Sashe 18
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Aminin babanku ne haƙƙun, tun suna yara suke abota har kasuwanci ya kawo su nan tare suka fara zuwa Nigeria, kuma tare suka kasance har mutuwa ta ɗauki babanku. Abokan taka ce ta haɗa su ba jini ba, saboda haka ba inda ƙaddarar Mahaifin ku ta shafe shi. Tun kafin ya auro ni yake xuwa nan, bayan mun aure ya dawo dani lokaci zuwa lokaci munkaje gida mu dawo, a lokacinda na haifi Ishaq yayanku kenan, Malamam yaga cewa ga ɗawainiya ta ƙaru ya kamata ace ya mallaki gidan kansa ya daina haya wanda ni kaina naga dacewar hakan domin ga sayen abinci ga kuɗin haya ga lalurar yaro ta ƙaru,daga haka sai muka yanke shawara cewa idan na tafi kai musu jariri, zai sayar da gonar guda biyu da ƙannen sa ke nomawa sannan a bashi nashi gadon Mahaifin su da ya bari. Tunda muka je kowa yake murnar zuwan mu kamar ko yaushe amma tunda yayi wa su Amadu zancen gona da kuɗin sa shikenan zance ya canza. Tun yana can ya so a siyar suka dage da lallai ya kamata ya koma wurin kasuwar sa su kuma idan suka sayar daga baya sai su haɗa komai su je da kansu su kai masa, tunda dai abin dole yana da jan lokaci, ni tunda naji sun fara mishi wannan hanya hanyar nace mishi ban yarda da su ba, amma abin ka da ɗan uwa yace min ai ba matsala, nayi sallama da iyayena da mahaifiyarsa kamar ko yaushe muka shirya muka dawo gida. Bayan dawowar mu saida akayi rabin shekara babu su Amadu babu dalilin su, tun babanku baya magana har ya fara tuntuɓa ta da zancen kai tsaye nace mishi ai saida nicce kada ka yarda dasu tun farko kace ba haka ba, ƙarshe muna nan Abu wasa wasa har aka shekare, daga nan ya yanke shawarar sake komawa yaji ina zance ya kwana, to tunda Malam ya sa ranar tafiyar nan ya kwanta wani irin mummunan ciwo wanda idan mutum ya kallesa ba zai sa ran zai ƙara kwana ba, mukayi ta yawon asibiti duk a banza, watarana sai nace mishi Malam ko dai zaka je Nijar ɗin ne daga can ka nemo magani ko Allah zai sa a dace. Sai ya girgiza kansa yace min shi yanzu ya bar zancen Nijar ɗin nan sai dai wani lokaci kuma, in faɗa muku cikin ikon Allah tunda yace ya janye tafiyar sa muka nemi ciwo muka rasa, abu kamar wasa. Muna nan kuma aka ɗauki lokaci ya sake saka ranar tafiya sai ga ciwo ya dawo kamar ba zai yi rai ba, to daga nan sai muka fara tsora ta, da kaina nace malam ka janye tafiyar nan har wani lokaci yace min ai ya bar zancen kuma shi ya ma cire rai da wannan tafiya, shima tun daga nan ciwo ya warke, haka haka tun bamu gasgata ba har muka yarda cewa akwai wani abu a ƙasa...”
Cikin tsananin firgice wa da ruɗewa nace.
“Mama karki ce min don Baba ya nemi haƙƙinsa ne Su Baba Amadu suka aikata mishi haka, kina nufin asiri suka mai kenan??”
Kuka take mai tsuma rai cikin raunatattar murya.
“Bahiyya wannan abun ba Babanku kaɗai suka yiwa ba, har da ni, domin shine silar da yasa har yau ban sake komawa tushe na ba, kuma ko yanzu ban isa nace zan tafi ba ni kaina, kuma abin da ya bamu tsoro, firgici da ban al'ajabi muka kasa warware shi har Mahaifinku ya bar duniya shine 'ƴan uwana da na Mahaifinku har yau babu wanda ya sake neman ina muke yau shekara ashirin da shida kenan rabon mu da gida, a wurin Malam maharazu kawai muke samun labarin su, a ta hannunsa ne Malam ya samu labarin rasuwar mahaifiyarsa, Nima a wurin shi na samu labarin rasuwar iyayena, da sauran Labaran dangi na daɗi ko akasinsa....”
Jikina sai ɓari yake ina wani irin kuka mai ban tausayi, cikin ruɗewa nace.
“Yanzu Mama akan abun duniya, suka rabaku da dangin ku?? Saboda abun duniya Mama! InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Kai duniya ina zaki damu,'ƴan uwanka uwa ɗaya uba ɗaya sune zasu aikata maka wannan mummunan aika aikar saboda wani ban zan abun duniya wanda dole watarana sai an barsa”
In banda kuka babu abinda Mama da Nuhaira suke, lallai tabbatas zancen Mama haka yake banga wani abun burgewa ba a cikin wannan labarin wanda har na koma ga Allah ba zan manta sa ba. Dafa kafaɗarta nayi nace a hankali nace.
“Lallai Mama da ciwo sosai a cikin rayuwar ki, wannan labarin da ban al'ajabi ya ke, Don bare yayi maka abu ba zai zama da ciwo sosai ba kamar ɗan uwanka, yanzu ta dalilin laifin babanmu shi ne ya shafe ki kema kika rasa dangin ki ba gaira ba dalili, kiyi haƙuri Mama, Wallahi Allah baya zalunci kuma baya yafe haƙƙin wani akan wani, kuma addu'ar wanda aka zalunta bata da wani shamaki tsakanin ta da ubangijin mu, na san cewa kun daɗe kuna addu'a akan wannan zaluncin da suka muku kuma muma daga yau zamu ɗora, matuƙar bamu da haƙƙin su suka yi mana wannan aika aikar to muna addu'a Allah ya bi mana haƙƙinmu a inda ba su da wani tsimi ba su da dabara”
Nuhaira ce tace.
“To Mama shi Yah Ishaq ɗin kenan ya samu zuwa Nijar ɗin kafin ya rasu??”
Gyaɗa kanta tayi tace.
“Eh! Tun zuwan da muka yi yana zanen goyo, bamu samu komawa ba har ya rasu”
Ajiyar zuciya na sauke ina ƙara jinjina girman wannan al'amari a raina na sake kallon Mama nace.
“Mama mutanen nan sun aikata kuskure, kuskure babba domin raba iyaye da ɗansu baban zunubi ne, saboda tsabar rashin imani Mama suka raba ki da duk dangin ki babu tausayar suyi tunani cewa ke fa mace ce, zuciyar ki ba zata iya jurewa ba”
Daga haka sautin kukan ta ya ƙaru sosai da ƙyar muka samu ni da Nuhaira muka rarrashe ta ta samu bawa zuciyar ta magana.
Daga haka kowa ya miƙe ya tafi wurin nasa yayin da zuciyoyinmu suka cika da rauni da damuwa.
Da dare cikin gabatar da sallar Isha, Ikram ta shigo tana mai ƙwala kiran sunana, Nuhaira ce ta tare ta tana tambayarta ya a kayi, Ina ji tace wai Maman su ce take Kirana cewa da Malama. Bayan na idar naje na sanar wa Mama na tafi.
Ina shi ga muka gaisa da Ita na samu wuri na zauna tare da rungume autar Fahaira nace.
"Gani Malama”
Tattaro nutsuwar ta tayi ta Kalleni da kyau tace.
" Bahiyya kyaun alƙawari cikawa, kuma da ilminki yadda kuka yarjejeniya da Hajiyah Hanifah ya kamata ki cika, ta kira doctor Sam ya kirani tace tana buƙatar zuwa UK ganin likita domin jikin ta ya matsa mata kuma tare take so ku wuce kamar yadda kuka alƙawaltama juna”
Gyaɗa kai nayi cikin gamsuwa da maganar ta nace.
"Haka ne malama, kyaun alƙawari cikawa. Daman can ba mantawa nayi ba, taya zan manta Malama? Matar da ta dalilin ta ne muka tsinci kanmu da sake darawa a rayuwa, ko kaɗan bana dana sani, wasu ma da ake ɗauka aikatau tun daga garin su zuwa wata uwa duniya na tsawon shekaru suyi ta wahala dare da rana ballanta kai da aikin bai taka kara ya karya ba kuma shekara ɗaya kacal. Kawai dai Mama ta nike tunani har yanzu ban iya faɗamata ba, kullum cikin zullumi nike.....”
Cike da ƙwarin guiwa tace.
“No kar ki damu in sha Allah zan yi mata bayani kuma zata fahimta da yardar Allah, ke dai abinda nike so da ke shine ki tsaya matsayin ki da Allah ya ajiye ki, ki ki ye yi kanki ki kuma zama mai wadatar zuci da godiya da duk abinda aka miki, ki riƙe ibada Bahiyya, mutanen nan sai a hankali, wasu wallahi ko ibada bata dame su ba, saboda haka kada kije ki samu canjin wuri ki ce zaki canja ɗabi'arki”
Gyaɗa kai na nayi na ce.
"in sha Allah zaki same ni mai kiyaye. Roƙona shine kuci gaba da kulamin da Mama da Nuhaira, sannan wannan kuɗin ku yanke shawara a tsakanin ku wace kasuwa za'a yi da su, ni bani da ja da hakan, Allah ya yi mana jagora”
Daga haka na miƙe tare da yi mata sai da safe na shige gida.
Bayan kwana biyu da maganar mu da malama, sai ga mama da kanta ta kirani ɗaki tace min.
“Bahiyya naji komai daga bakin Malama, ba abinda zance sai dai ince Allah ya kiyaye ki a duk in da kike, amma ba don abun yayi min daɗi a rai ba, to amma wani lokacin muna kan so abu ya zama ba alheri ba ne garemu, wani lokacin kuma sai muƙi abu ya zama shine mafi alheri a gare mu. Tace min gobe ne zaku tafi”
Cikin faɗuwar gaba na ce.
“Gobe kuma Mama??”
“Eh, tace matar tace ba tada lafiya kuma likitan na ta a can yake”
Cike da Murmushi Nuhaira ta kalle ni tace.
“Aunty Bahiyya kin ji daɗin ki ke kam, kina baƙin cikin baki je Nijar ba gashi yau Allah yayi zaki je garin da yaci uban Nijar ɗin, wani hanin ga Allah bai wa”
Ɗan guntun murmushi na saki tare da girgiza kai na nace.
“Nuhaira ba zan biye miki ba, domin ke har yanzu tunani bai gama shigar ki, in ba shi taya zaki haɗa tafiyar zumunci ta jini da wannan tafiyar da babu haɗin iya babu na Baba...”
Tare numfashi na tayi tace.
“Ni dai ba ruwa na, UK tafi Nijar, kuma dan Allah ki yo min tsaraba Aunty Bahiyya ki sawomin kayan kanti irin riga da wandon nan da naga matar nan ta saka ranar, wallahi ni dai ta burgeni ainun”
Ni dai jinta kawai nike domin can ƙasan zuciyata wani abu ni ke ji yana yimin ba daidai ba.
Cikin tsananin firgice wa da ruɗewa nace.
“Mama karki ce min don Baba ya nemi haƙƙinsa ne Su Baba Amadu suka aikata mishi haka, kina nufin asiri suka mai kenan??”
Kuka take mai tsuma rai cikin raunatattar murya.
“Bahiyya wannan abun ba Babanku kaɗai suka yiwa ba, har da ni, domin shine silar da yasa har yau ban sake komawa tushe na ba, kuma ko yanzu ban isa nace zan tafi ba ni kaina, kuma abin da ya bamu tsoro, firgici da ban al'ajabi muka kasa warware shi har Mahaifinku ya bar duniya shine 'ƴan uwana da na Mahaifinku har yau babu wanda ya sake neman ina muke yau shekara ashirin da shida kenan rabon mu da gida, a wurin Malam maharazu kawai muke samun labarin su, a ta hannunsa ne Malam ya samu labarin rasuwar mahaifiyarsa, Nima a wurin shi na samu labarin rasuwar iyayena, da sauran Labaran dangi na daɗi ko akasinsa....”
Jikina sai ɓari yake ina wani irin kuka mai ban tausayi, cikin ruɗewa nace.
“Yanzu Mama akan abun duniya, suka rabaku da dangin ku?? Saboda abun duniya Mama! InnaLillahi wa inna ilaihiraji'un! Kai duniya ina zaki damu,'ƴan uwanka uwa ɗaya uba ɗaya sune zasu aikata maka wannan mummunan aika aikar saboda wani ban zan abun duniya wanda dole watarana sai an barsa”
In banda kuka babu abinda Mama da Nuhaira suke, lallai tabbatas zancen Mama haka yake banga wani abun burgewa ba a cikin wannan labarin wanda har na koma ga Allah ba zan manta sa ba. Dafa kafaɗarta nayi nace a hankali nace.
“Lallai Mama da ciwo sosai a cikin rayuwar ki, wannan labarin da ban al'ajabi ya ke, Don bare yayi maka abu ba zai zama da ciwo sosai ba kamar ɗan uwanka, yanzu ta dalilin laifin babanmu shi ne ya shafe ki kema kika rasa dangin ki ba gaira ba dalili, kiyi haƙuri Mama, Wallahi Allah baya zalunci kuma baya yafe haƙƙin wani akan wani, kuma addu'ar wanda aka zalunta bata da wani shamaki tsakanin ta da ubangijin mu, na san cewa kun daɗe kuna addu'a akan wannan zaluncin da suka muku kuma muma daga yau zamu ɗora, matuƙar bamu da haƙƙin su suka yi mana wannan aika aikar to muna addu'a Allah ya bi mana haƙƙinmu a inda ba su da wani tsimi ba su da dabara”
Nuhaira ce tace.
“To Mama shi Yah Ishaq ɗin kenan ya samu zuwa Nijar ɗin kafin ya rasu??”
Gyaɗa kanta tayi tace.
“Eh! Tun zuwan da muka yi yana zanen goyo, bamu samu komawa ba har ya rasu”
Ajiyar zuciya na sauke ina ƙara jinjina girman wannan al'amari a raina na sake kallon Mama nace.
“Mama mutanen nan sun aikata kuskure, kuskure babba domin raba iyaye da ɗansu baban zunubi ne, saboda tsabar rashin imani Mama suka raba ki da duk dangin ki babu tausayar suyi tunani cewa ke fa mace ce, zuciyar ki ba zata iya jurewa ba”
Daga haka sautin kukan ta ya ƙaru sosai da ƙyar muka samu ni da Nuhaira muka rarrashe ta ta samu bawa zuciyar ta magana.
Daga haka kowa ya miƙe ya tafi wurin nasa yayin da zuciyoyinmu suka cika da rauni da damuwa.
Da dare cikin gabatar da sallar Isha, Ikram ta shigo tana mai ƙwala kiran sunana, Nuhaira ce ta tare ta tana tambayarta ya a kayi, Ina ji tace wai Maman su ce take Kirana cewa da Malama. Bayan na idar naje na sanar wa Mama na tafi.
Ina shi ga muka gaisa da Ita na samu wuri na zauna tare da rungume autar Fahaira nace.
"Gani Malama”
Tattaro nutsuwar ta tayi ta Kalleni da kyau tace.
" Bahiyya kyaun alƙawari cikawa, kuma da ilminki yadda kuka yarjejeniya da Hajiyah Hanifah ya kamata ki cika, ta kira doctor Sam ya kirani tace tana buƙatar zuwa UK ganin likita domin jikin ta ya matsa mata kuma tare take so ku wuce kamar yadda kuka alƙawaltama juna”
Gyaɗa kai nayi cikin gamsuwa da maganar ta nace.
"Haka ne malama, kyaun alƙawari cikawa. Daman can ba mantawa nayi ba, taya zan manta Malama? Matar da ta dalilin ta ne muka tsinci kanmu da sake darawa a rayuwa, ko kaɗan bana dana sani, wasu ma da ake ɗauka aikatau tun daga garin su zuwa wata uwa duniya na tsawon shekaru suyi ta wahala dare da rana ballanta kai da aikin bai taka kara ya karya ba kuma shekara ɗaya kacal. Kawai dai Mama ta nike tunani har yanzu ban iya faɗamata ba, kullum cikin zullumi nike.....”
Cike da ƙwarin guiwa tace.
“No kar ki damu in sha Allah zan yi mata bayani kuma zata fahimta da yardar Allah, ke dai abinda nike so da ke shine ki tsaya matsayin ki da Allah ya ajiye ki, ki ki ye yi kanki ki kuma zama mai wadatar zuci da godiya da duk abinda aka miki, ki riƙe ibada Bahiyya, mutanen nan sai a hankali, wasu wallahi ko ibada bata dame su ba, saboda haka kada kije ki samu canjin wuri ki ce zaki canja ɗabi'arki”
Gyaɗa kai na nayi na ce.
"in sha Allah zaki same ni mai kiyaye. Roƙona shine kuci gaba da kulamin da Mama da Nuhaira, sannan wannan kuɗin ku yanke shawara a tsakanin ku wace kasuwa za'a yi da su, ni bani da ja da hakan, Allah ya yi mana jagora”
Daga haka na miƙe tare da yi mata sai da safe na shige gida.
Bayan kwana biyu da maganar mu da malama, sai ga mama da kanta ta kirani ɗaki tace min.
“Bahiyya naji komai daga bakin Malama, ba abinda zance sai dai ince Allah ya kiyaye ki a duk in da kike, amma ba don abun yayi min daɗi a rai ba, to amma wani lokacin muna kan so abu ya zama ba alheri ba ne garemu, wani lokacin kuma sai muƙi abu ya zama shine mafi alheri a gare mu. Tace min gobe ne zaku tafi”
Cikin faɗuwar gaba na ce.
“Gobe kuma Mama??”
“Eh, tace matar tace ba tada lafiya kuma likitan na ta a can yake”
Cike da Murmushi Nuhaira ta kalle ni tace.
“Aunty Bahiyya kin ji daɗin ki ke kam, kina baƙin cikin baki je Nijar ba gashi yau Allah yayi zaki je garin da yaci uban Nijar ɗin, wani hanin ga Allah bai wa”
Ɗan guntun murmushi na saki tare da girgiza kai na nace.
“Nuhaira ba zan biye miki ba, domin ke har yanzu tunani bai gama shigar ki, in ba shi taya zaki haɗa tafiyar zumunci ta jini da wannan tafiyar da babu haɗin iya babu na Baba...”
Tare numfashi na tayi tace.
“Ni dai ba ruwa na, UK tafi Nijar, kuma dan Allah ki yo min tsaraba Aunty Bahiyya ki sawomin kayan kanti irin riga da wandon nan da naga matar nan ta saka ranar, wallahi ni dai ta burgeni ainun”
Ni dai jinta kawai nike domin can ƙasan zuciyata wani abu ni ke ji yana yimin ba daidai ba.