← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 23

Sashe 21

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Murmushi tayi tace.
“Wannan duk mai sauƙi ne, We are going to surprised them, daman can 2years back Momma ta taɓa tambaya na cewa har yanzu bata samu jika ba, nace mata sai time yayi, to since then bata sake tambayana ba kuma, so we will plan to hide it for them, it will serve as a secret, after she put to bed Sai mu kira su mu faɗa musu cewa na haihu, ita kuma sai ta tafiyar ta, har Grand Ma Itama.”

Gyaɗa kan shi yayi tare da ɗaga ta daga kan thigh ɗinsa ya miƙe tsaye yace.

"It's ok. I have meeting tomorrow morning, so zan je zan tattauna da Mahi...”

Wani faɗuwar gaba taji wanda bata san dalili ba saboda kawai taji ya kira sunan Mahi.

Da sauri tace.

" Wait.. Wait..!”

Tsayawa yayi yace.

"What?”

Kai tsaye tace.

“Please let it be secret, don't tell him anything pls”

Ɗan jim yayi kaɗan sai kuma ya Gyaɗa kai yace.

“Ok”

Tana ganin ficewar sa ta koma daɓas kan kujera ta zauna tare da sauke wani nannauyan ajiyan zuciya tana girgiza kai a ranta tana faɗin. I hate you Mahi! I so much hate you with passion, you are the cause of all my stress, we have plan and build our life simple and understandable with so much love and care, duk abinda na faɗawa mijina yarda yake bai taɓa fushi dani ba, but daga lokacin da ya fara zama da kai sai ka shiga canja sa a hankali ya fara dawowa mijin bahaushiya, ya fara yi min magana cikin ihu da nuna shine a gaba ni bani wani right, I promise you Mahi Sai na ɗaukeshi baki ɗaya daga ƙasar nan ka daina ganinsa.

Sai kuma ta ja guntun tsaki tana ƙara tuna yadda yanzu Farooq ya canja baki ɗaya, komai na sa ya dawo na ganin laifi, gashi yanzu two-four bai da wani zance sai na haihuwa. Taya zata iya yafewa Mahi Madinat, a yanzu ta gama yarda a duniya bata da wasu maƙiyanda suka wuce mutum biyu ɗin nan.

*************

BAHIYYA

Zaune nake na baje ina kwasar wainar ƙwai da shayi mai bala'in kauri ga dankalin turawa daban ga farfesun kayan ciki sai tashin ƙamshi yake,a gaskiya ina jin daɗin rayuwar da nike ciki a yanzu, amma da zaran na tuna da kalar masu gidan sai in ji komai ya fita kaina kuma.

Sallama Aunty Nafisat tayi ta shigo ciki tare da sakar min murmushi tace.

“Sannu Bahiyya, idan kika gama ki shirya zaku fita da Hajiya...”

Cikin damuwa nace.

"Ina zamu je kuma”

Aunty Nafisat tace

“I don't know”

Nace

" To tare da ke zamu tafi”

Girgiza kanta tayi tace.

“A'a, ki yi ki shirya she's waiting for you, don't waste her time”

Cikin zaƙuwa nace.

“Aunty Nafisat dan Allah ko zaki koyamin turanci nima in riƙa ji ina mayarwa kamar ku?”

Dariya tayi tace.

" Kai Bahiyya, kina nufin baki iya turanci ba? A ina kika makaranta?”

Taɓe baki nayi nace.

“A garin mu na da Zamfara, government ce nayi kuma kin san karatun can sai a hankali ba kamar na nan ba ne, sannan gashi na shiga Ss3 ba daɗewa muka dawo nan,nan ɗin kuma ban ci gaba ba”

“OK! Idan mun samu time zan riƙa koyar da ke ta baki da kuma rubutu”

Cikin jindadi maganar ta nayi mata godiya sannan ta juya ta tafi. Ina jin daɗin Aunty Nafisat a gidan nan, ban san matsayin ta ba amma tana da kirki sosai.

Miƙewa nayi domin abincin gaba ɗaya ji nayi ya fitar min a kai, amma kuma sai da naci naman tukun sannan na tashi, domin ni a gaskiya ina son nama ba wasa.

Wanka nayi shaf-shaf na fito na mulke jikina da mayuka na sababbi sannan naje gun kayana na buɗe na saka sabbin undies cikin waɗanda aka kawo min na zaɓo wata Abaya onion color na saka sannan na zuba black hijab ɗina a kai na sanya black shoe na fito.

Da Aunty Nafisat naci karo ta yi min murmushi ta juya na bita har bakin mota,ta buɗe na shiga sannan ta koma, wanda a raina na rasa gane wannan kulawar ko ta miye domin abin har mamaki yake bani. Ko a motar nafi minti talatin da ni da direba muna zaune sannan ta ga dama ta fito.

Tana shigowa na kalle ta kaɗan cikin tsoro tsoro nace.

"Ina kwana”

Ba tare da ta ko kalli in da nake ba tace.

" Lafiya”

Daga haka ta fitar da wayar ta ta fara latsawa cikin harshen turanci na ji tayi wa direban magana shi kuma na ji yace OK Ma.
Tsaki naja cikin raina nace shegu kawai idan na koyi turancin ai sai inga tsiyar ƙarya duk in da ta kwana.

Duk da ba'a faɗamin ba na gane cewa asibiti ce. Asibiti? Mi kuma zamuyi a asibiti? Tambayar da na yiwa kaina kenan wanda nasan cewa bani da amsar ta sai dai in zuba na mujiyata in yi kallo.

Bayan munyi tafiya naga mun shiga wani babban wuri mai girma gashi ya sha kyau kamar ba asibiti ba. Wani office muka shiga wanda naga wani likita zaune ya tsuke cikin suit baƙa mai blue ɗin necktie.
Da sauri ya miƙe suka fara gaisuwa su biyu bayan sun gama ya zauna tare da kallona yana murmushi yacemin.

“Welcome, please have a seat”

Murmushi nayi masa kamar yadda ya yi min na zauna akan kujerar da naga ya na nunamin.

Ba wata doguwar magana sukayi ba sai naga ya miƙe yace in biyo sa, ba musu na tashi na bi shi, zuciya ta sai bugawa take akan tsoro.

Jinina aka fara ɗiba, sannan aka kaini wani ɗaki ana ta min wasu abubuwa na gwaji kamar mai wata rashin lafiya, tambayoyi ne suke cizon raina bani da kuma wanda zan tambaya, domin duk basa jin Hausa. Mun jima sosai a asibitin sannan daga bisani na fito ni ka ɗai likitan ya rakoni har bakin mota, sai da na shiga na zauna sannan yace min.

“Sai Anjima Beautiful”

Ji nayi kamar na kafa masa mari ɗan iskan, wai daman yana jin Hausa amma yayi kamar baya ji, tsaki naja tare da juya fuskata nayi masa banza.

Daga haka ya rufe motar direban yaja muka tafi.
Bayan mun koma gida abun still yana raina, Ina ganin Aunty Nafisat nace.

"Aunty Nafisat mi yasa ta kaini asibiti hala?”

Cikin mamaki tace.

" Miya faru ?”

Nan na gaya mata duk abinda aka min na gwaje-gwaje da kuma Jinina da aka ɗiba.

Tace min ba komai nasan harakar masu kudin nan sunfi son komai suyi shi akan ƙa'ida.
Daga haka na wuce ciki na yi wanka nayi sallah sannan na ci abinci na zauna aikin kallo, domin shi kaɗai ne aikina a yanzu, daga ci sai kwanciya sai kallo sai Sallah.

Washe gari ma haka akayi, Ina zaune tace in shirya zamu fita, biye nike ni dai aka kaini wurin yin passport na shirye shiryen tafiyarmu, tafiyar da ban san dalilin ta ba, ko da yake renon cikin zan tayata dole su yi min gwaji kada ace ina ɗauke da wata cutar da zan iya shafa mata ita da ɗanta.

Bayan mun gama wani babban shopping mall muka tafi, a can na tarar da Aunty Nafisat mamaki duk ya gama kamani. Dariya tayi tacemin muje in zaɓi duk abinda nike so a nan. Ƙarshe dai ita ce ta shiga zaɓar min domin ni ban san komai ba, ganin ban taɓa saka wancan kayan ba yasa ta ƙara jibgamin Abayas masu uban yawa, da kayan shafe shafe muka koma gida.

A yanzu kam na saba sosai da Aunty Nafisat domin ina zagewa muyi ta fira, yawancin firar kuma duk akan turancin ne akan na dage dole sai ta koyamin ni kuma ko da bala'i na ƙuduri sai na iya.

Muna cikin firar mu naji an kira ta a waya ta ɗauka cikin ladabi tana magana daga Ƙarshe ta yanke bayan sun gama.

Kallona tayi tace.

“Bahiyya muje na ta yaki ki shirya kayan ki gobe zaku tafi”

Murya a sanyaye nace.

"Gobe kuma? To da ke zamu tafi ko Aunty Nafisat?”

Girgiza kanta tayi tace.

“A'a.”

Daga haka ta wuce na bi bayanta zuwa ɗaki na.

Trolley biyu tayimin babba da ƙarama sai wata jakar handbag da muka siyo ranar wadda sai dai na riƙe don passion domin ban san mi zan saka a ciki ba.

Muna nan tare da ita har lokacin tafiyar ta gida yayi na rakota har bakin motar ta har da guntun hawaye na duk da nasan cewa gobe da ƙila kafin mu tafi da wuri zata zo amma ina jin kewar ta sosai a ciki raina.

Da dare bayan na kwanta, bacci kasa ɗaukata yayi, tunanin Mama ne kawai a raina da kuma Nuhaira, sai yanzu naji takaici domin ba riƙe numbern Mama ba da kuma ta Malama sannan banyi azancin rubutawa na riƙe ba, sai yanzu na gane cewa nayi shirme babba, taya zan yi shekara ba tare da jin muryar Mama ba? Ga matar nan er renin hankali, ban gama damar ta balle na tambaye ta. Yanzu dai idan muka tafi sai inga wa kuma zata samu wanda zai riƙa yi mata magana da ni tunda bata so tana magana dani, wanda ban san dalilin hakan ba.

Washe gari ma da na farka, sukuku na tashi tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki.
Ina cikin shiryawa sai ga Aunty Nafisat ta shigo da murna naje na rungume ta.
Nan muka yi ta fira ta sai kuma ta tashi taje kitchen na bi bayan ta, ta gama shirya komai taje na jira ta, taje ta shirya musu table sannan ta dawo ni a nan ma nayi breakfast ɗin nawa. Sannan naje na shirya aka fitar da kayana zuwa mota.

Ƙiri Ƙiri suka hanani saka hijab Wai Sai dai in yi rolling da gyalen Abayar dole na tunda bani da wata mafita nayi.
Chapter 21 · 0% Book details