Sashe 20
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga haka kuma ta jani muka shiga bedroom wanda ko toilet ɗin kaɗai abin kallo ne, muka dawo ta sake nuna min wai inda kitchen yake duk a cikin wannan ɗan madaidaicin part ɗin, komai yayi kyau ba ƙarya. Bayan ta gama nuna min ta jani toilet ta shiga koyamin yadda zan yi amfani da komai na toilet ɗin bayan mun gama muka koma kitchen nan ma ta nuna min, muka dawo Parlour ta nuna yadda a kunna TV da AC da sauran su. Daga haka tace min zata je ta dawo.
Kan kujera na zauna tare da ƙurawa TV ido ina kallo, a raina ina mamaki wai yau nice a nan wai a gaban wannan tangamemen TV ace wai ƙarƙashin iko na yake. Allah mai yadda ya so kenan.
Nan na ƙaraci zamana daga ƙarshe da na duba agogon da ke manne a bangon parlourn nan na gane cewa har lokacin sallar Asr yayi gashi ko zuhr ban yi ba. Da sauri na wuce toilet ɗin daman can na saba amfani da irin su a irin gidajen su Maman Khadijat, so sai ban sha wata wahala ba
nayi alwala na zo na tayar da Sallah na gabatar da salloli na. Bayan na gama na sake komawa parlourn naci gaba da kallo har magrib tayi.
Bayan na idar da sallahr magrib ne sai matar dai ta ɗazu ta sake dawowa hannayenta ɗauke da warmers ɗin abinci sai wata matar a bayan ta sanye da kalar wani uniform a jikin ta ta ajiye kayan hannun ta ta fice.
Murmushi na sakar mata kamar yadda itama naga tayi min, tace min sannu. Nima sannun na mayar mata tare da kafe ta da ido ina jira in ji mi kuma zata faɗa mun.
“Wannan abincin Dinner ɗin ki ne, wannan kuma kayan amfani ne yanzu zan nuna miki yadda zaki yi amfani ko wane abu a nan”
Ni dai babu abinda nike sai binta da kallo, kaya ne tundaga na sanyawa har zuwa kayan gyaran jiki su mayukka da na gyara gashi da takalmi da sauran su. Komai sai ta tayi min bayanin shi ɗaya bayan ɗaya daga ƙarshe tace min duk abinda ban gane ba na riƙa tambayar ta don kada a samu matsala,ni ko a raina na tambayi kai na nace matsala? Wace irin matsala to? Ganin bani da amsar ta yasa na sake mayar da hankali na ga kallon ta yayin da taci gaba da yi min bayani. Komai da aka kawo min mai kyau ne, kayan dai ne nagan su wasu iri domin ni ba kayan da sukayi daidai da tsari na bane, gaba ɗaya kayan daga riga da wando sai riga da skirt, sai kuma Abayas sun kai shida, to suka ɗai ne nikejin a raina cewa zan iya sanyawa amma su kam waɗancan haram shan giya a gidan Malam, mamaki na babu atamfa ko kala ɗaya a ciki.
Da dare ma haka na kwanta a kan gadon tare da janyo bargo na rufe jikina saboda sanyin ACn da yake ratsani.
Sati ɗaya na kwashe a gidan ba tare da na sake sanya Hajiya Hanifah a ido na ba, wannan matar da a yanzu na saba da ita Nafisat itace kaɗai ni ke gani, ta dage sosai wurin koyar da ni abubuwa waɗanda tuni nayi nisa sosai a iya wasu abubuwan wasu kuma sai dai a hankali, ni kaina idan na kalli madubi na kan yarda da cewa jiki na ya canza sosai ba kamar yadda na zo ba, tsabar hutu da cin kayan daɗi iri iri,ko gashin kai na ban san cewa ina da dogon gashi sosai mai santsi ba sai yanzu da ya ke shan gyara a wurin Aunty Nafisat domin haka tace in riƙa kiranta.
A kwana na takwas ne ina zaune, bayan na gama sallar azahar ina tunanin su Mama a raina sai ga Aunty Nafisat ta shigo tacemin in shiryo mu tafi madam tana nemana. Lokaci guda annurin fuskata ya ɓace tare da jin wani irin faɗuwar gaba take na hau karanto addu'o'i. Daman nayi wanka already, wata Abaya ce maroon colour na ɗauko na saka tare da ɗaura ɗan kwalin na sake zura hijabi na a kai na cimma Aunty Nafisat Parlour muka tafi.
Wani parlourn ne na daban mai faɗi gaske ta nuna min yayin da ta juya daga bakin ƙofar ta koma abinta. Sai da na tsaya na gama sai ta kaina sannan na shiga ɗauke da sallama a baki na.
Ganin ta yau tare da wani wanda da alama mijinta ne yasa na tsaya tun daga nesa na tsuguna a ƙasa gaba na sai tsananta faɗuwa yake tamkar wadda za'a yanka naman jikin ta.
Na jima tsugune a wurin yayin da sukayi tamkar basu ganni ba suna ta maganar su a ƙasa ƙasa. Sai daga baya ta kalle shi tace.
“Farooq she's our surrogate...”
Sai kuma ta kalle ni tace.
"Hey! Look here. Kallo nan, tashi tsaye ya ganki”
Miƙewa nayi tsaye tare da kallon in da yake zaune kamar yadda ta umurce ni, sai dai daga ƙasƙantaccen kallon da naga ya fara bi na da shi ne yasa naji jikina yayi sanyi, kallo ne wanda har in koma ga Allah ba zan manta da shi ba duk da cewa ban san manufarsa ba. Wanda har cikin raina na ji na muzanta na kuma kunyata.
Cike da izgili ya zare ido ya kalli Hanifah yace.
“What! Oh no! It can't be possible Hanifah.Look at her Fa, wannan tsuntsuwar mi zata iya? daga ganin wannan ma abinci bai wadaci jikin ta ba, saboda haka she can't carry my baby gaskiya....”
Da sauri Hanifah tace..............
*OUM AMEER*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JDbgcC7yQyC5NhQw9Q1jFl💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA SHA HUƊU*
.......... “She can do it Farooq, I have already started preparing her, da shawarar doctor Nicholas ni ke amfani, he planned all the necessary nutrients for her so that she and our baby will be in good condition. Beside we are gonna stay together with her, So is our duty to take good care of her”
Girgiza kan shi yayi tare da kallon Hanifah yace.
"Hanifah! Hanifah har yanzu kina ganin cewa akan daidai kike?”
With full confidence tace.
“I'm 100% sure love, in sha Allah everything will go smoothly beyond your expectations”
Taɓe baki yayi tare da sake kallo na a karo na biyu, tun daga ƙasa na har sama sannan yace.
“While tunda har kince hakan yayi miki is ok. You can ask her to leave”
“Ki tafi”
Abinda na ji kenan ta faɗa, hakan yasa na juya na fice zuciya ta na wani tuƙuƙin baƙin ciki. Wai shin mi masu kuɗi suka ɗauki kan su ne a duniyar nan? ba fa saya ta suka yi ba ballantana suce yadda suka ga dama za su yi dani, ji wani kallon wulaƙancin da ya ke min tamkar an tilasta shi dole sai ya kalle ni banza a banza kawai, idan kuna taƙamar kuɗi ai Allah ba ruwan shi da wannan da zukata yake aiki ba jiki ba ko wani abin mutum mtsww! Wai harda Kirana Tsuntsuwa tsabar raina halittar Allah ko miye marabar matarsa da ni Oho! Don itama naga ba wani jikin a zo a gani ne da ita ba. ita kuma wannan matar bana tunanin ma cewa ta san suna na domin ko da wasa ban taɓa jin ta kira ni ba tsabar wulakanci, ni sai a yau nayi baƙin cikin rashin jin yaren nasara da bana ji kuma bana iya mayarwa, ɗan abinda nikeji da wanda nike iya mayarwa ɗin banji sunyi ko ɗaya ba ballantana in ce na fahimta domin da ina ji nasan tabbas zan fahimci ina suka dosa miye suke magana a kai. Kuma ai ban tilasta ta ba itace ta zaɓeni idan ban musu ba su mayar dani gidan Mama na mana. Tsaki na ja sai kuma a raina nace, ko ma dai miye ni dai buƙatata ta biya tunda har Mama ta samu lafiya ai shi kenan. Maimakon in ganni na ɓilla ƙofa ta kawai gani na nayi a wani wurin na daban, cikin ruɗewa na fara zare ido na rasa ina zan nufa, ga shegun mutanen har masu aiki wai turanci suke yi tsabar kinibibi da sanabe, domin duk wacce naga zasu yi magana da Aunty Nafisat da turanci suke yi so ba ni da halin in tambayi wani. Ina nan tsaye kamar an dasa Icce sai Aunty Nafisat na gani tana faɗin
“Bahiyya ina zaki je ne? Kin sani sai faman neman ki ni ke”
Dariya nayi kamar wata sakarya nace.
“Wallahi Aunty Nafisat manta hanyar nayi, kawai sai na tsinci kaina a nan”
“Eyyah sorry. To yanxu biyoni muje”
Babban kitchen ne ta jani wanda tunda ni ke ban taɓa ganin kitchen irin shi ba,komai an shirya shi bisa tsari gwanin burgewa. waigowa tayi ta kalle ni tace.
“Mi kike so ki ci yanzu?”
Cikin Mamaki na ce.
“Ai ban jima da cin abinci ba ko kin manta”
Girgiza kai tayi tace.
“Ban manta ba, Hajiya ce tace ki riƙa cin abinci time to time ba dole sai kina jin yunwa ba”
Cikin rashin fahimtar zancen nata nace.
“Bana jin yunwa, amma ki bani madarar nan mai daɗi irin ta ranar sannan ki haɗamin da naman kaza dafaffe”
"OK to muje in rakaki kada ki ƙara manta hanyar, Yanxu zan kawo miki”
************
HANIFAH
Bayan fitar Bahiyya zaunawa tayi kan cinyar sa tasa hannu tana yamutsa sumar kansa da ta sha gyara sosai tana murmushi tace.
“Ba lallai suna samun abinci mai gina jiki yadda ya kamata ba, but mu a nan zamu iya bata, Nafisat is taking good care of her, sannan Kuma wani gefen halittar jikin ta ne haka, kada ka damu. Gobe in sha Allah we will go to the hospital together for possible investigation, Idan an gama screening ɗinta Sai mu wuce kawai, you will become a father soon as you wish”
Kallonta yayi yace.
“Hanifah ya zamuyi da su Daddy ya zamuyi da Madinah?”
Kan kujera na zauna tare da ƙurawa TV ido ina kallo, a raina ina mamaki wai yau nice a nan wai a gaban wannan tangamemen TV ace wai ƙarƙashin iko na yake. Allah mai yadda ya so kenan.
Nan na ƙaraci zamana daga ƙarshe da na duba agogon da ke manne a bangon parlourn nan na gane cewa har lokacin sallar Asr yayi gashi ko zuhr ban yi ba. Da sauri na wuce toilet ɗin daman can na saba amfani da irin su a irin gidajen su Maman Khadijat, so sai ban sha wata wahala ba
nayi alwala na zo na tayar da Sallah na gabatar da salloli na. Bayan na gama na sake komawa parlourn naci gaba da kallo har magrib tayi.
Bayan na idar da sallahr magrib ne sai matar dai ta ɗazu ta sake dawowa hannayenta ɗauke da warmers ɗin abinci sai wata matar a bayan ta sanye da kalar wani uniform a jikin ta ta ajiye kayan hannun ta ta fice.
Murmushi na sakar mata kamar yadda itama naga tayi min, tace min sannu. Nima sannun na mayar mata tare da kafe ta da ido ina jira in ji mi kuma zata faɗa mun.
“Wannan abincin Dinner ɗin ki ne, wannan kuma kayan amfani ne yanzu zan nuna miki yadda zaki yi amfani ko wane abu a nan”
Ni dai babu abinda nike sai binta da kallo, kaya ne tundaga na sanyawa har zuwa kayan gyaran jiki su mayukka da na gyara gashi da takalmi da sauran su. Komai sai ta tayi min bayanin shi ɗaya bayan ɗaya daga ƙarshe tace min duk abinda ban gane ba na riƙa tambayar ta don kada a samu matsala,ni ko a raina na tambayi kai na nace matsala? Wace irin matsala to? Ganin bani da amsar ta yasa na sake mayar da hankali na ga kallon ta yayin da taci gaba da yi min bayani. Komai da aka kawo min mai kyau ne, kayan dai ne nagan su wasu iri domin ni ba kayan da sukayi daidai da tsari na bane, gaba ɗaya kayan daga riga da wando sai riga da skirt, sai kuma Abayas sun kai shida, to suka ɗai ne nikejin a raina cewa zan iya sanyawa amma su kam waɗancan haram shan giya a gidan Malam, mamaki na babu atamfa ko kala ɗaya a ciki.
Da dare ma haka na kwanta a kan gadon tare da janyo bargo na rufe jikina saboda sanyin ACn da yake ratsani.
Sati ɗaya na kwashe a gidan ba tare da na sake sanya Hajiya Hanifah a ido na ba, wannan matar da a yanzu na saba da ita Nafisat itace kaɗai ni ke gani, ta dage sosai wurin koyar da ni abubuwa waɗanda tuni nayi nisa sosai a iya wasu abubuwan wasu kuma sai dai a hankali, ni kaina idan na kalli madubi na kan yarda da cewa jiki na ya canza sosai ba kamar yadda na zo ba, tsabar hutu da cin kayan daɗi iri iri,ko gashin kai na ban san cewa ina da dogon gashi sosai mai santsi ba sai yanzu da ya ke shan gyara a wurin Aunty Nafisat domin haka tace in riƙa kiranta.
A kwana na takwas ne ina zaune, bayan na gama sallar azahar ina tunanin su Mama a raina sai ga Aunty Nafisat ta shigo tacemin in shiryo mu tafi madam tana nemana. Lokaci guda annurin fuskata ya ɓace tare da jin wani irin faɗuwar gaba take na hau karanto addu'o'i. Daman nayi wanka already, wata Abaya ce maroon colour na ɗauko na saka tare da ɗaura ɗan kwalin na sake zura hijabi na a kai na cimma Aunty Nafisat Parlour muka tafi.
Wani parlourn ne na daban mai faɗi gaske ta nuna min yayin da ta juya daga bakin ƙofar ta koma abinta. Sai da na tsaya na gama sai ta kaina sannan na shiga ɗauke da sallama a baki na.
Ganin ta yau tare da wani wanda da alama mijinta ne yasa na tsaya tun daga nesa na tsuguna a ƙasa gaba na sai tsananta faɗuwa yake tamkar wadda za'a yanka naman jikin ta.
Na jima tsugune a wurin yayin da sukayi tamkar basu ganni ba suna ta maganar su a ƙasa ƙasa. Sai daga baya ta kalle shi tace.
“Farooq she's our surrogate...”
Sai kuma ta kalle ni tace.
"Hey! Look here. Kallo nan, tashi tsaye ya ganki”
Miƙewa nayi tsaye tare da kallon in da yake zaune kamar yadda ta umurce ni, sai dai daga ƙasƙantaccen kallon da naga ya fara bi na da shi ne yasa naji jikina yayi sanyi, kallo ne wanda har in koma ga Allah ba zan manta da shi ba duk da cewa ban san manufarsa ba. Wanda har cikin raina na ji na muzanta na kuma kunyata.
Cike da izgili ya zare ido ya kalli Hanifah yace.
“What! Oh no! It can't be possible Hanifah.Look at her Fa, wannan tsuntsuwar mi zata iya? daga ganin wannan ma abinci bai wadaci jikin ta ba, saboda haka she can't carry my baby gaskiya....”
Da sauri Hanifah tace..............
*OUM AMEER*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JDbgcC7yQyC5NhQw9Q1jFl💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMIR)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA GOMA SHA HUƊU*
.......... “She can do it Farooq, I have already started preparing her, da shawarar doctor Nicholas ni ke amfani, he planned all the necessary nutrients for her so that she and our baby will be in good condition. Beside we are gonna stay together with her, So is our duty to take good care of her”
Girgiza kan shi yayi tare da kallon Hanifah yace.
"Hanifah! Hanifah har yanzu kina ganin cewa akan daidai kike?”
With full confidence tace.
“I'm 100% sure love, in sha Allah everything will go smoothly beyond your expectations”
Taɓe baki yayi tare da sake kallo na a karo na biyu, tun daga ƙasa na har sama sannan yace.
“While tunda har kince hakan yayi miki is ok. You can ask her to leave”
“Ki tafi”
Abinda na ji kenan ta faɗa, hakan yasa na juya na fice zuciya ta na wani tuƙuƙin baƙin ciki. Wai shin mi masu kuɗi suka ɗauki kan su ne a duniyar nan? ba fa saya ta suka yi ba ballantana suce yadda suka ga dama za su yi dani, ji wani kallon wulaƙancin da ya ke min tamkar an tilasta shi dole sai ya kalle ni banza a banza kawai, idan kuna taƙamar kuɗi ai Allah ba ruwan shi da wannan da zukata yake aiki ba jiki ba ko wani abin mutum mtsww! Wai harda Kirana Tsuntsuwa tsabar raina halittar Allah ko miye marabar matarsa da ni Oho! Don itama naga ba wani jikin a zo a gani ne da ita ba. ita kuma wannan matar bana tunanin ma cewa ta san suna na domin ko da wasa ban taɓa jin ta kira ni ba tsabar wulakanci, ni sai a yau nayi baƙin cikin rashin jin yaren nasara da bana ji kuma bana iya mayarwa, ɗan abinda nikeji da wanda nike iya mayarwa ɗin banji sunyi ko ɗaya ba ballantana in ce na fahimta domin da ina ji nasan tabbas zan fahimci ina suka dosa miye suke magana a kai. Kuma ai ban tilasta ta ba itace ta zaɓeni idan ban musu ba su mayar dani gidan Mama na mana. Tsaki na ja sai kuma a raina nace, ko ma dai miye ni dai buƙatata ta biya tunda har Mama ta samu lafiya ai shi kenan. Maimakon in ganni na ɓilla ƙofa ta kawai gani na nayi a wani wurin na daban, cikin ruɗewa na fara zare ido na rasa ina zan nufa, ga shegun mutanen har masu aiki wai turanci suke yi tsabar kinibibi da sanabe, domin duk wacce naga zasu yi magana da Aunty Nafisat da turanci suke yi so ba ni da halin in tambayi wani. Ina nan tsaye kamar an dasa Icce sai Aunty Nafisat na gani tana faɗin
“Bahiyya ina zaki je ne? Kin sani sai faman neman ki ni ke”
Dariya nayi kamar wata sakarya nace.
“Wallahi Aunty Nafisat manta hanyar nayi, kawai sai na tsinci kaina a nan”
“Eyyah sorry. To yanxu biyoni muje”
Babban kitchen ne ta jani wanda tunda ni ke ban taɓa ganin kitchen irin shi ba,komai an shirya shi bisa tsari gwanin burgewa. waigowa tayi ta kalle ni tace.
“Mi kike so ki ci yanzu?”
Cikin Mamaki na ce.
“Ai ban jima da cin abinci ba ko kin manta”
Girgiza kai tayi tace.
“Ban manta ba, Hajiya ce tace ki riƙa cin abinci time to time ba dole sai kina jin yunwa ba”
Cikin rashin fahimtar zancen nata nace.
“Bana jin yunwa, amma ki bani madarar nan mai daɗi irin ta ranar sannan ki haɗamin da naman kaza dafaffe”
"OK to muje in rakaki kada ki ƙara manta hanyar, Yanxu zan kawo miki”
************
HANIFAH
Bayan fitar Bahiyya zaunawa tayi kan cinyar sa tasa hannu tana yamutsa sumar kansa da ta sha gyara sosai tana murmushi tace.
“Ba lallai suna samun abinci mai gina jiki yadda ya kamata ba, but mu a nan zamu iya bata, Nafisat is taking good care of her, sannan Kuma wani gefen halittar jikin ta ne haka, kada ka damu. Gobe in sha Allah we will go to the hospital together for possible investigation, Idan an gama screening ɗinta Sai mu wuce kawai, you will become a father soon as you wish”
Kallonta yayi yace.
“Hanifah ya zamuyi da su Daddy ya zamuyi da Madinah?”