle na ta murɗa handle door ɗin ta shigo.
Kallonta kawai nayi tare da kau da kaina nace mata ina kwana sama sama naci gaba da kallon wajen da nike ba tare da sanin taji ko bata ji ba. Kallona tayi sama da ƙasa tamkar mai nazartar wani abu sannan tace.
“Zamuyi magana ne”
Juyowa nayi na kalle ta da kyau nace.
“Ina jinki”
Taɓe baki tayi sannan ta fara magana kamar haka.
“Yanda kika ɗauke ni ba shine mai muhimmancin ba, alaƙar da ta haɗamu itace abinda nasa a gaba. Daman can munyi yarjejeniya da ke zaki tayani renon ciki na wata tara kika amince da hakan nima na amince da biyawa mahaifiyarki kuɗin surgery ɗinta. So daman a nan ƙasar za'a yi kuma mun riga mun kambala shirye shiryen ranar Monday zamu je ayi aikin, so sai ki kasance cikin shiri”
Cikin rashin sanin in da zancen ta ya dosa nace.
"Aiki? Aiki kamar ya kenan?, ban fahimce ki ba, wane kalar aiki kike nufi?”
Kallona tayi da kyau tace.
“Za'a miki dashen Sperm ɗin mijina da Egg ɗina a mahaifarki, yayi girma a jikin ki ya rayu idan wata tara ya cika ki haife mana.....”
Wata irin gigicewa ce da ruɗewa suka ziyarci ƙwaƙwalwata lokaci ɗaya na zabura tamkar mai sabon taɓin hankali nace.
“InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Kiji tsoron Allah, kada ki danganta ni da alfasha,miye wannan kike magana akai??”
Wani kallon banza ta watsamin a wulaƙance tace.
“Ina ga kin hauka ce ne, mahaukaciya kawai, ko mata sun ƙare a duniya mi Farooq zai yi da ke, miye a jikin ki da rayuwarki baki ɗaya da Farooq zai kwanta da ke, wata ƙazama irin ki, ko zina yake mi zaiyi da ke a whole village girl like you. Common ki rufamin baki dan Allah ki saurari bayani na. Ƙwan halitta ta da Ƙwan halittar sa za'a ɗauka a saka a mahaifarki yayi girma ya rayu idan wata tara ya cika sai ki haife ki ƙara gaba shi kenan aikin.”
Cikin tsananin tashin hankali da ruɗewa na shiga girgiza kai tamkar wata zararriya ina faɗin.
“A'a ba zai yi yu ba, hakan ba zai faru ba, nifa budurwa ce. Ciki! Ciki fa kike magana Hajiya, inyi ya da shi to? Bani da aure zan yi ciki, Haba ki duba maganar nan kisa ma'aunin hankali a ciki. Gaskiya ba zai yi yu ba, ba zan iya ba...”
Taɓe baki tayi tare da ɗaga kafaɗa irin i don't care ɗin nan tace.
“While, since you say so, nasan Ina mahaifiyarki take a halin yanzu, tana asibiti ciwo ya taso mata, idan kina ganin kamar tunda na riga da na biya kuɗin aikin shikenan kinci bulus fine, kai tsaye zan kira likitan in faɗa masa ayi mata allurar mutuwa, kinga shikenan na yarda nayi asarar kuɗi na dana kashe ke kuma kin rasa mahaifiyarki.............”
*Tofa readers! Wannan shi ake kira ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Cakwakiya ce cike, danƙare a cikin wannan littafin, shin ya BAHIYYA zatayi???? Miye makomar HANIFAH a wannan TAFIYAR???? , kada fa ruwa ya ƙarewa ɗan Kada bai gama wanka ba. Farooqqq dai ya tsani BAHIYYA, ko ya abin zai kasance a tsakanin su. Ku biya kuɗin ku kuci gaba da karatu cikin nishaɗi*
“OUM AMEER”
*************
FAROOQ
Bayan ya kambala duk wani muradinsa na daren yau, zaunawa yayi ya janyo system ɗin sa yana duba aikin da Mahi ya tura masa tun daren jiya.
Yana cikin aiki ne ta turo ƙofar ta shigo, sanye take cikin wasu night wears masu bala'in santsi da walwali pink color, kallon ta yayi tare da sakin murmushi yace.
“You look beautiful dear”
Haye jikin sa tayi tana murmushi itama tace.
“Really?”
Lumshe idanuwansa yayi yace.
“Yeah!. So can we get down to business? I'm always ready and available for that...”
Dariya tayi tace.
"Nifa wani zubin sai inga kwata kwata baka da kunya at all”
Zaro ido yayi da mamaki kwance a fuskar sa yace.
“Oh! A haka kika ɗauki abin Hanifah? Don't forget that you are my wife,I mean my Halal, to miye abin rashin kunya a ciki bayan sunnah ce mai ƙarfi, ni dai matuƙar za'a bani to zan karɓa in yi godiya ba da wasa ba....”
Miƙewa tayi ta koma kan gadonsa ta kwanta tana faɗin.
"That's not what brought me here, Wallahi a matuƙar gajiye ni ke, kawai ina so in faɗamaka mungama arrangement da Doctor Nicho gobe zamuje hospital ɗin.....”
Wayarsa ce tayi ƙara da sauri ya ɗaga tare da sakin murmushi duk da cewa baya gabanta. Sallama ya fara mata sannan ya gaishe ta daga can ɓangaren tace.
“Faruku ya kuka isa? Da fatan kuna lafiya”
Yace.
“We are fine Madinah, ya gida ya kike”
Tace.
“Komai Alhamdulillah. Allah ya taimaka ya bada sa'ar abinda aka je nema, ka gaisar da matar taka”
Cikin daɗin addu'ar ta yace.
“Amin Madinah, thank you so much, Hanifah zata ji in sha Allah”
Suna gama wayar Hanifah ta kalle shi tace.
“Farooq what did you tell madinat??”
Cikin mamaki yace.
“What did I tell her? Kawai na gaya mata cewa we are going for a business trip for one year, and you know it cewa Madinah is an understandable and supporting woman, fatan alheri kawai tayi mana.”
"While that's good to hear...”
Daga haka ta miƙe tana zabga hamma tace.
“I'm feeling sleepy, good night love, gobe zamu tattauna ko a mota ne”
Da sauri ya kalleta kafin ta iyarda ficewa yace.
“Why! Why Hanifah? Miyasa kullum kike son ɓatamin ne, ko tausayi na bakya yi, Hanifah sex is life....”
Da sauri ta saka hannunta ta toshe kunnen ta tare da yin waje da sauri tana dariya.
Kallon ta kawai yake har ta ɓacewa ganin sa. Ya ma rasa wane kalar tunanin zaiyi akan Hanifah, she's always always busy, Bayan Kuma yasan auren su shine kan gaban komai, amma idan zai kwana ya na faɗa mata ba zata amince ba,gani take kawai wannan kawai ra'ayin sa ne.
**************
BAHIYYA
Ganin duhun dare da wayewar gari da kuma tafiyar lokaci a agogon bangon da ke manne a ɗakin kaɗai ke nuna min shigowar dare da wayewar gari. Wani abu ne ajiye a side bed drawer Kamar alarm yake bugawa daga zaran lokacin sallah yayi sai ya fara kiran sallah.
Nafi kwana goma ban sanya kowa a ido na ba, tun ranar da muka zo ban sake ganin ko ɗaya daga cikin su ba. Abinci ne kawai wannan kukun ke kawo min ko wane lokaci wanda tun bana iya ci har yanzu dole na koyawa kaina don dole gudun yunwa amma kam shan madara da cin nama bana wasa da shi.
Fatar jiki na sai ƙara sheƙi ta ke tana ƙara luwui luwui tsabar hutu da shan sanyin AC mai daɗi. Can ƙasan zuciyata kuma kewar Mama ce ta addabeni, idan abin yayi min yawa har kuka nake. Ga kaɗaici duk yabi ya ishe ni, tashoshin da ke cikin wannan TV ɗin duk ba masu daɗi bane kamar na gida Nigeria. Shiyasa ban damu da kunna TVn ba.
.......... Ina tsaye jikin window kamar kullum ina kalle kalle na ta murɗa handle door ɗin ta shigo.
Kallonta kawai nayi tare da kau da kaina nace mata ina kwana sama sama naci gaba da kallon wajen da nike ba tare da sanin taji ko bata ji ba. Kallona tayi sama da ƙasa tamkar mai nazartar wani abu sannan tace.
“Zamuyi magana ne”
Juyowa nayi na kalle ta da kyau nace.
“Ina jinki”
Taɓe baki tayi sannan ta fara magana kamar haka.
“Yanda kika ɗauke ni ba shine mai muhimmancin ba, alaƙar da ta haɗamu itace abinda nasa a gaba. Daman can munyi yarjejeniya da ke zaki tayani renon ciki na wata tara kika amince da hakan nima na amince da biyawa mahaifiyarki kuɗin surgery ɗinta. So daman a nan ƙasar za'a yi kuma mun riga mun kambala shirye shiryen ranar Monday zamu je ayi aikin, so sai ki kasance cikin shiri”
Cikin rashin sanin in da zancen ta ya dosa nace.
"Aiki? Aiki kamar ya kenan?, ban fahimce ki ba, wane kalar aiki kike nufi?”
Kallona tayi da kyau tace.
“Za'a miki dashen Sperm ɗin mijina da Egg ɗina a mahaifarki, yayi girma a jikin ki ya rayu idan wata tara ya cika ki haife mana.....”
Wata irin gigicewa ce da ruɗewa suka ziyarci ƙwaƙwalwata lokaci ɗaya na zabura tamkar mai sabon taɓin hankali nace.
“InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Kiji tsoron Allah, kada ki danganta ni da alfasha,miye wannan kike magana akai??”
Wani kallon banza ta watsamin a wulaƙance tace.
“Ina ga kin hauka ce ne, mahaukaciya kawai, ko mata sun ƙare a duniya mi Farooq zai yi da ke, miye a jikin ki da rayuwarki baki ɗaya da Farooq zai kwanta da ke, wata ƙazama irin ki, ko zina yake mi zaiyi da ke a whole village girl like you. Common ki rufamin baki dan Allah ki saurari bayani na. Ƙwan halitta ta da Ƙwan halittar sa za'a ɗauka a saka a mahaifarki yayi girma ya rayu idan wata tara ya cika sai ki haife ki ƙara gaba shi kenan aikin.”
Cikin tsananin tashin hankali da ruɗewa na shiga girgiza kai tamkar wata zararriya ina faɗin.
“A'a ba zai yi yu ba, hakan ba zai faru ba, nifa budurwa ce. Ciki! Ciki fa kike magana Hajiya, inyi ya da shi to? Bani da aure zan yi ciki, Haba ki duba maganar nan kisa ma'aunin hankali a ciki. Gaskiya ba zai yi yu ba, ba zan iya ba...”
Taɓe baki tayi tare da ɗaga kafaɗa irin i don't care ɗin nan tace.
“While, since you say so, nasan Ina mahaifiyarki take a halin yanzu, tana asibiti ciwo ya taso mata, idan kina ganin kamar tunda na riga da na biya kuɗin aikin shikenan kinci bulus fine, kai tsaye zan kira likitan in faɗa masa ayi mata allurar mutuwa, kinga shikenan na yarda nayi asarar kuɗi na dana kashe ke kuma kin rasa mahaifiyarki.............”
*Tofa readers! Wannan shi ake kira ga ƙoshi ga kwanan yunwa. Cakwakiya ce cike, danƙare a cikin wannan littafin, shin ya BAHIYYA zatayi???? Miye makomar HANIFAH a wannan TAFIYAR???? , kada fa ruwa ya ƙarewa ɗan Kada bai gama wanka ba. Farooqqq dai ya tsani BAHIYYA, ko ya abin zai kasance a tsakanin su. Ku biya kuɗin ku kuci gaba da karatu cikin nishaɗi*
“OUM AMEER”