Sashe 10
Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai bayan ya dawo ya wuce ɗakin Madinah direct ya cimma bata nan, ba kayan ta, Wayar ta ya kira kai tsaye tace mishi gata a Kaduna. Abin yayi matuƙar bashi mamaki kamar wadda ake kora, ya rasa ya ta ɗauki Hanifah a rayuwar ta ko dai surukar ta ce iyaka kenan.
Ko da ya shigo bata nan, dining ɗin ya wuce ya ci abinci sannan ya shige ciki. Kwantawa yayi yay lamo yana tunani. Shi yanzu ya gama yankewa ba zai sake matsawa Hanifah ba akan buƙatarsa ba domin ɓacin rai ne kawai zai yi ta addabar sa, shiyasa yanzu ya yankewa kansa yin azumi domin ya riƙa samun sauƙi.
Yana nan yaji an murɗa handle ɗin ƙofar a hankali, ko bai duba ba yasan wacece ta shigo.
Kwantawa tayi akan ƙirjinshi ta saƙala hannayenta cikin wuyan shi. A hankali taji sautin Muryar sa yana faɗin
“Hanifah time yayi da ya kamata ace munyi settling mun samu yara, duk wannan maganar taki a baya ba tunani ba ne”
Cikin fargaba da tashin hankali tace.
“What! Haba Farooq yanzu duk tsawon lokacin nan da muka ɗauka ba ma tare da abinda zaka tare ni kenan? Bayan kasan cewa abinda ba zai yi yu ba ne....”
“Zai yi yu mana Hanifah,I'm fertile you are fertile too, to minene ba zai yi yu ba a nan?”
“Farooq No!”
“Hanifah abinda nike so kenan”
Miƙewa tayi without thinking twice kawai ta bar mishi ɗakin, abinda ba zai taɓa ma yiyu wa ba kenan. To Farooq Wai ko dai ya fara shaye shaye ne? Kawai kuma sai tayi tsaki domin babu abinda ya faɗo mata a rai sai Grand Ma Madinah da Mahid, ta sani sarai duk sune manyan munafukai da suke so su sanya mata ido a rayuwar gidanta. Ba ta taɓa jin ta tsani Madinah ba a rayuwar ta ba sai yau.
Ƙarshe kwanciyar ta tayi abinta tayi baccin ta ta ƙyale shi bata sake komawa kan shi ba, domin ta gama yankewa a ranta komai zai faru ba zata amince da wannan shirmen nasa ba, iyakaci dai ya gama fushi da ya huce zai dawo, ballantana ma tasan Farooq ba ya iya fushi da ita.
Washe gari ko da ta fito har ya fice daga gidan ko break fast Bai yi ba, nan ya bar mata kayanta yayi tafiyar sa.
Wanda hakan ba ƙaramin shayar da ita mamaki yayi ba.
Waya ta ɗauka tayi ta kashin wayar sa amma yaƙi ɗagawa, Ƙarshe sai ga text ya turo mata kamar haka.
“Ki amsamin buƙata ta kawai Hanifah”
Ajiye wayar tayi tare da zaunawa tayi break fast ɗin ta sannan ta shirya ta fita.
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMEER)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BAKWAI*
BAHIYYA
Yau ma da wani irin matsanancin faɗuwar gaba na farka sakamakon mummunan mafarkin da nayi a daren jiya,wanda har yafi wanda na saba yi a kullum muni. A sukuku na fito ɗaki bayan na gama sallah tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, ɗakin mama na shiga na gaidata sannan na fito waje na zauna na buga tagumi ina karanta wasiƙar jaki. Ganin wankin hula na nema ya kai ni dare ga tarin ayyukana a gaba na yasa ni yunƙurawa da nufin miƙewa sai kwatsam Malama tayo Sallama ta shigo.
Cike da mamaki na amsa mata sallamar ta domin duk da cewa ban duba agogo ba nasan cewa iyaka ƙarfe shida ne yanzu na safe.
Da sauri tace min.
“Bahiyya ina mamanku? Yi maza ki shirya mu tafi Maman Khadijat ta kira ni yanzu tace dan Allah ki zo tafiya biki ta kama ta garin su ki zo kiyi mata lalle zuwa ƙarfe biyu zata wuce.”
Nima miƙewa nayi cikin sauri nace.
“Mama tana ciki bari naje to na shirya”
Bayan sun gaisa da Mama tayi mata bayani na shiga ɗaki na ɗanawa Nuhaira duka a cinya saboda takaicin baccin da take kwantawa bayan asuba, duk da cewa tasan tana zuwa school amma akan mugun bacci kullum sai ta sake kwanciya bayan sallar Asuba.
Firgigit ta miƙe cike da mita tace.
“Haba Aunty Bahiyya!”
Cikin jin haushi nace.
"Dan Allah ta shi kije ki nema abinda zaku karya ni fita zanyi, kada kiyi latti”
Miƙewa tayi tare da yin gunguni ta zo ta wuce nima naje na yiwa Mama Sallama muka tafi.
Ina jin daɗin zuwa gidan Maman Khadijat masu kuɗi ne na gaske amma babu ruwanta, ta iya sakin jiki da kowa, bata da wulaƙanci, hakama 'yar ta Khadijat da ta ke ji da ita, Allah ya haɗa jinin mu da ita sosai, bata ma wani jin Hausa sosai ni kuma ba wani dogon turanci nike ji ba, haka zamu zauna in tsantsara mata kalar kitson da suka nuna min in yi mata lalle tayi ta santi, tana ce min Aunty Bahiyya Thank you.
Hakama yayanta Ahmad da zaran ya ganni muna haɗa ido zai sakar min murmushi yace. Aunty Bahiyya hi! Mamar take gayamin cewa kullum idan suna fira ta sai yayi ta ce mata ina da kyau sosai ina burgeshi. Shiyasa ni ke jin daɗin zuwa gidan domin ba su da matsala.
*************
HANIFAH
Duk iya ƙoƙarin ta tayi akan cewa taga ta shawo kan Farooq amma abu ya faskara, zata iya cewa tunda take da shi wani abu makamancin haka bai taɓa shiga tsakanin su ba, duk yadda zasu samu ƙololuwar misunderstanding bai taɓa ɗagawa daga wurin ba sai ya tabbata ya shawo kanta komai ya wuce. Baya fushi da ita kai zata iya cewa ma basu taɓa samun makamancinyar wannan matsalar ba, domin zata iya bugun gaba ta tsaya ko a gaban waye tayi alfahari da mijinta tace yafi na kowa kaf a faɗin duniya.
Amma yau Farooq ne yake gudun ta, ko da zata farka ta wayi gari ya wuce abinshi ko da zata dawo daga office kuma bai dawo wa gidan ba sai cikin dare ya ke shigowa koda zai shigo tayi bacci.
Ranar da ta ritsa shi kuma sai ya wayance mata yace aiki ne yayi masa yawa a Office shiyasa.
Har office ta je ta sameshi yace mata taje gida idan ya gama zai dawo haka ta koma amma ƙarshe ma da ta bincika wai yayi tafiya zuwa Kenya.
Ganin ta kasa gane masa yasa ta shirya da wuri ta wuce gidan Rasi'at her best friend.
Tana shiga gidan ta cimma Rasi'at rungume da Khadijat Bahiyya na yi mata kitso.
Murmushi Rasi'at tayi tana mai kallon ƙawarta ta tace.
“Welcome Hanifah”
Ƙugu Hanifah ta riƙe cikin mamaki tace.
“Wai Rasi har yanzu ba zaki sararawa kanki ba ki daina ɗora Khadijat a jikin ki, yarinya shekara bakwai amma kullum kin maidata kamar 'ƴar shekara ɗaya.”
Khadijat waving ɗin hannunta tayi da lalle tana murmushi domin bata ma fahimci wane zancen Hanifah ke yi ba tace.
“Hi' Aunty Hanifah! See my beautiful Henna Aunty Bahiyya done it for me”
Duba lallen tayi tana murmushi tace.
“Wow! You look beautiful Baby, how are you?”
Khadijat tace.
“I'm fine, welcome...... ”
Sai kuma ta kalli Bahiyya tace.
“Aunty Bahiyya can't you greet Aunty Hanifah? But you are the one that told me to be greeting our visitors”
Sai yanzu Bahiyya ta ɗago cike da kunya ta kalli Hanifah tace.
“Ina wuni”
Kallon ta Hanifah tayi up and down sannan tace lafiya ta sakai ta wuce Babban farlourn Rasi'at.
Cikin hanzari Rasi'at ta sauke Khadijat daga jikin ta tacewa Bahiyya su ci gaba tana zuwa.
Tana shiga ta iske Hanifah ta dafe goshinta alamar damuwa ta bayyana akan fuskar ta tace.
“Friend is there any problem?”
Hanifah mace ce mai zurfin ciki da wuya abu ya dameta ta nemi wani ta faɗa mishi ko mahaifiyarta bata iya faɗawa abinda yake damunta in dai ba ta kama dole ɗin sai ta sanar mata ba.
Gyara zama tayi cikin damuwa ta fallasawa Rasi'at sirrin ta gaba ɗaya komai bata ɓoye mata ba har abinda ya faru a Dubai tsakanin ta da Farooq sai da faɗa mata.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su na ɗan lokaci sannan Rasi'at ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Hanifah tace.
“You are at fault for everything Hanifah,kuma kin bani mamaki matuƙa. Miye a cikin haihuwa da zaki ce ba zaki iya ba? 'ƴa' ƴa sune farin ciki Hanifah, knock senses in to your brain, ba'a haihuwa aka haifeki?.....”
“Look Rasi, please I just need a way out, ni ba wani dogon zance nike so ba”
Cike da ɓacin rai Rasi'at tace.
“You are not serious Hanifah! Wallahi you better shine eyes, tunda har mijinki ba haka yake ba ta ƙarfin tsiya kika canja shi to ina tabbatar miki kwaɓarki tana gab da yin ruwa. Ni ban ma taɓa jin miji irin Farooq ba, abu sai kace a film ko a novel, duk abinda kika ga dama shi kike yi kuma wai ranshi bai taɓa ɓaci ba, ji abinda kika ce kin Mishi a Dubai kuma ya dawo kiran ki sannan kika dawo gida yace miki ba komai komai ya wuce, wallahi in baban Amed ne a ranar sai na gane nayi kuskure. Miye a cikin haihuwa? na haifi Amed gashi shekara Goma na haifi Khadijat she's seven years now, kinga wani abu ya fita a jiki na?....”
With full confidence Hanifah tace.
“Wallahi kin ragu Rasi, ke kanki kin san ba zaki taɓa haɗa kanki da wacce ba ta taɓa haihuwa ba irina”
Rasi tace.
Ko da ya shigo bata nan, dining ɗin ya wuce ya ci abinci sannan ya shige ciki. Kwantawa yayi yay lamo yana tunani. Shi yanzu ya gama yankewa ba zai sake matsawa Hanifah ba akan buƙatarsa ba domin ɓacin rai ne kawai zai yi ta addabar sa, shiyasa yanzu ya yankewa kansa yin azumi domin ya riƙa samun sauƙi.
Yana nan yaji an murɗa handle ɗin ƙofar a hankali, ko bai duba ba yasan wacece ta shigo.
Kwantawa tayi akan ƙirjinshi ta saƙala hannayenta cikin wuyan shi. A hankali taji sautin Muryar sa yana faɗin
“Hanifah time yayi da ya kamata ace munyi settling mun samu yara, duk wannan maganar taki a baya ba tunani ba ne”
Cikin fargaba da tashin hankali tace.
“What! Haba Farooq yanzu duk tsawon lokacin nan da muka ɗauka ba ma tare da abinda zaka tare ni kenan? Bayan kasan cewa abinda ba zai yi yu ba ne....”
“Zai yi yu mana Hanifah,I'm fertile you are fertile too, to minene ba zai yi yu ba a nan?”
“Farooq No!”
“Hanifah abinda nike so kenan”
Miƙewa tayi without thinking twice kawai ta bar mishi ɗakin, abinda ba zai taɓa ma yiyu wa ba kenan. To Farooq Wai ko dai ya fara shaye shaye ne? Kawai kuma sai tayi tsaki domin babu abinda ya faɗo mata a rai sai Grand Ma Madinah da Mahid, ta sani sarai duk sune manyan munafukai da suke so su sanya mata ido a rayuwar gidanta. Ba ta taɓa jin ta tsani Madinah ba a rayuwar ta ba sai yau.
Ƙarshe kwanciyar ta tayi abinta tayi baccin ta ta ƙyale shi bata sake komawa kan shi ba, domin ta gama yankewa a ranta komai zai faru ba zata amince da wannan shirmen nasa ba, iyakaci dai ya gama fushi da ya huce zai dawo, ballantana ma tasan Farooq ba ya iya fushi da ita.
Washe gari ko da ta fito har ya fice daga gidan ko break fast Bai yi ba, nan ya bar mata kayanta yayi tafiyar sa.
Wanda hakan ba ƙaramin shayar da ita mamaki yayi ba.
Waya ta ɗauka tayi ta kashin wayar sa amma yaƙi ɗagawa, Ƙarshe sai ga text ya turo mata kamar haka.
“Ki amsamin buƙata ta kawai Hanifah”
Ajiye wayar tayi tare da zaunawa tayi break fast ɗin ta sannan ta shirya ta fita.
*OUM AMEER*
💝 *BAHIYYA*💝
*ADABI WRITERS ASSOCIATION*
*BY*
*AMINA IBRAHIM*
*(OUM-AMEER)*
*BAHIYYA NOVEL ƊIN KUƊI NE KIBIYA 500 TA WANNAN ASUSUN 3132703269 FIRST BANK AMINA IBRAHIM SAI KI TURA SHAIDAR BIYA TA WANNAN LAYIN 08068974831*
*FREE PAGE*
*BABI NA BAKWAI*
BAHIYYA
Yau ma da wani irin matsanancin faɗuwar gaba na farka sakamakon mummunan mafarkin da nayi a daren jiya,wanda har yafi wanda na saba yi a kullum muni. A sukuku na fito ɗaki bayan na gama sallah tamkar kazar da ƙwai ya fashewa a ciki, ɗakin mama na shiga na gaidata sannan na fito waje na zauna na buga tagumi ina karanta wasiƙar jaki. Ganin wankin hula na nema ya kai ni dare ga tarin ayyukana a gaba na yasa ni yunƙurawa da nufin miƙewa sai kwatsam Malama tayo Sallama ta shigo.
Cike da mamaki na amsa mata sallamar ta domin duk da cewa ban duba agogo ba nasan cewa iyaka ƙarfe shida ne yanzu na safe.
Da sauri tace min.
“Bahiyya ina mamanku? Yi maza ki shirya mu tafi Maman Khadijat ta kira ni yanzu tace dan Allah ki zo tafiya biki ta kama ta garin su ki zo kiyi mata lalle zuwa ƙarfe biyu zata wuce.”
Nima miƙewa nayi cikin sauri nace.
“Mama tana ciki bari naje to na shirya”
Bayan sun gaisa da Mama tayi mata bayani na shiga ɗaki na ɗanawa Nuhaira duka a cinya saboda takaicin baccin da take kwantawa bayan asuba, duk da cewa tasan tana zuwa school amma akan mugun bacci kullum sai ta sake kwanciya bayan sallar Asuba.
Firgigit ta miƙe cike da mita tace.
“Haba Aunty Bahiyya!”
Cikin jin haushi nace.
"Dan Allah ta shi kije ki nema abinda zaku karya ni fita zanyi, kada kiyi latti”
Miƙewa tayi tare da yin gunguni ta zo ta wuce nima naje na yiwa Mama Sallama muka tafi.
Ina jin daɗin zuwa gidan Maman Khadijat masu kuɗi ne na gaske amma babu ruwanta, ta iya sakin jiki da kowa, bata da wulaƙanci, hakama 'yar ta Khadijat da ta ke ji da ita, Allah ya haɗa jinin mu da ita sosai, bata ma wani jin Hausa sosai ni kuma ba wani dogon turanci nike ji ba, haka zamu zauna in tsantsara mata kalar kitson da suka nuna min in yi mata lalle tayi ta santi, tana ce min Aunty Bahiyya Thank you.
Hakama yayanta Ahmad da zaran ya ganni muna haɗa ido zai sakar min murmushi yace. Aunty Bahiyya hi! Mamar take gayamin cewa kullum idan suna fira ta sai yayi ta ce mata ina da kyau sosai ina burgeshi. Shiyasa ni ke jin daɗin zuwa gidan domin ba su da matsala.
*************
HANIFAH
Duk iya ƙoƙarin ta tayi akan cewa taga ta shawo kan Farooq amma abu ya faskara, zata iya cewa tunda take da shi wani abu makamancin haka bai taɓa shiga tsakanin su ba, duk yadda zasu samu ƙololuwar misunderstanding bai taɓa ɗagawa daga wurin ba sai ya tabbata ya shawo kanta komai ya wuce. Baya fushi da ita kai zata iya cewa ma basu taɓa samun makamancinyar wannan matsalar ba, domin zata iya bugun gaba ta tsaya ko a gaban waye tayi alfahari da mijinta tace yafi na kowa kaf a faɗin duniya.
Amma yau Farooq ne yake gudun ta, ko da zata farka ta wayi gari ya wuce abinshi ko da zata dawo daga office kuma bai dawo wa gidan ba sai cikin dare ya ke shigowa koda zai shigo tayi bacci.
Ranar da ta ritsa shi kuma sai ya wayance mata yace aiki ne yayi masa yawa a Office shiyasa.
Har office ta je ta sameshi yace mata taje gida idan ya gama zai dawo haka ta koma amma ƙarshe ma da ta bincika wai yayi tafiya zuwa Kenya.
Ganin ta kasa gane masa yasa ta shirya da wuri ta wuce gidan Rasi'at her best friend.
Tana shiga gidan ta cimma Rasi'at rungume da Khadijat Bahiyya na yi mata kitso.
Murmushi Rasi'at tayi tana mai kallon ƙawarta ta tace.
“Welcome Hanifah”
Ƙugu Hanifah ta riƙe cikin mamaki tace.
“Wai Rasi har yanzu ba zaki sararawa kanki ba ki daina ɗora Khadijat a jikin ki, yarinya shekara bakwai amma kullum kin maidata kamar 'ƴar shekara ɗaya.”
Khadijat waving ɗin hannunta tayi da lalle tana murmushi domin bata ma fahimci wane zancen Hanifah ke yi ba tace.
“Hi' Aunty Hanifah! See my beautiful Henna Aunty Bahiyya done it for me”
Duba lallen tayi tana murmushi tace.
“Wow! You look beautiful Baby, how are you?”
Khadijat tace.
“I'm fine, welcome...... ”
Sai kuma ta kalli Bahiyya tace.
“Aunty Bahiyya can't you greet Aunty Hanifah? But you are the one that told me to be greeting our visitors”
Sai yanzu Bahiyya ta ɗago cike da kunya ta kalli Hanifah tace.
“Ina wuni”
Kallon ta Hanifah tayi up and down sannan tace lafiya ta sakai ta wuce Babban farlourn Rasi'at.
Cikin hanzari Rasi'at ta sauke Khadijat daga jikin ta tacewa Bahiyya su ci gaba tana zuwa.
Tana shiga ta iske Hanifah ta dafe goshinta alamar damuwa ta bayyana akan fuskar ta tace.
“Friend is there any problem?”
Hanifah mace ce mai zurfin ciki da wuya abu ya dameta ta nemi wani ta faɗa mishi ko mahaifiyarta bata iya faɗawa abinda yake damunta in dai ba ta kama dole ɗin sai ta sanar mata ba.
Gyara zama tayi cikin damuwa ta fallasawa Rasi'at sirrin ta gaba ɗaya komai bata ɓoye mata ba har abinda ya faru a Dubai tsakanin ta da Farooq sai da faɗa mata.
Shiru ne ya ratsa tsakanin su na ɗan lokaci sannan Rasi'at ta sauke ajiyar zuciya ta kalli Hanifah tace.
“You are at fault for everything Hanifah,kuma kin bani mamaki matuƙa. Miye a cikin haihuwa da zaki ce ba zaki iya ba? 'ƴa' ƴa sune farin ciki Hanifah, knock senses in to your brain, ba'a haihuwa aka haifeki?.....”
“Look Rasi, please I just need a way out, ni ba wani dogon zance nike so ba”
Cike da ɓacin rai Rasi'at tace.
“You are not serious Hanifah! Wallahi you better shine eyes, tunda har mijinki ba haka yake ba ta ƙarfin tsiya kika canja shi to ina tabbatar miki kwaɓarki tana gab da yin ruwa. Ni ban ma taɓa jin miji irin Farooq ba, abu sai kace a film ko a novel, duk abinda kika ga dama shi kike yi kuma wai ranshi bai taɓa ɓaci ba, ji abinda kika ce kin Mishi a Dubai kuma ya dawo kiran ki sannan kika dawo gida yace miki ba komai komai ya wuce, wallahi in baban Amed ne a ranar sai na gane nayi kuskure. Miye a cikin haihuwa? na haifi Amed gashi shekara Goma na haifi Khadijat she's seven years now, kinga wani abu ya fita a jiki na?....”
With full confidence Hanifah tace.
“Wallahi kin ragu Rasi, ke kanki kin san ba zaki taɓa haɗa kanki da wacce ba ta taɓa haihuwa ba irina”
Rasi tace.