← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 23

Sashe 5

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun lokacin shekarun gwagwarmayar sa ya kasance Pediatrician Doctor a ƙasar sa Nigeria, sai kuma Allah ya haɗa shi da ƙungiyar NGO's wanda a hankali ya zama sanadiyyar samun matsayi a United Kingdom ƙarƙashin ƙungiyar Saboda Ɗan-Ali ya kasance Jajirtacce mai ƙwazo wurin aiki shiyasa ya zama lamba ɗaya. Daga baya ya dawo da matarsa Nuriyyat suka ci gaba da zama wanda a nan a ka Haifi Hanifahr  da kuma Hamrah, haka yayi ta aiki kala kala daga nan UK zuwa gida Nigeria da kuma businesses da ya keyi na daban daban tsawon shekaru. Shekara 4 da suka gabata ya samu zama jekadan Nigeria a ƙasar Cairo Egypt, in da suka dawo nan da zama a yanzu.
   Hanifah tayi karatu har zuwa matakin Degree a nan UK a fannin Business, ta taso cikin gata da samun cikakken 'ƴan ci wanda ya bata damar yin duk abinda taga dama kuma ta yarda da cewa a duniyar nan babu abinda ya ke fin ƙarfin ta matuƙar zata nema sai ta samu saboda suna da kuɗi da freedom, Hanifah ta waye ta buɗe ido da rayuwa tayi karance karance iri iri, ta sha shiga ƙungiyoyin matasa mata da maza domin ta ƙara samun gogewa da kuma iya zaman duniya.
A hanyar ta ta zuwa Nigeria daga UK wurin wani gagarumin taron ƙarama juna sani a harakar business suka haɗu da Farooq suka ƙulla abota daga nan kuma ta juye zuwa Soyayya, Hanifah bata so auren ba a wannan lokacin ganin irin naci da tsananin sonda Farooq ya nuna mata yasa ta saukar da kai bori ya hau.
Ga shi kuma Allah ya haɗa jinin Daddy da Farooq sosai domin ganin irin ci gaban da Farooq ya samu a irin ƙananun shekarunsa abin alfahari ne kuma yayi amanna cewa Hanifah ta samu mijin da ya dace da matsayin ta haka ma a wurin Hajiya Nuriyyat.
Ba'a ɗauki dogon lokaci ba Madinah ta shirya da wakilanta aka shirya zancen aure ba ɓata lokaci akayi gagarumin bukin da ya amsa sunan shi buki, an sha daga sosai da Hanifah domin cewa tayi ita fau-fau ba zata zauna a Nigeria ba, Farooq yasha matuƙar wahala kafin ya samu ya shawo kanta akan tayi hak'uri ta zauna a Nigeria sai da aka haɗa da su Madinah wurin bata baki. Shine dalilin da yasa ya tafi Life Camp ya tantatsa mata gida naji da gani a Abuja sannan ya zuba mata masu aiki birjik da body guide kamar yadda ta buƙata. Wanda lokacin baya iyaka ya zo Abuja wurin harakar business ɗin sa idan ya gama ya koma Kaduna.
  A irin  karance-karance da kalle kallen da Hanifah tayi da kuma mu'amalantar mutane daban daban a fadin duniya yasa ta fahimci cewa rayuwar aure kawai cike take da takurawa da kuma wahala da ƙarewa da ɗaukar nauyin namiji kullum, ko kuma ayi ta samun domestic violence sanadiyyar rashin jituwa tsakanin ma'aurata musamman wasu ma'auratan akan 'ƴa' ƴa za'a yi ta samun saɓani. Shi yasa ita a aƙidar ta ba zata iya sakarwa namiji jiki ba ko da yaushe yayi ta duk abinda ya ga dama da ita. Sannan ganin yadda mata ke shan wahala tun wurin ɗaukar ciki yana farko har zuwa haihuwa da shayarwa abin ba ƙaramin ɗaga mata hankali ya ke ba, ga wahala kuma ita babbar damuwar ta ma shine idan mace ta ɗauki ciki a hankali cikin zai fara buɗewa yana girma saboda abdominal muscles zasu riƙa stretching a hankali given room for a baby to grow well, Daga zaran Kuma ta haihu sai cikin ya canja shape ya buɗe, sannan ga tear da ake samu ko kuma a bada episiotomy lokacin labour daga nan vagina ɗin mace ta samu matsala, a wurin breastfeeding Kuma breast zasu lakuce su canza shape suyi sagging, Idan kuma CS shima dai duk uwa ɗaya suke domin sai kin samu scar, sannan kuma ka dawo renon yaro yayi ta kuka kana rarrashi duk a banza, yayi kashi yayi fitsari. Ita a ganin ta duk wannan wahala ce is better kawai kayi zamanka a haka. Ganin yadda Farooq ya ɗauke ta tare da nuna mata tsantsar kula da bata freedom yasa ta saki jikinta tana abin ranta yake so, duk abinda Hanifah tace shi kenan ya zauna ko da ya masa daɗi ko bai masa ba shi dai kawai ya na so ya faranta mata suyi rayuwar auren su cikin soyayya da kaunar juna.

Tsawon shekara bakwai da tayi a Nigeria bata fi zuwa huɗu ba Kaduna wurin Madinah, ita ma kuma Madinah ganin kalar matar da Farooq ɗin ya aura sai ta ja wa kanta layi da shiga al'amarin ta. Itama Madinah tunda aka kawo Hanifahr sau biyu ta taɓa zuwa Abuja gidan ta, a lokacin aurenta da kuma sanda ta buɗe Ɗan-Ali Decor and event center.

Daga haka sai dai ta waya idan sun samu sararin gaisawa.

Ci gaban labari.........

Zaune suke a palourn Daddyn da yamma suna tsara yadda tafiyar su zata kasance gobe. Hamrah ta kalli Hanifah tace.

“Fav Sis Yah Farooq ba zai zo bane?”

Zaro ido tayi tace.

“What! Inji wa, yana nan zuwa daga zaran mun isa in sha Allah”

Hamrah tace.

“Ah to, ai naga yah Farooq ɗin ne kamar anyi masa kafi a Nigeria duk sanda zamuyi waya na tambaye ki shi sai ki ce min yana office”

Hannunta Hanifah ta ɗauke daga kan system ɗin da take aiki a kai ta kalli Hamrah tace.

“But  I said he's coming, ba shi kenan ba”
Daga nan kuma ta kalli Daddy tace.

“Daddy please sai kayi magana da su na tura musu kalar furnitures ɗin da nike so ayi amfani da su”

Yace
“OK!”

Washe gari ƙarfe tara jirgin su ya ɗaga zuwa Dubai.

**************

Abuja
      Nigeria

Kusan watan Hanifah biyu da tafiya Farooq har yayi tafiye tafiye kusan sau huɗu zuwa Kenya da London. A duk lokacin da ya shigo gida ji yake can ƙasan ransa yana mugun jin kewar matarsa but bashi da abinda zai yi sai dai ya jira dawowar ta.
Yanzu ma kwance yake kawai a ɗakin ta yayi shiru yana ta karanta wasiƙar jaki.
Bayan ya kai kusan 1hour a kwance daga ƙarshe ya tashi kamar wanda aka tsikara ya je ya shirya ya nufi gidan Mahi.

Ganin shi tsaye a balcony ɗin gidan nasa yayi matuƙar bashi mamaki.

“Yaushe kama dawo ƙasar ban sani ba, har gaka tsaye a cikin gidana?”

Kallon sa yayi yace.

“Da safe, na kiraka baka ɗauka ba”

“Wallahi a lokacin tana hannun Amrah 'yar rigima. Juyawa yayi ya nufi Parlour yana faɗin....  Shigo ciki mana”

Parlour suka shiga yaje ya kira Husnah matarsa ta fito ta gaishe sa, Zarah da Amrat ma suka gaishe sa cikin ladabi ya amsa duk da maganar Amrat ba wani fita sosai ta ke yi ba because she's just 3years, Zarah Kuma itace babba wadda zatayi 6years.

Cikin shaƙiyanci Mahi yace.

“Husnah kawo wa gauron nan abinci dan Allah, nasan akwai yunwa tare da shi”

Harararsa Farooq yayi yace.

"You are not serious, Yanxu Haka na baro abincin da aka jera min a gida ko taɓawa banyi ba”

Mahi yace.

“Saboda mai gidan bata nan shiyasa komai ya fita a ranka ko?”

Maganar suke amma kallon Yaran da ke wasa jikin Mahi shi ya ɗauke masa hankali. Amrah ce da ƙaramin ƙanin ta Haidar wanda he's just 8 month now.
Zarah Kuma tana gefe da littafanta tana rubuta. Wannan yanda ake ta drama da Amrah da Haidar shine abinda ya burgesa, Amrah ta kafe akan Lallai sai Haidar ya sauka itama ta hau, shi kuma daga zaran an ɗaga shi sai ya fara kuka, ganin taƙi samun yadda ta ke so kawai sai ta fasa ihu ta faɗi ƙasa zata fara birgima.
Lokaci guda Farooq ya ɗaga ta sama ya ɗora ta akan thigh ɗinsa yana murmushi ya gyara mata tsorayen kalbanta da suka sha bit zuwa baya yace.

"Is ok.....”

Kuka kawai take tana nuna Mahi da Haidar tana faɗin.

" Abbah... Abbah ne, Haidar...”

“Shiihhh! It OK! Sai na yiwa Abbah duka”

Mahi kuwa sai dariya yake yana jefa Haiydar sama suna ƙyaƙyata dariya.
Husnah ce ta katse su da faɗin.

“Abbahn Zarah na gama shirya abincin”

“Owk, thank you, zo ki shiga da yaran nan ciki ya samu ya ci abincin.”

Zarah najin haka ta miƙe ta kwashe tarkacenta ta shige ciki. Husnah ta zo cikin nutsuwarta  ta karɓi Haiydar da ƙyar ta amshi Amrah daga jikin Farooq shi kuma sai murmushi yake yana lallaɓa ta har ta tafi.

Suna kan cin abincin ya ajiye spoon ɗin hannunsa ya kalli Mahid cikin damuwa yace.

“Mahi am missing Hanifah so much. Sai mu yi kusan kwana biyu bamuyi waya ba idan taga na matsa mata da kira sai ta ɗauka ta fara bani excuses ɗin cewa she's busy shi yasa bata samun cikakken lokacin magana dani ba.”

Ganin damuwa kwance ƙarara akan fuskar sa yasa a hankali Mahi ya shiga kwantar masa da hankali yace.

"Haba Farooq kamar ba ka san sha'anin kasuwa ba,kafi kowa sanin irin wahala da gwagwarmayar da ake shiga musamman idan zaka kafa branch in da ba ƙasar ka ba yafi komai wahala kafi kowa sanin haka. Is a matter of time kayi mata uzuri nasan itama ba don tana jin daɗin hakan ba da ta riga ta gama shikenan. Yanzu a ina aka tsaya da zancen”

Ajiyar zuciya ya sauke because sai yanxu yaji ɗan sauƙi sauƙin abinda ya taru ya danne masa zuciya. Yace.

“she spend almost 6weeks a Cairo Sai last two weeks suka Isa Dubai ɗin amma ta faɗamin Friday ne bukin zai gudana.”

Mahi yace.
“To ai shi kenan, kaga zuwa Friday komai ya ƙare za kuma iya dawowa tare”

Farooq yace
“Hmmm! Allah yasa”

Mahi yace
“Amin”

Miƙewa yayi tare da kallon Mahi yace.
“Thank you for the food. Ina so zan tafi Kaduna gobe da safe in sha Allah tun last month da naje har yanxu bata sake gani na ba”

“Owk! Allah ya tsare ka gaida min ita”

****************

Malali
Kaduna state
           Nigeria
Chapter 5 · 0% Book details