← Book details Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 23

Sashe 13

Bahiyya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Duk gudun Hanifah da ya ke ba wai yana yinsa ne cikin daɗin rai ba, sai dai kawai yana so ta amince da buƙatarsa su samu ɗa tare kamar yadda Mahi ya bashi shawara, shi a plan ɗin sa Idan har ta amince ta haihu wata ƙila zasu iya samun fahimtar juna yadda yake so, idan ta haihu it may be ta fara sanin muhimmancinsa da kuma bashi damar da zai ji cewa yes shi ɗin mijinta ne. Domin abinda tayi masa ranar da ta dawo Nigeria tayi matuƙar bashi Mamaki, taya za'a ce duk tsawon lokacinda suka ɗauka basa tare saboda kawai ya yi mata zancen haihuwa zata hau dokin zuciya har ta iya barinsa tayi tafiyar ta ɗakin ta, to shi dutse ne da baya da zuciya a cikin ƙirjinsa ko ya ya?

Shiyasa kawai ya bata iska wata ƙila nisantar ta zaisa taji ko kaɗan ne a cikin ranta cewa tayi masa ba dai dai ba. Allah ne shaidar sa da irin tsananin son da yake yiwa HANIFAH, ya na so su rayu cikin soyayya da kulawar juna, yayi mata duk abinda take so haka shima tayi masa duk abinda yake so
amma ita sam bata gane hakan a wurinta ba abu mai yiyuwa ba ne, saboda haka he must take action Ko da zai sa ta shiga hankalin ta.

Idan yana tuna irin stories ɗinda Madinat ke basa dangane da rayuwar ta da mijinta Modu sai yaji ina ma ace Hanifah zata amince suyi irin wannan rayuwar tare da juna.

Ya jima tsaye a balcony ɗin gidan nasa kafin daga bisa ni yaja ɗan guntun tsaki ya shige cikin gidan, turus sukayi suna masu kallon juna tamkar yau ne ranar haɗuwar su ta farko.

Murmushin yaƙe yayi mata wanda iya ka cinsa kan leɓensa sannan yace.

“Hi..”

Da gudu taje ta rungume sa tare da sakin wani rikitaccen kuka tana faɗin.

“Why? Why are you doing all this to me? Farooq Ko ka daina so na ne ka faɗa min inji?”

Jin yanda take kuka yasa zuciyar sa jin wani irin ba daɗi.

Hannayensa ya sanya ya zagaye bayan ta a hankali yace.

“Idan na daina sonki wa zan so a duniyar nan? You are my heart beat Hanifah, da sonki kaɗai zuciya ta take bugawa. So ni ke mu haihu Hanifah, idan har kina so na kasance cikin farin ciki to tabbas ki amince ki haihu dani”

Janyewa tayi ta koma jikin faɗeɗiyar windown palourn tana mai zurawa waje ido tace.

“Sai naji kamar zan iya Farooq sai kuma zuciya ta tayi ta nuna min ba haka ba, ɗan Allah Farooq kayi haƙuri.....”

“No Hanifah, ni a yanzu shine kaɗai ni ke so daga gare ki”

Cikin ƙara ji tace.

“Toh let's adopt a child mana, zamu iya, yes we can get as many children as we want Saboda muna da dukiyar da zata iya bamu ko adadin 'ya' ƴa nawa muke so...”

Runtse idanunsa yayi tare da girgiza kansa sannan ya buɗe yace.

"No Hanifah! That's not part of my plan, ba zan iya adopting child ba as far as ubangiji na ya bani lafiyar samun yara bani da wata naƙasa....”

Rintse idanunta tayi tare da yarfar da hannuwanta alamar zancen ya fara harzuƙa ta tace

“OK... OK! We can get a child through Surrogacy, Hakan yayi maka?”

A matuƙar mamakance ya kalleta yace.

“What!..”

Da sauri ta zo ta zauna in da yake zaune tare da cukuikuye hannunsa ta karyar da wuya in a pleading tone tace.

"Dan Allah mana Farooq ka amince. Ƙwanmu dai ka ke so ka gani a duniya ko? To we can achieve it through Surrogacy, Sperm ɗinka za'a haɗa da Egg ɗina a dasa cikin mahaifar wata macen in 9 months data haife mana shi kenan sai ta kama gabanta...”

“No Hanifah...”

Wani Sabon kukan ta sake fashe masa da shi, tana faɗin.

“Dan Allah mana Farooq! Dan Allah ka amince, matuƙar kana sona kana kuma son farin ciki na to ka amince.”

A duniya cikin abubuwan da Farooq ya tsana a rayuwar sa akwai kukan Hanifah ciki, baya son kukanta ko kaɗan baya so.
Ba tare da wani tunani ba yace.

“Shi kenan na amince. But yanzu a ina kike ganin zamu samun macen da zata amince tayi mana wannan sacrifice ɗin.”

Cikin murmushin nasara tace.

“No kar ka damu, just leave everything in my hand, Ni zan samo macen da kaina, babu zancen sacrifice a nan tunda biya zamuyi, kawai dai everything have to be in secret between us daga zaran 9 months yayi ta haife sai ta kama gabanta”

Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace.

“OK. Allah yasa a dace”

“Amin sweet heart, let me ask Nafisat to prepared table for us, today is a special day to us. Thank you”

Murmushi yayi mata yace.
“Thank you too Hanifah, I love you”

Matsowa tayi gab da shi ta yi brushing lips ɗinta da na shi sannan ta kalle shi tace.

“Na miss I dey miss you Love”

Miƙewa yayi cikin jindaɗi ya miƙa mata hannu yace.

“Shall we?”

Itama hannun ta miƙa masa suka nufi sashen sa, da taimakon ta yayi wanka yau tana tare da shi har ya gama shiryawa suka zo dining yaci abinci, sannan suka wuce nata ɗakin itama ta shirya. Soyayya suka sha abinsu tamkar wani abu na ɓacin rai bai shiga tsakanin su ba, Farooq ya zage ya nuna mata irin yadda yayi mugun missing ɗinta,That's her sweet test wanda yake mugun driving ɗinsa crazy, ga taushin fatarta da take shan gyara kullum da kuma haɗaɗɗen ƙamshinta mai canza duniyar sa zuwa wata duniya mai wuyar fassarawa.

A daren ranar through out tare suke maƙale da juna ta zamto masa wata kalar Hanifah ta daban tamkar yau ya fara sanin ta.

Da gari ya waye tana gama shiryawa suka yi break fast shaf-shaf ta ɗauko Jakarta ta na dariya ta kalle shi tace.

“Mission started, so I need your absolute support”

Murmushi yayi yace.

“My support is always there with you Hanifah, bye bye”

Daga haka ta fice.

Tun a hanya ta kira Doctor Nicho tace mishi she's on her way coming ya samu matar, yace mata ya samu, cikin farin ciki tayi mishi godiya kafin ta ƙara sa.

Tana zuwa kuwa ya tarbeta, bayan sun gaisa yace.

“She's Agnes by name, er asalin jihar Oyo ce, ta amince ne bayan na gabatar mata da manufarki.....”

“OK.. Bani Account na ta in fara bata kafin alƙalami”

Ba musu ya janyo wayar sa ya buɗe details ɗinda already ta riga turo mai ya bata account number ɗin take yanke ta tura mata 5million.

Ba'a fi minti biyar ba sai ga kiranta ya shigo wayar Doctor Nicho, Hanifah tayi zaton godiya zatayi kawai ta ji ta fara bragging cewa mi ta ɗauke ta ne talaka ko me, kamar ita da girman ta tana neman irin wannan sacrifice ɗin amma ta tura 5million wannan ai abin kunya ne, ya faɗa mata kuɗin aikin ta tunda har lafiyar ta ƙalau haihuwa ce bata so to zata bayar da 100 million idan yayi mata to idan kuma bai yi ba shikenan.

Da sauri Hanifah tace.

“Tell her that I will pay the money, kawai ta zo a fara shirye shirye.”

Bayan ya gaya mata abinda Hanifah tace, sai tace. Ita yanzu haka ma bata ƙasar, su jira idan ta dawo zata neme su but ta tura kuɗi kawai idan zata tura. Kai tsaye ta sake ca ke mata 45 plus wancan ya zama 50,tayi mata godiya tace sai taji daga gare ta.

Godiya ta sake yiwa doctor Nicho tace yanxu shi take jira taji daga gare sa su a shirye suke.

*************

BAHIYYA

A Yanzu kallo ɗaya zaka yimin ka fahimci cewa bana cikin hayyacina sakamakon gigicewa da ɗimautar da na shiga wurin neman kuɗin da za'a yiwa Mama aiki. Yanzu haka a kan magani take wanda a ƙalla anci kuɗi sunfi dubu dari uku. Malama Allah ne zai saka mata da mafifin alheri ita da mijinta domin kuwa sun dage wurin neman mana taimako wanda sun haɗa kuɗi yakai dubu ɗari bakwai, shima likitan namu doctor Samuel wanda ake kira doctor Sam ya taka rawar gani sosai wurin ganin cewa ya haɗa mu da ƙungiyoyi masu taimakawa marasa lafiya marasa ƙarfi, wanda a yanzu an haɗa mana kuɗi sunkai million ɗaya da rabi.
Nayi yawon nayi yawon har takalmin ƙafata sai da ya tsinke, yawo nake lungu lungu kwararo kwararo ina neman taimako amma ban iya haɗa ko dubu ɗari ba duk tsawon kwanakin nan, nayi ta gwada numbern Baba Maharazu amma shiru bata shiga tamkar malam yaci shirwa.
Har Gusau na shirya na tafi in da muka baro ko Allah zai sa a dace in samu Baba Maharazu da kuma mutanen unguwar mu ko zan samu wani taimako amma abin ba sauƙi saboda mutane rayuwar kowa ta kansa yake, haka dai suka yita yi muna addu'ar samun mafita ƙarshe sai maƙoncin mu ɗaya ne ya bani dubu ashirin yace dubu goma in yi na mota dubu goma kuma muƙara mu sayi magani.
Duniyar tayi min zafi, gabas da yamma kudu da arewa na duba na waiga na hanga amma babu wani sauƙi sai a wurin Rabbis-samawati.

Yau ma haka ne na gamo bilin bito na ban samu uwar komai ba sai tsabagen yunwar da ta addabi ciki na sai ƙugi yake, duk kuɗin mu sun ƙare komai yanzu sai a hankali ga asibitin kullum cikin bani bani.

Ɗakin na turo na shigo, a rakuɓe na hango Nuhaira gefe da alama bacci ɓarawo ne ya biyo ya saceta, domin ita na faɗa mata kada ta ɗaga ko ina, ko wane lokaci dole ta kasance tana kusa da Mama.

“BAHIYYA!”

Da gudu naje gare ta jin ta kira sunana, na fashe da kuka nace.

“Sannu Mama, in sha Allah zaki samu Lafiya ba jimawa..”

Girgiza kai tayi tare da sakin wani murmushin da yafi kuka ciwo tace.

“Bahiyya, abinda nike so in faɗa miki, ko da ta Allah ta kasance a gare ni, ki kula da ƙanwarki ku kuma tsare mutuncin ku duk wuya duk tsanani, sannan ku gwada tafiya tushen ku....”
Chapter 13 · 0% Book details