← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 23

Sashe 22

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bansan cewa da ɗan renin hankalin mijinta zamu tafi ba sai da muka haɗu a filin jirgin. Ina ganin sa na ɗauke kai na kamar ban gansa, har ita matar yau bata samu gaisuwa domin gani nike kamar tilasta mata nike wurin ansa gaisuwar yawa saboda haka yau sai na hutar da ita.

Banza nayi da su na mayar da hankali na wurin bawa ido na abinci domin ganin abinda ban taɓa gani ba a rayuwata sai yau.

Yadda na nuna ban damu da su ba suma haka sukayi min sai da naga sun miƙe nima da sauri na bi bayan su, wani mutum sai faman kallo na yake sai da yagan ni kusa da mijin Hanifahr sannan yayi murmushi ya mishi magana da cewa.

"Congratulations! Two beautiful wives at young age, nice family....”

Take Hanifah taji jinin ta ya shiga tafasa ta kalle shi rai a ɓace tace.

" Please would you mind your business? I'm his wife alone, banga abinda ya shafe ka da rayuwar mu ba, minafiki kawai”

Daga haka mutumin ya wuce gaba abinshi zuciyar sa fal da mamakin Hanifah.
Mijin shi kuma yana tsaye kawai baice uffan ba. Ita kuma sai ta dawo bayan Mijin nata a maimakon da can da take gaban sa shi kuma yana bayan ta ni kuma a bayansa sai ya zamana ya shiga tsakiyar mu. Yanzu kuma sai ta dawo ita ce a tsakiya ni kuma a bayan ta.

Tana yi tana jan tsaki har muka shiga jirgin muka zauna wanda har yanzu fatar baki na da nasu bai haɗu ba, tafiya tamkar ta jaraba.............

*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝

*ADABI WRITERS ASSOCIATION*

               *BY*
*AMINA IBRAHIM*
  *(OUM-AMIR)*

*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*

*LAST FREE PAGE*
      *LAST FREE PAGE*
          *LAST FREE PAGE*

*A nan muka kawo ƙarshen free pages in Sha wadda take so sai tayi payment ga account a sama taci gaba da karatu hankali kwance*

*FREE PAGE*
     *BABI NA GOMA SHA BIYAR*

BAHIYYA

  Mijinta ne ya fara wucewa ya zauna sannan ta zauna sai ni a ƙarshe, sai wani haɗe rai take tamkar an tilasta mata dole tafiya DANI, wanda a yanzu abun har mamaki ya ke ba ni. Sosai na shiga morewa bawa idona abinci, domin wata duniya ce ta daban na tsinci kaina a yau, Ina cikin kalle-kalle na a hankali bayan komai ya gama dai-dai ta jirgin ya fara tafiya a slow lokaci guda nayi tsit! nayi tamkar wadda ruwa suka cinye na fara zare ido, domin yanayin jin tafiyar jirgin yasa gabaɗai sai na ji ni ba dai-dai ba, kafin kace mi tuni jikina ya ɗauki mazari, akan tsabagen tsoro da firgici, Ina jin an yi wata fisga wani abu ya kaɗa can cikin hanta ta tamkar numfashi ne zai ɗauke ga wani jiri da ya ɗibeni, wata irin razananniyar ƙara na saki tare ƙanƙame hannun Hajiya Hanifah na runtse ido gam, Ina faɗin.

“Wayyo Allah Mama na! Na shiga uku, wallahi mutuwa zanyi, wayyo! Ni wallahi ku sauke ni tsoro nike ji, zamu faɗa ƙasa wallahi.....”

Wata irin muguwar tsawa Hanifah ta daka min tare da faɗin.

“Hey! What sort of nonsense is this? Ki na da hankali kuwa?”

Still idanuwana a rufe kuma hannun ta riƙe gam a nawa nayi saurin girgiza kai nace.

"Wallahi tsoro ni ke ji...”

Ganin yadda kowa ya zuro ido yana kallon mu shi ya sanya Hanifah jin wata irin matsananciyar kunya,take tayi ƙasa da kanta saitin kunnena murya a ƙasa ƙasa tace.

“Sai na miki mugun wulaƙanci idan kika sake ko tarin ki na ƙara ji, banza village girl kawai. Cikamin Hannuna!”

Da sauri na sake mata hannun ta kamar yadda ta ce, na riƙe gefen handle ɗin kujerar jirgin da ƙarfin tsiya, Ina ta karanto duk addu'ar da ta zo baki na,a raina ina istigfari ina ta kuma neman gafarar iyayena domin ban zaci numfashi na zai ci gaba da wanzuwa ba a ruhun jiki na.

Daga haka a hankali tsoron da ya mamaye dukkan ilahirin jikina ne ya fara tafiya a hankali yana bari na.

Farooq kuwa tsabar baƙin ciki da takaici tunda ya kallo ni sau ɗaya ya ɗauke kansa. A jikin seat ɗin ya jingina tare da kwantar da kansa ya lumshe ido yana ji wani ƙarin haushina ya na cika masa zuciya.

A cure nike wuri ɗaya na kasa yin wani ƙwaƙwƙwaran motsi, sai da yaje sauke a hankali tsoron ɗazu ya fara dawomin, rufe baki na nayi a wannan karon tare da runtse idanuwana ina ta addu'a cikin raina.

Ganin an fara miƙewa nima na miƙe na basu wuri suka fara yin gaba sannan na bi bayan su.

Mutumin ɗazu ne ya ƙara biyoni ya kalle ni da murmushi a fuskar sa yace.

“Hey pretty, Is this your first time being in plane?”

Gyaɗa kaina kawai nayi duk da cewa ban gama fahimtar mi yake faɗi ba.

Ɗan sake murmusawa yayi yace.

“Eyyah! Sorry....”

Sai kuma ya miƙomin hannunsa yana faɗin.

“I'm Shuraim Tafidah by name”

Ganin na maƙale hannun na ya sashi sakin dariya yace.

"OK! I understand, please can we be friends... Yeah, friends only...”

Tsinkayo muryar Hanifah nayi cike da masifa tana faɗin.

" Malama zaki zo mu tafi ne ko kuma mubarki a nan tare da shi?”

Zare ido nayi tare da yin gaba da sauri na bar shi a baya. Biyo bayan mu yayi yana murmushi yace.

" Haba Aunty! Kin ce ba mijin ku ɗaya ba kuma yanzu kin hana ta saurare ni hakan ba dai-dai ba ne....”

Sai kuma ya juya ga Farooq yace.

“Yayah please zan iya samun numbern ta? numbernta kawai”

Ina ga tunda ƙaddarar tafiyar nan ta haɗamu ban san ya waigo ko sau ɗaya ya kalleni ba sai yanzu. Kallo na yayi sama da ƙasa kallon da ke sakani ina jin matuƙar haushin sa domin sai inga tamkar kashi ya ɗauke ni marar amfani bayan su ne suka ɗauko ni don ƙashin kansu.
Sai da ya gama kallona sannan yace.

“I don't have any business with her, ruwanta tayi abinda take so”

Wani kallon tsana na bishi da shi a raina nace wato shi gani mai zaman kanta na fito yawon Bariki kenan ko? Lallai mutumin nan ban san ƙiyayyar tasa da ni ta kai haka ba sai yau.

Hanifah kuma dariya ce ta so suɓuce mata, yanzu ace classy guy kamar wannan ya tsaya wai zai karɓi numbern wannan village girl ɗin. Bai san ta ba ne shiyasa da zaran yasan wacece ba zai taɓa marmarin haɗa class ɗin shi da ita ba.

Daga ƙarshe sukayi gaba abin su suka barni nima ba shiri na bi bayan su raina cike da tsanar halayyar da suka nuna min ni ba baiwar su ba domin ba saya ta sukayi ba. Wannan tafiya wannan tafiya ta zame min ƙarfen ƙafa nikam Bahiyya. Allah ka nuna ranar da zan yasar da ƙwallon mangoro in huta da ƙuda.

Shuraim ma cikin rashin fahimtar wannan hargitsatstsiyar tafiya tasu kawai ya juya ya kama gaban sa. A ransa yace in dai da rabon ya sa meta in sha Allah watarana za su sake haɗuwa.

*************

Finchley Road, Hampstead.
London, United Kingdom.

Tun a mota nike ta kalle kallen gine-ginen benaye masu tsawo da kuma bala'in kyau, ga garin yayi duhu sai Fitilu kake gani masu azabar kyau da ɗaukar hankali. Ba ƙaramin burgeni garin yayi ba.

A hankali naga munyi parking a dai-dai wani bene mai masifar kyau ko a ta fuska.

Suna fita nima nabi su baya, bayan mun shiga gidan wani parlour ne babba na gammu a ciki wanda yaji kayan alatu iri da iri.

A nan na samu wani cushion mai laushi na ɗosana ɗuwawu na yayin da su kuma suka shiga ciki.
Kalle kalle kawai nike ina ta mamaki a raina cewa banga kowa a gidan ba kawai sa kai sukayi suka shigo, ko gidan waye wannan oho?

Sun ɓata kusan minti yafi talatin sannan daga ƙarshe ta shigo kamar ba zata min magana ba sai kuma tace min in biyo ta.

Ba musu na tashi na bi bayanta, wata hanya ce muka bi daga cikin parlourn sai gashi ta sadamu da wani katafaren ɗaki mai ɗauke da komai na more rayuwa.

“Nan shi ne ɗakin ki daga yau har ranar da contract ɗin mu zai ƙare.”

Daga haka ta fice ni kuma na taɓe baki, domin a yadda ta ɗauke ni nima haka na ɗauke ta, duk yadda suke ɗaukata yarinya dole ina da hankali da tunani dai-dai irin wanda Allah ya bani, a hakan nasan kyautatawa kuma nasan musgunawa. duk da cewa wata zuciyar na faɗin a irin taimakon da tayimin ta cancanci girmamawa da mutuntuwa sosai daga wuri na. To amma halin da take nuna min ne bana so.

Kan gadon na faɗa rub da ciki. Ina ta tunanin wannan sabuwar rayuwar da na tsinci kaina a cikin ta, ko wace kalar rayuwar zamu gurza a nan? Allah ma sani.
Nocking naji anyi, hakan yasa ni miƙewa da sauri naje na buɗe, wani mutum na gani fari ɗauke da tiren abinci a hannun sa. Jin yayi min wani kalar yaren da ban gama tantance cewa turanci ba ne ko yaya yasa na juya abina na koma ciki. Baya na ya biyo tare da ajemin tiren ya na sake yi min magana. Kamar in tartse shi da mari haka naji, banzaye kawai marasa aikin yi. Wata zuciyar ta ce min ko laifin mi sukayi min Oho!

Yana fita na sauko na bubbuɗe abincin, daman can yunwa na ciciyata. Hmmm! Kawai Kallon kalar abinci nike a raina ina faɗin uban waye zai ci muku wannan abun.
Naman kajin na zage na cinye duk da ba magin albarka a ciki, na shanye madarar da na fiso na ɗora da shan fruit da akayi slizing ɗin su a wani haɗaɗɗen bowl. Nan naji cikina ya ɗauka sannan na tashi na shige toilet na yi wanka na fito na buɗe kayana da aka shigo min da shi na ɗauki wasu riga da wando masu taushi ga faɗi na saka sannan na sanya hijabi na tayar da sallah.
Chapter 22 · 0% Book details