Sashe 2
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“That's the challenges of life. We must plan on how to deal with our business partners always, along the line ka shirya shirin amsar faɗuwa duk lokacin da abubuwa ba su zo maka kamar yadda kayi expecting ba. A fuska sam kamar ba zasu yi daɗin hulɗa ba amma daga baya dubi yadda muka ƙare da su”
Gyaɗa kai Mahid ya yi yace.
“Haka ne fa, bari in maka ta karin maganar malam bature yace wai 'do not judge a book by it's cover'. While Ya Madinah ta ke? Kwana biyu”
Wani irin sassanyar ajiyar zuciya ya saki yana murmushi yace.
“Madinah is doing Good Mahi, Ina missing ɗin tsohuwar nan kwana biyu wallahi, gashi aiki ya hana min zuwa ganin ta, ita kuma ƙiri-ƙiri taƙi Abuja wai ba zata zauna da ni ba”
With full confidence ya Kalli Farooq ɗin cikin idonsa yace.
“Farooq mi yasa zata zauna da kai? Zama ba zai yi tsakanin ta da Hanifah ba, dama ace kun haihu ne, ko don saboda yaran zata zauna ko kuma ta riƙa zuwa a kai a kai”
Taɓe baki yayi yace.
“Haihuwa? Ba saboda haihuwa ba dai kawai bata so zuwa ba ne...”
“Farooq! Madinah ko bata furta maka ba nasan a cikin ranta tana da burin ganin 'ƴa' ƴan ka a duniya. Aure shekara bakwai! At least ka saka hankali da lissafi a cikin wannan maganar, kai kaɗai ta raina ƙwallin ƙwal nasan abu mafi farin ciki yau ta gan ka da 'ƴa' ƴa....”
Hannu ya ɗaga mishi alamar baya son zancen yace.
“Mahi please! Mubar wannan maganar, Hanifah ta ishe ni rayuwa ita da Madinah, ni ka ɗai ne na rayu a duniya ta sai yanzu da na samu Hanifah, babu kalar farin cikin da bata bani, babu abinda muka nema muka rasa....”
Miƙewa Mahid yayi tare da dangwarar da spoon ɗin hannunsa akan plate ɗin abincin da kwata kwata basu yi masa cokali uku na kirki ba, cike da jin haushi yace.
“Farooq ka daina yi min zancen banza a nan, aure ba 'ya' ƴa miye ribar sa? Manzon Allah S. A. W ya faɗamana cewa muyi aure mu hayayyafa zai yi alfahari da hakan ranar gobe ƙiyama. Sannan ya sake faɗa mana a cikin wani hadith ɗin cewa, yayin da ɗan Adam ya mutu dukkan ayyukan sa zasu yanke, fa ce abubuwa guda uku zasu rakasa zuwa ƙabarinsa, bayan an binne sa dukkan su zasu dawo ɗaya ne kawai zai tsaya tare da shi a cikin ƙabarinsa,kasan mi ne ne shi? Aikin sa walau Hairan ko Sharran. Abubuwan da ya bari kuma a doron ƙasa waɗanɗa ba zasu yanke ba matukar ya gina su a lokacin da yake raye a ban ƙasa su ne:Sadaka mai gudana, na biyu waladun salih yaro na gari wanda zai riƙa yi masa addu'a a lokacin da baya raye, na uku ilimin da ya wanzar a ban ƙasa mutane na ci gaba da amfana da shi. Ka gayamin idan baka haihu ba ta ina zaka samu yaron da zai riƙa yi maka addu'a idan ka mutu? Tun wuri ina kiran ka da babbar murya ka aje wannan banzar aƙidar yahudancin da ka ɗaukar wa kanka tun lokaci bai ƙure maka ba ka haihu, 'ƴa' ƴa su ne farin ciki sanyin idanuwan iyayen su matuƙar sun taso akan turba madaidaiciya”
Daga haka ya kwashe kayan sa ya juya da nufin ficewa daga Office ɗin.
Cike da ɓacin rai Farooq ya ce..............
Ki biya 500 ki sha karatu sister
3132703269
First Bank
Amina Ibrahim
💝 *BAHIYYA* 💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*FOLLOW ME ON WATTPAD:*
*@UMMU-AMEER*
*PAID BOOK 500*
*3132703269*
*FIRST BANK*
*AMINA IBRAHIM*
*08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BIYU*
“......... Mahi ji yanda kake magana dani tamkar ni ba shugaban ka bane, what's your problem about my marital life kana da matsala da hakan ne?”
Juyowa Mahid ya yi yace.
“Kai mai gidana ne saboda ina aikin a ƙarƙashin companynka and again don't forget I'm also a friend to you. So if you want zaka iya cewa na ajiye maka aikin ka saboda na faɗa maka gaskiya amma ba zaka iya datse iyakar abotar mu ba Farooq”
Daga haka ya juya ya fice daga ma'aikatar baki ɗaya ya nufi gida, yana ƙara jinjina al'amarin Farooq da matar sa Hanifah. Abu wasa wasa tun yana ɗauka amarci ne kawai suke morewa idan suka gama za su nemi su haihu amma sam a iya yanda ya fahimci Hanifah sam bata kawo zancen haihuwa ko kaɗan idan aka yi mata kuma ko da wasa bakin gaskiyar ta zata kafe cewa, 'ya' ƴa problem ne saboda haka ko babu su mutum zai iya rayuwa, kuma yayi farin ciki.
Mahid Baffa abokin Farooq ne tun a UK Allah ya haɗa su wurin karatu, sosai ta su ta zo ɗaya wurin halayya da mu'amalantar juna. Shi Mahid ɗan Kano ne yayin da Aiki yanzu ya kawo shi Abuja tare da Farooq ɗin.
*************
BAHIYYA
Sai kusan ƙarfe biyar na yamma na dawo ma gidan ina mai faɗuwa zaune a gindin bishiryar da suka shimfiɗa tabarma suna zaune na ce.
“Wash Allah! Wallahi duk na gaji jikina ji ni ke tamkar an naɗa min duka, aikin lalle da kitso wallahi akwai wahala...”
Nuhaira tana dariya ta ce.
"Amma kuma akwai kama naira ba. Ko da yake mutanen basa son biyan kuɗin ƙwarai sai dai kayi musu dan Allah dan zaman tare”
Girgiza kai Mama tayi tace.
" Ku dai har yanzu yara ne, ko naira goma ake samu ai yafi maganin zaman banza kuma yau da gobe in dai ana saka haƙuri sai naira gomar ta koma naira ɗari.”
Cike da zumuɗi Na ce.
“Ai Mama na manta ma in yi miki albishir, Malam ta ce zata riƙa zuwa dani cikin gari domin in riƙa yiwa mutanen ta kitso da lalle tunda Maryam ta yi aure. Tace kullum sai damunta su ke yi da kira wai ta kawo musu mai lalle da kitso...”
Shewa Nuhaira tayi tare da tafa hannu tace.
“Shikenan Aunty Bahiyya Allah ya kawo miki hanyar samun biyan kuɗin kitso da lalle mai tsoka domin su mutanen nan sun san darajar wahalar mutum, kamar yadda Maryam ɗin ta ke faɗa. Ki ji fa yanda cikin unguwar nan a ke ta zagin ta wai ta cika girman kai yanzu kowa ba ta iya yiwa lalle da kitso a yankin nan namu saboda tana zuwa manyan gidaje cikin Abuja tana kama kuɗi. Amma ji dan Allah irin sayayyar kayan kitchen ɗin da tayi....”
Katse ta Mama tayi da faɗin.
“Nuhaira wuce ki duba mana sanwa kinji”
“To lallai kam, daga fara magana kin a re kin yafe kamar ke nike faɗawa maganar. Ni mi kike dafa mana ne yau? yunwa ma ni keji”
Daga bakin Murhun Nuhaira ta bani amsa tace.
" 'ƴar sada mana, shinkafa da wake da mai da ya ji”
“To don Allah kiyi sauri I'm hungry Wallahi. Mama ya jikin naki?”
“Jiki da sauƙi Bahiyya, ni har na manta ma,saboda Ina shan maganin shi kenan na nemi ciwon na rasa”
“To masha Allah. Haka ni ke son ji Mama, Allah ya ƙara miki lafiya, ya kuma ji ƙan Baba”
“Ameen! Bahiyya nicce dai shi zuwa kitson da Malama Rabi ta ce ba dai zuwa akeyi a kwana ba ko?”
Hijabina na cire tare da ɗan gincirawa kaɗan na ce.
“A'a, ba kwana ba ne Mama wuni ɗaya ne, amma tace ma zata shigo da kanta tayi miki bayani, duk lokacin da buƙatar hakan ta taso sai mu tafi”
“To Allah yasa mu dace. Ni yanzu burina ki samu ki koma makarantarki ki iyar da ƙarasa aji shidan nan ki amshi takardun mu gani kamar yadda Malam yayi buri. Ita ma Nuhaira a maida ta Js3 ɗin ta samu itama ta kambala ko da secondary ɗin ce kuka kambala ai zai fi...”
Jin Mama ta ambaci sunan Baba ban san lokacin da zuciyata tsinke ba sai ji nayi hawaye suna kwaranya daga kwarmin idanuwana. Gefen in da zuciyata take harbawa na dafe ina faɗin.
“Mama kinji zuciyata yadda ta wani buga da ƙarfi? Wallahi ban san lokacin da zuciyata zata manta da baba ba, kullum kwanan duniya mutuwar Baba sabuwa take dawo min, duk burin da ya ci a kanmu ya tashi a banza....”
“Bai tashi a banza ba Bahiyya, a iya yadda kuka samu kula da tarbiyya daga wurin Jafaru hakan ya nuna cewa yayi nasara, kawai Addu'a ita ce yafi buƙata Bahiyya, muyi ta yi masa addu'a da nema masa gafara a wurin ubangiji”
Hawayena na share nace.
“Hakane Mama, Allah ya yi mana jagora ya gafarta masa. Gaskiya Mama ni dai yanzu na fiso ayi ƙoƙari a mayar da Nuhaira ɗin. Kin san bokon nan ba kamar na Zamfara da muka baro ba ne. Na tambayi malama kudin register WAEC kuɗi ne masu yawa. Shi ne nake ganin yafi ita ta fara komawa ni kuma daga baya idan an samu yadda ake so sai nayi register nayi exam ɗin kawai ba tare da na sake komawa Ss3 ɗin ba.”
Mama tace
“Kina ganin hakan zai fi?”
“Eh Mama. Haka za'a yi”
“Allah ya hore muna abin hidimar, ya bamu rai da lafiya”
“Amin Mama, bari in watsa ruwa kafin nan abincin ya ida kambala”
**************
FAROOQ
Tunda Mahid ya fita ya bar shi bai samu wani ƙwarin guiwar barin office ɗin ba har yamma. Duk iya ƙure tunani ya gama yi ko da zai samu wata mafita amma babu wani haske, Hanifar sa kawai ya ke tunanin, farin cikin ta shi ne nasa. Ta daɗe da nuna mai bata da wata buƙata da yara sannan shima kuma haka. But ya rasa gane mi Mahi yake nufi da shi akan dole sai ya kutsa kai a cikin rayuwar gidan sa.
Gyaɗa kai Mahid ya yi yace.
“Haka ne fa, bari in maka ta karin maganar malam bature yace wai 'do not judge a book by it's cover'. While Ya Madinah ta ke? Kwana biyu”
Wani irin sassanyar ajiyar zuciya ya saki yana murmushi yace.
“Madinah is doing Good Mahi, Ina missing ɗin tsohuwar nan kwana biyu wallahi, gashi aiki ya hana min zuwa ganin ta, ita kuma ƙiri-ƙiri taƙi Abuja wai ba zata zauna da ni ba”
With full confidence ya Kalli Farooq ɗin cikin idonsa yace.
“Farooq mi yasa zata zauna da kai? Zama ba zai yi tsakanin ta da Hanifah ba, dama ace kun haihu ne, ko don saboda yaran zata zauna ko kuma ta riƙa zuwa a kai a kai”
Taɓe baki yayi yace.
“Haihuwa? Ba saboda haihuwa ba dai kawai bata so zuwa ba ne...”
“Farooq! Madinah ko bata furta maka ba nasan a cikin ranta tana da burin ganin 'ƴa' ƴan ka a duniya. Aure shekara bakwai! At least ka saka hankali da lissafi a cikin wannan maganar, kai kaɗai ta raina ƙwallin ƙwal nasan abu mafi farin ciki yau ta gan ka da 'ƴa' ƴa....”
Hannu ya ɗaga mishi alamar baya son zancen yace.
“Mahi please! Mubar wannan maganar, Hanifah ta ishe ni rayuwa ita da Madinah, ni ka ɗai ne na rayu a duniya ta sai yanzu da na samu Hanifah, babu kalar farin cikin da bata bani, babu abinda muka nema muka rasa....”
Miƙewa Mahid yayi tare da dangwarar da spoon ɗin hannunsa akan plate ɗin abincin da kwata kwata basu yi masa cokali uku na kirki ba, cike da jin haushi yace.
“Farooq ka daina yi min zancen banza a nan, aure ba 'ya' ƴa miye ribar sa? Manzon Allah S. A. W ya faɗamana cewa muyi aure mu hayayyafa zai yi alfahari da hakan ranar gobe ƙiyama. Sannan ya sake faɗa mana a cikin wani hadith ɗin cewa, yayin da ɗan Adam ya mutu dukkan ayyukan sa zasu yanke, fa ce abubuwa guda uku zasu rakasa zuwa ƙabarinsa, bayan an binne sa dukkan su zasu dawo ɗaya ne kawai zai tsaya tare da shi a cikin ƙabarinsa,kasan mi ne ne shi? Aikin sa walau Hairan ko Sharran. Abubuwan da ya bari kuma a doron ƙasa waɗanɗa ba zasu yanke ba matukar ya gina su a lokacin da yake raye a ban ƙasa su ne:Sadaka mai gudana, na biyu waladun salih yaro na gari wanda zai riƙa yi masa addu'a a lokacin da baya raye, na uku ilimin da ya wanzar a ban ƙasa mutane na ci gaba da amfana da shi. Ka gayamin idan baka haihu ba ta ina zaka samu yaron da zai riƙa yi maka addu'a idan ka mutu? Tun wuri ina kiran ka da babbar murya ka aje wannan banzar aƙidar yahudancin da ka ɗaukar wa kanka tun lokaci bai ƙure maka ba ka haihu, 'ƴa' ƴa su ne farin ciki sanyin idanuwan iyayen su matuƙar sun taso akan turba madaidaiciya”
Daga haka ya kwashe kayan sa ya juya da nufin ficewa daga Office ɗin.
Cike da ɓacin rai Farooq ya ce..............
Ki biya 500 ki sha karatu sister
3132703269
First Bank
Amina Ibrahim
💝 *BAHIYYA* 💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*FOLLOW ME ON WATTPAD:*
*@UMMU-AMEER*
*PAID BOOK 500*
*3132703269*
*FIRST BANK*
*AMINA IBRAHIM*
*08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BIYU*
“......... Mahi ji yanda kake magana dani tamkar ni ba shugaban ka bane, what's your problem about my marital life kana da matsala da hakan ne?”
Juyowa Mahid ya yi yace.
“Kai mai gidana ne saboda ina aikin a ƙarƙashin companynka and again don't forget I'm also a friend to you. So if you want zaka iya cewa na ajiye maka aikin ka saboda na faɗa maka gaskiya amma ba zaka iya datse iyakar abotar mu ba Farooq”
Daga haka ya juya ya fice daga ma'aikatar baki ɗaya ya nufi gida, yana ƙara jinjina al'amarin Farooq da matar sa Hanifah. Abu wasa wasa tun yana ɗauka amarci ne kawai suke morewa idan suka gama za su nemi su haihu amma sam a iya yanda ya fahimci Hanifah sam bata kawo zancen haihuwa ko kaɗan idan aka yi mata kuma ko da wasa bakin gaskiyar ta zata kafe cewa, 'ya' ƴa problem ne saboda haka ko babu su mutum zai iya rayuwa, kuma yayi farin ciki.
Mahid Baffa abokin Farooq ne tun a UK Allah ya haɗa su wurin karatu, sosai ta su ta zo ɗaya wurin halayya da mu'amalantar juna. Shi Mahid ɗan Kano ne yayin da Aiki yanzu ya kawo shi Abuja tare da Farooq ɗin.
*************
BAHIYYA
Sai kusan ƙarfe biyar na yamma na dawo ma gidan ina mai faɗuwa zaune a gindin bishiryar da suka shimfiɗa tabarma suna zaune na ce.
“Wash Allah! Wallahi duk na gaji jikina ji ni ke tamkar an naɗa min duka, aikin lalle da kitso wallahi akwai wahala...”
Nuhaira tana dariya ta ce.
"Amma kuma akwai kama naira ba. Ko da yake mutanen basa son biyan kuɗin ƙwarai sai dai kayi musu dan Allah dan zaman tare”
Girgiza kai Mama tayi tace.
" Ku dai har yanzu yara ne, ko naira goma ake samu ai yafi maganin zaman banza kuma yau da gobe in dai ana saka haƙuri sai naira gomar ta koma naira ɗari.”
Cike da zumuɗi Na ce.
“Ai Mama na manta ma in yi miki albishir, Malam ta ce zata riƙa zuwa dani cikin gari domin in riƙa yiwa mutanen ta kitso da lalle tunda Maryam ta yi aure. Tace kullum sai damunta su ke yi da kira wai ta kawo musu mai lalle da kitso...”
Shewa Nuhaira tayi tare da tafa hannu tace.
“Shikenan Aunty Bahiyya Allah ya kawo miki hanyar samun biyan kuɗin kitso da lalle mai tsoka domin su mutanen nan sun san darajar wahalar mutum, kamar yadda Maryam ɗin ta ke faɗa. Ki ji fa yanda cikin unguwar nan a ke ta zagin ta wai ta cika girman kai yanzu kowa ba ta iya yiwa lalle da kitso a yankin nan namu saboda tana zuwa manyan gidaje cikin Abuja tana kama kuɗi. Amma ji dan Allah irin sayayyar kayan kitchen ɗin da tayi....”
Katse ta Mama tayi da faɗin.
“Nuhaira wuce ki duba mana sanwa kinji”
“To lallai kam, daga fara magana kin a re kin yafe kamar ke nike faɗawa maganar. Ni mi kike dafa mana ne yau? yunwa ma ni keji”
Daga bakin Murhun Nuhaira ta bani amsa tace.
" 'ƴar sada mana, shinkafa da wake da mai da ya ji”
“To don Allah kiyi sauri I'm hungry Wallahi. Mama ya jikin naki?”
“Jiki da sauƙi Bahiyya, ni har na manta ma,saboda Ina shan maganin shi kenan na nemi ciwon na rasa”
“To masha Allah. Haka ni ke son ji Mama, Allah ya ƙara miki lafiya, ya kuma ji ƙan Baba”
“Ameen! Bahiyya nicce dai shi zuwa kitson da Malama Rabi ta ce ba dai zuwa akeyi a kwana ba ko?”
Hijabina na cire tare da ɗan gincirawa kaɗan na ce.
“A'a, ba kwana ba ne Mama wuni ɗaya ne, amma tace ma zata shigo da kanta tayi miki bayani, duk lokacin da buƙatar hakan ta taso sai mu tafi”
“To Allah yasa mu dace. Ni yanzu burina ki samu ki koma makarantarki ki iyar da ƙarasa aji shidan nan ki amshi takardun mu gani kamar yadda Malam yayi buri. Ita ma Nuhaira a maida ta Js3 ɗin ta samu itama ta kambala ko da secondary ɗin ce kuka kambala ai zai fi...”
Jin Mama ta ambaci sunan Baba ban san lokacin da zuciyata tsinke ba sai ji nayi hawaye suna kwaranya daga kwarmin idanuwana. Gefen in da zuciyata take harbawa na dafe ina faɗin.
“Mama kinji zuciyata yadda ta wani buga da ƙarfi? Wallahi ban san lokacin da zuciyata zata manta da baba ba, kullum kwanan duniya mutuwar Baba sabuwa take dawo min, duk burin da ya ci a kanmu ya tashi a banza....”
“Bai tashi a banza ba Bahiyya, a iya yadda kuka samu kula da tarbiyya daga wurin Jafaru hakan ya nuna cewa yayi nasara, kawai Addu'a ita ce yafi buƙata Bahiyya, muyi ta yi masa addu'a da nema masa gafara a wurin ubangiji”
Hawayena na share nace.
“Hakane Mama, Allah ya yi mana jagora ya gafarta masa. Gaskiya Mama ni dai yanzu na fiso ayi ƙoƙari a mayar da Nuhaira ɗin. Kin san bokon nan ba kamar na Zamfara da muka baro ba ne. Na tambayi malama kudin register WAEC kuɗi ne masu yawa. Shi ne nake ganin yafi ita ta fara komawa ni kuma daga baya idan an samu yadda ake so sai nayi register nayi exam ɗin kawai ba tare da na sake komawa Ss3 ɗin ba.”
Mama tace
“Kina ganin hakan zai fi?”
“Eh Mama. Haka za'a yi”
“Allah ya hore muna abin hidimar, ya bamu rai da lafiya”
“Amin Mama, bari in watsa ruwa kafin nan abincin ya ida kambala”
**************
FAROOQ
Tunda Mahid ya fita ya bar shi bai samu wani ƙwarin guiwar barin office ɗin ba har yamma. Duk iya ƙure tunani ya gama yi ko da zai samu wata mafita amma babu wani haske, Hanifar sa kawai ya ke tunanin, farin cikin ta shi ne nasa. Ta daɗe da nuna mai bata da wata buƙata da yara sannan shima kuma haka. But ya rasa gane mi Mahi yake nufi da shi akan dole sai ya kutsa kai a cikin rayuwar gidan sa.