Sashe 11
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Eh bazan haɗa ba domin nasan cewa Allah ya bani girman da yafi naki, ke bari in faɗa miki wani ɗan ƙaramin sirrin samun yara da baki sani ba; a duk lokacin da kuka samu wani saɓani da namiji ya ƙona miki rai, da zaran kin zo ga yaran ki kin kalle su kunyi fira sai kiji duk wata damuwar ki ta wanke to idan baki da su fa? Sai dai damuwar nan ya kashe ki a banza kuma wata matar zai sake aura. Hanifah ki zama mai tunani da hangen nesa kar ki zama mai son kai, ki duba duk irin ƙaunar da mijinki ya nuna miki amma ke ace Common ƙaramin abu ba zaki iya yimai ba ya neme ki alfarma, Haba ki yi tunani in dai ke mai hankali ce...”
Hura hanci Hanifah tayi tare da runtse ido ta buɗe ta kalli Rasi'at tace.
“Is that all you have for me? A matsayin ki na aminiyata na kawo miki damuwata ina neman mafita abinda zaki faɗa min kenan?”
Matsowa Rasi'at tayi tare da janyo hannun Hanifah ta riƙe ta saukar da murya ƙasa tace.
“Hanifah, in dai ni kin yarda cewa best friend ɗin ki ce, to ina roƙon ki da ki amsa buƙatar mijin ki, ki haihu tare da shi matuƙar kina son sa, dan Allah Hanifah, wallahi babu abinda zai rage ki da shi face ma ƙara kusanta ki da mijinki ƙaunar da yake miki ta ƙara ninkuwa ninkin ba ninkin. Maza da dama basu yarda cewa matayensu na son su sai idan sun haihu da su to a lokacin zasu yarda cewa mace ta na son su and she is ready to die together with him. Let me give you an example with my self Hanifah ;ko da mukayi aure da Abdul-fatah bai yarda cewa ina son shi na shirya zama da shi ba sai da na haifi Amed, a lokacin na fara ma sanin miye soyayyar namiji kuma har yau muna respecting juna, I'm a business woman like you, but nothing can deprived me daga kula da mijina. Hanifah ki riƙa kulawa da mijinki, Farooq ba ƙaramin yaro bane kuma ba ƙaramin mutum bane, karki yarda ki bar wata ƙofar da zai fara yarda da cewa bai samu matar da ta dace da shi ba. Ki duba irin kyau da zubin da Allah yayi miki ki kuma duba siffar mijin ki shima, zaku samu 'ya' ƴa masu kyau da nagarta. Hanifah from the bottom of my heart that's the only advice I have for you Ko Nasibat ce sister na iya abinda zan faɗa mata kenan, idan kin ɗauka yayi miki amfani idan baki ɗauka ba watarana zaki ce na faɗa miki haka”
Ajiyar zuciya Hanifah ta sauke tare da gyaɗa kai tace.
“Thank you Rasi. I will think about it”
Miƙewa Rasi'at tayi tace.
“Thank you for understanding. Let me bring you something, kinzo na cika ki da surutu ba tare da na kawo miki abun taɓawa ba”
Dawowa tayi hannun ta ɗauke da tray with handmade juice da Kuma tsire tana dariya tace.
“Kin zo a daidai friend saboda na yi tsiren tukunyar da kike so”
“Wow! Thank you”
Bayan ta ajiye mata tace.
"Let me check on Bahiyya, Kar taga kamar na ƙyale ta....”
Ajiye Juice ɗin hannunta Hanifah tayi tace.
“Wait Rasi! Ina Wai kika samo wannan ita kuma? I wanted to ask you na manta ne, duk shagun nan da ke akwai na masu saloon komai kuma ana yi na masu kuɗi shine zaki ƙare da wannan tana taɓa miki jikin ki har kuna dariya da ita”
Zaunawa Rasi'at tayi tana murmushi tace.
“Eyyah! She's Bahiyya by name, wallahi Malama Rabi ce ta kawo min ita, yarinyar tana da kirki bata cika hayaniya ba, kuma ta iya sosai, Abdulfatah bai cika son zuwa saloon ba shi yasa na raba kaina. Hanifah yarinyar abin a tausaya ce, Mahaifin ta ya rasu daga ita sai Mahaifiyarta da ƙanwar ta ne a nan Nigeria duk sauran dangin su suna Nijar, kuma ba zasu iya Komawa ba...”
Cikin mamaki Hanifah tace.
“And who told you all this, is she the one? Kin san buzayen nan sun iya ƙarya, so karki wani saki jiki da ita wallahi zata iya aure miki miji, daga wannan kirkin nata zaki ji zance ya canza”
Dariya sosai Rasi'at tayi sannan tace.
“No! Ba ita ce ta faɗa min ba malama ce kuma ko shi ni na tambayeta bayan Bahiyyar bata nan nace miyasa bata yin school. Allah na tuba mi Abdulfatah zai yi da Bahiyya”
Daga haka Hanifah ta miƙe ta ɗauki jakar ta tace.
“Ni dai kar ki ce ban gaya miki ba watarana, kice mi Abdulfatah zai yi da ita, ko ni da na san na fiki kyau Rasi wannan yarinyar ta Cuna min balle ke. Ni Kinga tafiyata”
Dariya sosai Rasi tayi sannan tace.
"To ba matsala ni yoruba ita Buzaye sai mu shiga asirtar juna in ga ni da ita waye zai yi nasara”
Hanifah tace.
" Maganin dai kar ayi kar a fara, ki kore ta kawai”
Ko a parlorn sai da Hanifah ta sake ca ke ta da kallon ƙurullah, ganin yadda suke ta karatu ita da Khadijat da Ahmed suna dariya yasa ta taɓe baki ta wuce abin ta.
Rasi kuwa tsiren ta kawo wa Bahiyya tace.
“Bahiyya na gaya miki daman tafiya zan yi kuma sai gashi nayi baƙuwa, lokaci kuma yanzu ya ƙure ba zaki iya yi min ba. Sai dai idan na dawo kamar zan iya kai 1week saboda auren ƙanwata ne zanje idan nadawo zan aika Malama ta kiramin ke”
Cikin girmamawa Bahiyya tace.
“Allah ya kai lafiya, ya sanya alheri ya bada zaman lafiya”
Ƙarfe biyu na rana ta saka driver ya kai Bahiyya gida bayan ta cika ta da sha tara na arziki.
***************
BAHIYYA
Duk irin ɗaukin da na shigo da shi gida akan irin abin arzikin da maman Khadijat tayi mini lokaci guda ya suranye samakon wani irin mummunan yanayin da na riski Mama a ciki. A bakin bishiyar tsakar gidan mu na iske ta kwance shame shame a jikin Nuhaira Ko motsi bata yi. Wani irin jifa nayi da duk wani abinda yake hannuna nayo kanta tare da zunduma ihu nace.
“InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Nuhaira miye ya samu Mama? Miye ya same ta dan Allah??”
Itama cikin Kuka tace.
“Nima Aunty Bahiyya ban sani ba, Ina makaranta Sharifu yazo ya kirani wai Mama tana cikin yin Niƙa a injin shi kuma yana wanke wanke kawai suka ga ta yanke jiki ta faɗi, ko da nazo har Maman Walida ta shigo tana tare da ita, ni kuma na ruga wurin mai chemist na ce ya zo dan Allah ga halin da Mama take ciki shine bayan ya zo yace kawai muyi gaggawar kai ta asibiti, to naje Malama da mijinta duk basa nan, shi ne na zauna jiranki....”
Cikin masifa na ce.
“Amma sai yau Nuhaira na yarda cewa baki da hankali, shine zaki zauna ki barta ta mutu? bayan kinji abinda likitan yace cewa ayi gaggawar kai ta asibiti, uban mi kika tsaya jira baki san in da kuɗi yake ba, wawiyar banza”
Da gudu na faɗa ɗaki na ɗauko kuɗin da ban san ma adadin nawa ba ne na fito.
Da gudu na fita waje na hau mashin naje na ɗauko mota nadawo.
In banda kuka itama Nuhairar ba abinda take sai famar bani haƙuri take tana cewa ta ruɗe ne shi yasa.
Wata private hospital muka kaita in da aka taɓa admitting ɗin ɗiyar Malama wato Umaimah. Da sauri suka karɓe mu aka shiga da ita emergency. Tare da tsare mu da tambayoyin mi ye yake damunta.
Kusan kwanan mu biyu muna reto tare da Malama har da mijinta ƙarshe suka tura mu federal medical center bayan sun caje mu kuɗi sunfi dubu hamsin.
Ni dai biye kawai nike daga Malama sai mijinta Uncle Idris suka ɗai ke kai da kawo.
Ƙarin ruwa ne ake ta yi mata da allurai, tun muna waccan asibitin ta farfaɗo amma dai tana nan zurum kawai tana bin mu da ido malama kuma ta kasa yi min bayanin komai.
Ranar da muka cika kwana huɗu a ranar akace muna result ya fito na gwaje gwajen da duk aka yi mata wanda ko a nan an caje mu kusan dubu saba'in, har kuɗin da muke da yayi ƙasa nan ta ke.
Malama ta jima a ɗakin ganin likitan sannan daga bisa ni ta zo ta kirani muka shiga tare. Shekara ta sha takwas yanzu, duk da irin ƙananun shekaru na, Ina iya fahimtar abu akan fuskonki mutane na daɗi ko aka sin haka. Kafin ma likitan ya fara mini magana naji gaba ɗaya zuciya ta ta gama tsinkewa domin ji nike a jiki na wani mummunan abu ya faru da Mama.
“Bahiyya ko?”
Likitan ne ya faɗi hakan lokacin da ya dallomin Fitilun ganin sa babu ko ƙyaftawa.
Gyaɗa kaina kawai na iya yi ina wani muzurai tamkar an tsoma kaza a ruwan zafi.
“Da ace akwai wani na gaba da ke da dashi zamu tattauna wannan zancen, but unfortunately you are the only person na kusanta da zan iya yiwa bayani, Allah yasa zaki fahimce ni”
Lumshe jiƙaƙkun idanuwa na nayi waɗan da suka shabke da ruwan hawaye na sake buɗe su akan shi nace.
“Ina jinka likita. Miye matsalar, na roƙe ku da girman Allah ku faɗa min gaskiya kada ku ɓoyemin komai, nayi muku alƙawari zamowa jajirtacciya”
“To Alhamdulillah! Bahiyya haƙiƙa kowa ne irin mutum a duniya yana da irin tashi ƙaddarar ke musulma ce saboda haka nasan addinin ku ya koyar da ku yarda da ƙaddara...”
Ta wutsiyar ido na sake ƙare mishi kallo a karo na biyu, a raina nace yanzu kai duk haibar nan taka da iya bada magana kahiri ne kenan? To kuma ji yadda yaji Hausa kamar jakin Kano.....
“Bahiyya are you listening?”
Da sauri na gyaɗa kai na alamar eh sannan yaci gaba da cewa.
Hura hanci Hanifah tayi tare da runtse ido ta buɗe ta kalli Rasi'at tace.
“Is that all you have for me? A matsayin ki na aminiyata na kawo miki damuwata ina neman mafita abinda zaki faɗa min kenan?”
Matsowa Rasi'at tayi tare da janyo hannun Hanifah ta riƙe ta saukar da murya ƙasa tace.
“Hanifah, in dai ni kin yarda cewa best friend ɗin ki ce, to ina roƙon ki da ki amsa buƙatar mijin ki, ki haihu tare da shi matuƙar kina son sa, dan Allah Hanifah, wallahi babu abinda zai rage ki da shi face ma ƙara kusanta ki da mijinki ƙaunar da yake miki ta ƙara ninkuwa ninkin ba ninkin. Maza da dama basu yarda cewa matayensu na son su sai idan sun haihu da su to a lokacin zasu yarda cewa mace ta na son su and she is ready to die together with him. Let me give you an example with my self Hanifah ;ko da mukayi aure da Abdul-fatah bai yarda cewa ina son shi na shirya zama da shi ba sai da na haifi Amed, a lokacin na fara ma sanin miye soyayyar namiji kuma har yau muna respecting juna, I'm a business woman like you, but nothing can deprived me daga kula da mijina. Hanifah ki riƙa kulawa da mijinki, Farooq ba ƙaramin yaro bane kuma ba ƙaramin mutum bane, karki yarda ki bar wata ƙofar da zai fara yarda da cewa bai samu matar da ta dace da shi ba. Ki duba irin kyau da zubin da Allah yayi miki ki kuma duba siffar mijin ki shima, zaku samu 'ya' ƴa masu kyau da nagarta. Hanifah from the bottom of my heart that's the only advice I have for you Ko Nasibat ce sister na iya abinda zan faɗa mata kenan, idan kin ɗauka yayi miki amfani idan baki ɗauka ba watarana zaki ce na faɗa miki haka”
Ajiyar zuciya Hanifah ta sauke tare da gyaɗa kai tace.
“Thank you Rasi. I will think about it”
Miƙewa Rasi'at tayi tace.
“Thank you for understanding. Let me bring you something, kinzo na cika ki da surutu ba tare da na kawo miki abun taɓawa ba”
Dawowa tayi hannun ta ɗauke da tray with handmade juice da Kuma tsire tana dariya tace.
“Kin zo a daidai friend saboda na yi tsiren tukunyar da kike so”
“Wow! Thank you”
Bayan ta ajiye mata tace.
"Let me check on Bahiyya, Kar taga kamar na ƙyale ta....”
Ajiye Juice ɗin hannunta Hanifah tayi tace.
“Wait Rasi! Ina Wai kika samo wannan ita kuma? I wanted to ask you na manta ne, duk shagun nan da ke akwai na masu saloon komai kuma ana yi na masu kuɗi shine zaki ƙare da wannan tana taɓa miki jikin ki har kuna dariya da ita”
Zaunawa Rasi'at tayi tana murmushi tace.
“Eyyah! She's Bahiyya by name, wallahi Malama Rabi ce ta kawo min ita, yarinyar tana da kirki bata cika hayaniya ba, kuma ta iya sosai, Abdulfatah bai cika son zuwa saloon ba shi yasa na raba kaina. Hanifah yarinyar abin a tausaya ce, Mahaifin ta ya rasu daga ita sai Mahaifiyarta da ƙanwar ta ne a nan Nigeria duk sauran dangin su suna Nijar, kuma ba zasu iya Komawa ba...”
Cikin mamaki Hanifah tace.
“And who told you all this, is she the one? Kin san buzayen nan sun iya ƙarya, so karki wani saki jiki da ita wallahi zata iya aure miki miji, daga wannan kirkin nata zaki ji zance ya canza”
Dariya sosai Rasi'at tayi sannan tace.
“No! Ba ita ce ta faɗa min ba malama ce kuma ko shi ni na tambayeta bayan Bahiyyar bata nan nace miyasa bata yin school. Allah na tuba mi Abdulfatah zai yi da Bahiyya”
Daga haka Hanifah ta miƙe ta ɗauki jakar ta tace.
“Ni dai kar ki ce ban gaya miki ba watarana, kice mi Abdulfatah zai yi da ita, ko ni da na san na fiki kyau Rasi wannan yarinyar ta Cuna min balle ke. Ni Kinga tafiyata”
Dariya sosai Rasi tayi sannan tace.
"To ba matsala ni yoruba ita Buzaye sai mu shiga asirtar juna in ga ni da ita waye zai yi nasara”
Hanifah tace.
" Maganin dai kar ayi kar a fara, ki kore ta kawai”
Ko a parlorn sai da Hanifah ta sake ca ke ta da kallon ƙurullah, ganin yadda suke ta karatu ita da Khadijat da Ahmed suna dariya yasa ta taɓe baki ta wuce abin ta.
Rasi kuwa tsiren ta kawo wa Bahiyya tace.
“Bahiyya na gaya miki daman tafiya zan yi kuma sai gashi nayi baƙuwa, lokaci kuma yanzu ya ƙure ba zaki iya yi min ba. Sai dai idan na dawo kamar zan iya kai 1week saboda auren ƙanwata ne zanje idan nadawo zan aika Malama ta kiramin ke”
Cikin girmamawa Bahiyya tace.
“Allah ya kai lafiya, ya sanya alheri ya bada zaman lafiya”
Ƙarfe biyu na rana ta saka driver ya kai Bahiyya gida bayan ta cika ta da sha tara na arziki.
***************
BAHIYYA
Duk irin ɗaukin da na shigo da shi gida akan irin abin arzikin da maman Khadijat tayi mini lokaci guda ya suranye samakon wani irin mummunan yanayin da na riski Mama a ciki. A bakin bishiyar tsakar gidan mu na iske ta kwance shame shame a jikin Nuhaira Ko motsi bata yi. Wani irin jifa nayi da duk wani abinda yake hannuna nayo kanta tare da zunduma ihu nace.
“InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Nuhaira miye ya samu Mama? Miye ya same ta dan Allah??”
Itama cikin Kuka tace.
“Nima Aunty Bahiyya ban sani ba, Ina makaranta Sharifu yazo ya kirani wai Mama tana cikin yin Niƙa a injin shi kuma yana wanke wanke kawai suka ga ta yanke jiki ta faɗi, ko da nazo har Maman Walida ta shigo tana tare da ita, ni kuma na ruga wurin mai chemist na ce ya zo dan Allah ga halin da Mama take ciki shine bayan ya zo yace kawai muyi gaggawar kai ta asibiti, to naje Malama da mijinta duk basa nan, shi ne na zauna jiranki....”
Cikin masifa na ce.
“Amma sai yau Nuhaira na yarda cewa baki da hankali, shine zaki zauna ki barta ta mutu? bayan kinji abinda likitan yace cewa ayi gaggawar kai ta asibiti, uban mi kika tsaya jira baki san in da kuɗi yake ba, wawiyar banza”
Da gudu na faɗa ɗaki na ɗauko kuɗin da ban san ma adadin nawa ba ne na fito.
Da gudu na fita waje na hau mashin naje na ɗauko mota nadawo.
In banda kuka itama Nuhairar ba abinda take sai famar bani haƙuri take tana cewa ta ruɗe ne shi yasa.
Wata private hospital muka kaita in da aka taɓa admitting ɗin ɗiyar Malama wato Umaimah. Da sauri suka karɓe mu aka shiga da ita emergency. Tare da tsare mu da tambayoyin mi ye yake damunta.
Kusan kwanan mu biyu muna reto tare da Malama har da mijinta ƙarshe suka tura mu federal medical center bayan sun caje mu kuɗi sunfi dubu hamsin.
Ni dai biye kawai nike daga Malama sai mijinta Uncle Idris suka ɗai ke kai da kawo.
Ƙarin ruwa ne ake ta yi mata da allurai, tun muna waccan asibitin ta farfaɗo amma dai tana nan zurum kawai tana bin mu da ido malama kuma ta kasa yi min bayanin komai.
Ranar da muka cika kwana huɗu a ranar akace muna result ya fito na gwaje gwajen da duk aka yi mata wanda ko a nan an caje mu kusan dubu saba'in, har kuɗin da muke da yayi ƙasa nan ta ke.
Malama ta jima a ɗakin ganin likitan sannan daga bisa ni ta zo ta kirani muka shiga tare. Shekara ta sha takwas yanzu, duk da irin ƙananun shekaru na, Ina iya fahimtar abu akan fuskonki mutane na daɗi ko aka sin haka. Kafin ma likitan ya fara mini magana naji gaba ɗaya zuciya ta ta gama tsinkewa domin ji nike a jiki na wani mummunan abu ya faru da Mama.
“Bahiyya ko?”
Likitan ne ya faɗi hakan lokacin da ya dallomin Fitilun ganin sa babu ko ƙyaftawa.
Gyaɗa kaina kawai na iya yi ina wani muzurai tamkar an tsoma kaza a ruwan zafi.
“Da ace akwai wani na gaba da ke da dashi zamu tattauna wannan zancen, but unfortunately you are the only person na kusanta da zan iya yiwa bayani, Allah yasa zaki fahimce ni”
Lumshe jiƙaƙkun idanuwa na nayi waɗan da suka shabke da ruwan hawaye na sake buɗe su akan shi nace.
“Ina jinka likita. Miye matsalar, na roƙe ku da girman Allah ku faɗa min gaskiya kada ku ɓoyemin komai, nayi muku alƙawari zamowa jajirtacciya”
“To Alhamdulillah! Bahiyya haƙiƙa kowa ne irin mutum a duniya yana da irin tashi ƙaddarar ke musulma ce saboda haka nasan addinin ku ya koyar da ku yarda da ƙaddara...”
Ta wutsiyar ido na sake ƙare mishi kallo a karo na biyu, a raina nace yanzu kai duk haibar nan taka da iya bada magana kahiri ne kenan? To kuma ji yadda yaji Hausa kamar jakin Kano.....
“Bahiyya are you listening?”
Da sauri na gyaɗa kai na alamar eh sannan yaci gaba da cewa.