← Book details Asp Zarah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 21

Sashe 3

Asp Zarah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Nufar inda Nusaiba take ɗaure kusada Shahid yayi tare da tsugunawa a gabanta, hannu biyu yasa tare da jan gaban rigarta da ƙarfi hakan yayi sanadiyar yagewar rigar atamfar dake jikinta tun daga sama har ƙasa wanda ya bayyana ƙirjinta da kuma fatar cikinta.
Shahid wanda ya gane abinda yakeson aikatawa ga Nusaibar ne yasa ƙafafunshi biyu dake ɗaure ya naushi fuskarsa da ƙarfin gaske, take kuwa ya kuma da baya ya faɗi. Da sauri sauran yaran suka nufi kan Shahid saidai kafin su ƙarasa inda yake Ogan ya dakatar dasu, tashi yayi tare da isa gaban Shahid ɗin batare da yayi magana ba ya zaro wuƙa a gefen cinyarshi take ya caka mishi a ciki tare da zarewa ya ƙara caka mishi. Jini ne ya ɓalle tamkar a kwata take Shahid ya sulale babu rai a jiki.

Bakinsu na kulle duka amma hawayene ke bin fuskokinsu na bakin ciki.
Sunaji kuma suna gani ya ketama Nusaiba haddi amma babu abinda zasu iya domin sosai aka ɗauresu bazasu iya taɓuka komai ba.

Da sauri Rahma ta sake labulen jikinta na karkarwa ganin babu wanda ya ganta ne yasa tayi saurin komawa cikin banÉ—akin tare da kullewa.
Wayarta da bata rabo da ita na hannunta, sau da dama Mami kan hanata shiga da waya banÉ—aki amma takasa dainawa domin wasu lokutan babu abinda zatayi a banÉ—aki take shiga saboda kawai kar a sakata wani aikin tana tsaka da chat.

Tunawa da wayar da tayi yasa take tafara ƙoƙarin kiran Zarah domin a kawo musu taimako, kuka sosai takeyi amma na zuciya ganin kiran nata shiga ba'a ɗagawa.

A ɓangaren Zarah kuwa tun ƙarfe 12:30nr kwamishina ya mata kiran gaggawa domin su gana, fiye da awa ɗaya yanata yi mata surutan da basu shafi gefen da take aiki ba amma a matsayinshi na shugabanta ta kasa tanka mishi duk da tanason komawa gida su gaisa da kakanninta da ƴan uwanta da sukazo.
Wayoyinta gabaÉ—aya suna cikin mota hakan yasa batasan irin kiran da Rahma ke mata ba.

Sai da suka tabbatar da babu wani sauran mai rai a cikinsu kafin su bar gidan.

Ganin Zarah bata ɗaga kiran ne yasa Rahma danna kiran wani abokin Yayansu Mustapha dake aikin soja, bugu biyu ya ɗaga kiran yana mamakin kiranshi da tayi domin ya daɗe yana mata magiyar soyayyarshi amma tana wulaƙantashi.

Yana ƙoƙarin magana ta riga shi.

"Ka taimakeni Mustapha zasu kashemin iyayena dan Allah kazo da sauri". Ta faÉ—a da disasshiyar muryarta saboda kukan da takeyi.

Jin abinda ta faɗa ne yasa shi miƙewa daga zaunen da yake.

"Rahma su waye zasu kashe miki iyayen kuma a ina suke.?"

"Suna cikin gidanmu yanzu haka sun ɗaure kowa da kowa nima basu ganni bane, dan Allah kazo da sau..... " kuka ne yaci ƙarfinta batare da ta ƙarasa maganarta ba.

"Subhanallahi! Ki zauna a inda kike gamu nan zuwa."..

Bata iya amsawa saboda toshe bakinta da tayi tana kuka.

Cikin mintuna goma sha biyar taji jiniyar sojoji wanda hakan ya tabbatar mata da Mustapha ya iso da jami'ansu na soji.

A farfajiyar gidan kuwa mai gadi ne da sauran ma'aikata biyar dake musu aiki kwance basu motsi, tun daga hakan Mustapha ya gane tabbas babu lafiya hakan yasa suka tunkari ƙofar babban falon cikin shiri da ƙwarewar aiki.

Jini suka fara arba dashi bayan buɗe ƙofar har zuwa cikin falon, da basu kasance sojoji ba toh tabbas sai wasu daga cikinsu sun firgice da ganin gawarwakin mutanen dake kwance domin kuwa kisa aka musu tamkar a kwata.
Lungu da saƙo na gidan gabaɗaya sun duba amma babu kowa hakan ya tabbatar musu cewa masu laifin sun samu nasarar tserewa.
Duk da haka sai suka raba kawunan su a ɓangarorin gidan ciki da waje.

Ƙarfin hali kawai Mustapha yake yana maida hawayen dake son zubo mishi, lambar Zarah ya shiga kira saidai ba'a ɗagawa. Ganin haka ya canja akalar kiran ga wani maƙocin shi D.P.O yayi mai bayani tunda case ɗin ba wanda sojoji zasu shiga bane, taƙaitaccen bayani kawai ya iya yimishi ya kashe wayar.

Cikin mintunan da basu wuce talatin ba Æ´an Sanda da sojoji suka kewaye gidan ta kowanni fanni.

Hayaniyar mutane da taji sosai ne yasata jarumtar buɗe ƙofar banɗakin, saida ta fara leƙowa taga taron masu kaki ne sannan ta fito gabaɗaya.
Abinda ta gani ne yasata sakin ihu tare da faɗowa ƙasa sumammiya.

Sai a lokacin mutanen dake falon suka ankara da ita, shikuwa Mustapha sai a lokacin ya tuna da ita tun bayan da yayi arba da mummunar ɓarnar da akayi musu.

"Ya kamata a sanar da wani a cikin danginsu domin bazamu iya yin wani abu da gawarwakin batare da izinin su ba." cewar D. P. O. dake kusada Inda Rahma ke kwance.

Waya Mustapha ya ciro tare da danna lambar Alhaji Sulaiman sannan ya miƙama D.P.O wayar domin baisan ta ina zai fara faɗin wannan baƙin labarin ba.
Fita yayi bayan ya karɓi wayar bai jima sosai ba ya dawo sannan ya miƙawa Mustapha wayar.

Ƙarfe huɗu daidai motocin Alhaji Sulaiman da tawagar shi suka iso, motar farko mutane biyar ne a ciki. Direba dake jan motar sai Alhaji Sulaiman dake gefenshi a baya koma Baaba Faɗimatu, Ammi da Momi.
Sauran motoci biyun koma abokan kasuwancinshi ne a ciki daya sanar musu da rasuwar suka biyoshi domin yin jana'iza.

Ganin Ƴan sanda da sojoji yasa kansu ɗaurewa domin dai Alhaji Sulaiman ɗin bai sanar dasu abinda ke faruwa ba umarni kawai yabada su shirya suzo garin Bauchi.

Momi ce tayi ƙarfin halin magana lokacin da direba yayi parking.

Tace" Daddyn su meke faruwa ne haka, meya kawo jami'an tsaro haka a gidan. Kodai Zarah ta karɓi masu tsaron da aka bata ne.?"

"Tambayoyin sunyi min yawa ku sauka mu shiga ciki, tada Baaba daga baccin nan haka tunda mun iso." Ya faÉ—a gamida ficewa a cikin motar

Ammi kuwa ta kasa tankawa domin zuciya da gangar jikinta sun tabbatar mata babu lafiya.

"Meke faruwa ne naga Æ´an'uwansu Zara'u sun cika gidan.?" FaÉ—in Baaba FaÉ—imatu da farkawarta kenan daga baccin data fara tun a hanya.

"Mu shiga daga ciki dai Baaba sai muji abinda ke faruwa domin dai waƴannan jami'an tsaro akwai abinda ya kawosu ko kuma suke tsaro." Momi tafaɗa tana mai buɗe ma Baba ƙofar.

Cikin rashin kuzari Ammi ta fito tabi bayansu suka nufi hanyar shiga cikin gidan.

Sam Alhaji Sulaiman baiyi tunanin irin ɓarnar dazai tarar ba kenan domin D.P.O ɗin ce mishi kawai yayi ƴan fashi sun shiga gidan ɗan'uwan shi sunyi fashi haɗe da kisa.
Kuka yake bil hakki ganin irin kisan wulaƙanci da akayi musu duk da kasancewar ƴan Sanda sun gyarasu daga asalin yadda suka samesu bayan likita ya tabbatar babu wani mai sauran numfashi a cikin su. Saidai tambarin *Alpha*🌴 da aka zana da jini na nan a tsakiyar falon.

Da sauri ya miƙe da nufin tsayar dasu daga shigowa falon kasancewar su mata yasan dole basu da juriyar da zasu iya ganin wannan aika aikar, hatta shi dayake namiji yanajin tamkar ya ciro zuciyarshi ya aje a ƙasa saboda tarin baƙin cikin daya shige shi a lokaci ɗaya.

Saidai kash!!! Kafin yakai ga ƙarasawa ƙofar fita daga falon Momi da Baba Faɗimatu sun sako kai bakinsu ɗauke da sallama, duk da haka saida ya ƙarasa inda suke cikin sassarfa ya kare fuskokinsu daga ganin cikin falon.

"Baaba da kun É—an tsaya a waje ana gudanar da bincikene anan."

"Sulaimanu wani irin bincikene akeyi haka daya saka zubar da hawaye, ka matsa ka bamu guri mu ƙarasa muga abinda ake ɓoye mana. Shin ina ahalin gidan ne.?" Faɗin Baaba kenan tana mai kaucewa daga hanyar daya tare.
Bayanta Su Ammi su bi domin ƙarasawa falon.

Abinda ya guda shiya faru domin a tare gabaɗaya su ukun suka zube a ƙasa sumammu, shima dai hawayen ne yake zubo mishi.

Wani daga cikin mutanen falon ne yayi dabarar watsa musu ruwa saidai Momi ce kawai ta farfaÉ—o itama ba'a cikin hayyacinta ba.

"Dan Allah ku tayar dani daga wannan mummunan mafarkin ba gaskiya ban.." bata ƙarasa ba ta ƙara sulale wa.

"Yallaɓai kasa hannu anan munason mu wuce da gawarwakin asibitine domin gudanar da bincike." cewar likitan da aka damƙa case ɗin binciken gawarwakin a hannunshi yana miƙawa Alhaji Sulaiman wasu takardu.

"Babu wani binciken da za'a gudanar saboda a yau É—innan nakeson a sadasu da gidansu na gaskiya, ku taimakawa waÉ—annan dake sume kawai." YafaÉ—a cike da rauni.

Nan ya ciro waya ya fara bugawa ƴan uwa da abokan arziki, abu da zamani nan da nan anguwar ta cika maƙil da jama'a domin sallartar mamatan.
Da taimakon likitoci aka samu damar kimtsa su a cikin likkafani Saidai kafin wani lokaci gabaÉ—aya sun rine daga kalar fari zuwa Ja saboda jinin dake zuba da jikin gawarwakin.
Sau uku ana canjawa amma babu wani sauyi hakan yasa aka barsu a haka.

Acan falon baƙi kuwa Limamin masallacin Juma'a na gwallaga ne tare da su Momi da aka samu suka farfaɗo dakyar, saidai har zuwa wannan lokacin Rahma bata farka ba hakan yasa aka wuce da ita asibiti.

Nasiha ya musu mai ratsa jiki hakan yasa suka sassauta da koke koken da sukeyi, nan suka miƙe suka nufi falon inda baƙi suka fara cika. Nan aka fara gaisuwa da jajantawa.

Kwamishina ne ya kalli Zarah dake zaune a kujerar dake fuskantar shi yace

"Zarah ta wace hanya kike ganin zamu iya magance matsalar tsaro a ƙasar nan.?"

Zuwa yanzu Zarah ta fara zargin akwai wani abu a ƙasa domin duk lokacin da tayi nufin tafiya sai shugaban nata ya tsayar da ita ta hanyar yi mata wasu maganganun da ba ita ya dace a faɗawa, cike da ƙosawa tace " Yallaɓai a tunani na wannan matsala ce da zamu taro mu samu mafitar ta, matsala ce data shafi jaharmu da ƙasa baki ɗaya don haka muna buƙatar mu tattauna da sauran manyan jami'ai domin samun mafita.?"

Kafin ya samu damar amsa mata wayarsa dake gefe tayi ƙara, hannu yasa ya ɗauku wayar tare da karawa a kunnenshi batare da yayi magana ba.
Chapter 3 · 0% Book details