← Book details Asp Zarah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 21

Sashe 14

Asp Zarah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A daidai wannan lokacin kuma M. J da Abdallah suka shigo garin Bauchi sannan kai tsaye suka nufi hotel ɗin domin kama masauki, Abdallah ne ya fita a motar domin zuwa kama musu ɗaki, bai ɗauki lokaci ba ya dawo imda aka basu room 233 buɗe ƙofar yayi tare da faɗin.
"Mr. President sai ka fito mu shiga."
Fitowa yayi suka nufi cikin hotel É—in, a wannan lokacin ma Zarah da Alhaji Mati sun fito a motarsa suma da nufin zuwa É—akin da aka kama mishi.
Abdallah da M. J ne a gaba yayinda suku ma suke baya a lokacin da suke haura matattakalar dazata sada su da inda jerin É—akunan suke.
Tamkar ance ya waiga..........

_Insha Allah daga next page bazan ƙara free page ba, nagode sosai da ƙaunar da kuka nunawa littafina. ASP ZARAH VIP GROUP, ASP ZARAH FANS 1 DA ASP ZARAH FANS TWO INAYINKU SOSAI DA SOSAI NAGODE MATUƘA._

_BY_
_JASMINE._🌸🌸
*ASP ZARAH*👩‍✈️

_Domin samun damar cigaba da karantawa batare da ɗaukarwa kai alhaki ba biya N300 kacal ko kuma N500 na VIP, tuntuɓi 07048961623._

*🌍MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION*📚🖊️
*M*. *W*. *A*

__Kallo ɗaya yayimata ya gane ta saboda yawan ganinta da yake yi a cikin mafarkinshi tun bayan haɗuwarsu da ita a Abuja, take yaji wutar tsanarta ta ƙara ruruwa a zuciyarshi, tsaki yaja mara sauti bayan ganin irin kallon da Alhaji Mati yake yiwa Zarah na tsantsar maitar buƙata, tamkar zuciyarsa zata fito waje haka yake ji lokacin dayaga sun shige ɗakin bayan an buɗe mata ƙofar. Kwafa yayi shima yabi bayan Abdallah suka shige nasu ɗakin.

"Duk sanda nayi magana sai ka dinga ƙaryatani bayan sai na tabbar nake faɗa, gashi yau dai ka tabbatarwa idanunka." cewar M.J

Kallonshi Abdallah yayi cikin rashin fahimta yace.
"Kai da waye kake magana haka."
"Ina tare da wani bayan kai ne anan.?" cike da jin haushin tambayar ya amsamai.
"Sorry ranka ya daÉ—e bangane akan me kake magana ba."
"Kwanakin baya ba tare da kai mukayi maganar wata Æ´ar sanda a Abuja."
"Oh wannan yarinyar da har yau nake fatan sake ganinta , gaskiya duk da bansanta sosai ba ta burgeni matuƙa."
"Mtswww" M.J yaja tsaki tare da kuma faÉ—in
"Sai kayi kuma ai, itace wacce muka hauro tare suka shiga next room É—in nan."
Miƙewa Abdallah yayi daga kwancen da yake tare da cewa.
"M. J banason wasa fa wai da gaske kake police É—in nan ce muka hauro tare dasu."
"Dama ina wasa da irin wannan maganar ne."
"Allah ya kyauta" shine kawai abinda Abdallah ya faɗa tare da miƙewa ya shige toilet, bai jima ba ya fito bayan yayi wanka. Shima M.J toilet ɗin ya shiga yayi wanka ya fito, basu wani jima ba suka fita domin isa inda zasuje.

A ɓangaren Zarah kuwa bayan shigarsu ɗakin, hannunta Alhaji Mati ya riƙo da nufin janyota jikinsa ya rungumeta saidai kafin yayi hakan cikin dabara ta zame hannayenta tare da zama a gefen gadon tana faɗin.
"Alhaji bazaka watsa ruwa ba tukun, kayi dogowar tafiya kayi wanka zaka fi jindaÉ—in aiwatar da komai cikin nutsuwa."

"Tabbas wannan shawarace mai kyau, bari nayi wankan na fito, ko zaki taimakamin ne." ya ƙarasa faɗa yana mai kashe mata ido.

"A'a shiga kafito dai, yanzu nayi wankan kafin na fito."

Bai ce komai ba ya cire babbar rigarsa tare da shigewa banɗakin, ganin shigarsa yasa tayi saurin nufar inda akwatin kayansa yake, bata wani sha wuyar buɗewa ba saboda ta rigada tasan komai, kamar yadda suke zargi, kaya ne sosai a saman jakar saidai acan ƙasa rafar kuɗi ne sosai sai hodar ibilis.
"Zaku iya shigowa Bala zarginmu ya tabbata ku shigo cikin shiri." ta faÉ—a a hankali.
A buɗe ƙofar take dan haka jami'an suka shigo tare da yiwa ɗakin ƙawanya cikin shirin ko ta kwana.
Zigir! haihuwar mahaifiya , haka ya fito daga banÉ—akin yana faÉ—in.
"Gaskiya baby ina...." maganarshi ce ta katse take tashin hankali yayiwa fuskarshi tambari, juyawa yayi da nufin komawa cikin banɗakin saidai hakan bai yiwu ba sakamakon damƙarshi da wani jami'i yayi, zagaye shi sukayi sa'an nan wani a cikinsu ya taimakamai da kayansa, shidai ya kasa cewa komai illa rawar ɗari da yakeyi, ankwa aka ɗaura mishi hannu tare da tisa ƙeyarsa aka wuce dashi batare da an bashi damar magana ba duk da irin kallon da yakewa Zarah na zargi tare dason yi mata maganan.
Bincike suka cigaba da gudanarwa tarw da sauran jami'ai biyu dake tare da ita, sun jima kafin suka tattara zuwa ofishin nasu.

Sai da Abdallah ya tirsasa M.J kafin ya yadda suka tsaya a wani mall suka yiwa Zarah siyayyar abubuwan da sukasan mace zata buƙata musamman mai shirin yin aure.
Cike da murna Baaba ta tarbesu bayan isarsu gidan, nan suka gaisa tare da hirar yaushe gamu wanda yawanci tsokanace kawai take yimusu, sun daɗe suna hira kafin daga bisani Abdallah yayi ƙarfin halin tambayar Zarah ganin har zuwa wannan lokacin batazo ba sai Raliya dake ta hidima dasu.

"Zara'u dai sai shiriyar ubangiji, saida nace karta fita aikin nan yau saboda zuwanku amma tayi biris dani wai akan idan kunzo akirata aiki zatayi mai mahimmanci a can ofishin nasu." cewar Baaba cikin kwafa.

"Allah sarki dama tana aiki ne.?" Abdallah ya kuma tambaya.

"Ehh tana aiki kuma itama shugaba ce a wajen, ko bataje ba bazata samu matsala ba amma dan naci saida ta tafi, bari na kirata ta dawo yanzu ungo dubamin numbarta anan zakaga ansaka Zara'u." takarasa faɗa tana miƙa mishi ƙaramar wayarta.
Shidai M. J yanajinsu amma bai tanka ba, saidai ranshi yayi mugun ɓaci da lamarin wannan yarinyar da akeson ya aura, wato an faɗa mata zaizo shine ta saka ƙafa ta fita.

Kiran wayar ake tayi amma bata ɗagawa, hakan yasa M.J ya umurci su kuma falon Abba su zauna, nan suka bar Baaba tana ta mitar Zarah taƙi ɗaga mata waya da gangan saboda bata da gaskiya.

🥶🥶🥶🥶🥶🥶🥶🥶

A hankali ta kulle ƙofar tare da murɗa key ɗin jiki kana ta isa kan gadonta ta zauna tare da fiddo da wata ƙaramar waya da ke ta kawo wuta alamun ana kiranta, karawa tayi a kunne tare da faɗin
"Barka da safiya ranka ya daÉ—e."

"Baki da hankali ne Raliya, shin ban tsara miki yadda nakeson ki gabatar da komai ba, wato saboda kinga bakya kusa dani kike tunanin zakiyi abinda kikaga dama ko? Toh wallahi duk wani motsinki kinsan a tafin hannuna yake, saboda bakisan mahimmancin abinda ya kaiki ba har zakiyi saken da za'a cire camera daga inda kika aji. Mtssww! Baki san darajar wannan abun da muke nema koh, wallahi ki kiyayeni Raliya kiyi abinda nagaya miki cikin tsari, yanzu tayaya zamu samu masaniyar inda abun yake bayan ancire cameras ɗin, kiyi gaggawar nemowa kanki mafita tun kafin raina ya kai ga ɓaci, Nonesense!." Batare da jiran abinda zatace ba ya kashe wayar.

Kuka mai ciwo ne ya kwace mata, kifa kanta tayi akan pillow tare da fara rera kukan cike da takaicin maganganun mutumin da take matuƙar so da ƙauna a gareta, a gefe guda kuma takaicin cire cameras ɗin ne ya dameta wanda ta tabbar wannan aikin Zarah, ta rasa gane alƙiblarta, tamkar mai aljanun da suke faɗa mata sirrin mutum haka take, a ɗan zaman da sukayi ne ta fahimci haka. Tabbas a da taso ta rangwanta mata kodan albarkacin Baaba, amma a yanzu batajin ko iyayenta dake kabari ne zasu dawo rayuwa suce ta haƙura da satar Diamond ɗin nan ba zataji maganarsu, dole ta sake shiri domin tasan ta wannan hanyar ne kaɗai zata iya cimma burinta na rayuwa da Alpha a matsayin masoyi.
Miƙewa tayi tare da share hawayen da ya ɓata mata fuska ta nufi ƙofar fita daga ɗakin saboda jin kiranta da Baaba keyi.

"Gani Baaba". Ta faÉ—a bayan ta iso falon.

"Yauwa Raliya kiramin direba na aikashi ya tahomin da Zara'u tunda naga batada da niyar dawowa."

"A'a Baaba kinsan yanayin aikinsu fa, ki barta zata dawo yanzu idan yaje ma ba lallai su barshi ya ganta ba."

"Shikenan amma tabbas zata gamu da fushina idan ta dawo, yanzu da ba Æ´an gida bane ai kunyata mu zatayi kenan."

"Ayi haƙuri Baaba, kina buƙatar wani abu ne." Raliyan ta faɗa tana mai sunkuyar dakai ƙasa.

"A'a bakomai jeki kema ki huta kinyi aiki sosai."

"Nagode" ta faÉ—a tare da nufar É—akinta.

✈️✈️✈️✈️✈️✈️✈️✈️✈️✈️✈️
*SINGAPORE*

Daddy ne zaune da wani kyakkyawan matashin saurayi a wanj keɓaɓɓen lambu mai cike da shukoki kaloli daban-daban, kallo ɗaya zaka yiwa saurayin kaga tsantsar kama da sukeyi da Zarah da kuma Rahama saidai ƙarin hasken fata da Zarah tafiso duka, hannun Daddyn na akan kafaɗar saurayin da idanuwanshi sukayi jazir saboda kukan daya sha, hankacif ya saka tare da ƙara goge mishi idanunshi yana faɗin.
"Kayi haƙuri Son muma har yanzu haka mukeji a zuƙatan mu bayyanawa ne kawai bama yi, amma kayi hakuri ka biyoni mu koma gida." cewar Daddy

"Daddy bazan iya zama a Nigeria ba alhalin babu waÉ—anda zan iya gani na samu farin ciki."

"Kada kace haka As-Siddiq zaman ka anan bashine zai iya dawo da waɗanda suka rasu ba, idan kace baka da kowa toh mufa ko baka ɗaukemu a matsayin iyaye bane dama, ƴan uwanka mata fa, bawai ina nufin bazan iya riƙesu bane tamkar ƴaƴan da na haifa amma suna buƙatarka a kusa dasu a matsayinka na wanda zasu dinga gani tamkar ɗan'uwana da ya rasu, kaine kaɗai zaka iya rarrashinsu musamman Zarah da ita bata kukan fili saina zuciya wanda yafi ƙuna, kayi haƙuri ka shirya mukoma gida tare dan Allah ina neman wannan alfarmar."

"Daddy kai ubane a wajena baka da buƙatar neman alfarma a wajena, umarni kawai zaka bani na aiwatar, insha Allahu zuwa ƙarshen shekara zan tattaro na dawo gida."

"Me zaka tsayayi anan har ƙarshen shekara? Bayan haka ma bikin ƴan uwanka za'ayi nan da wata ɗaya da sati biyu ka shirya kawai mu tafi tare."

Idanunshi da suka fara washewa ya waro wanda hakan yayi mishi kyau matuƙa, kafin yace.
"Wasu Æ´an uwan nawa kuma Daddy."

"Ehh Æ´an uwanka Zarah da Jawwad, insha Allah nan da wani lokaci za'a É—aura aurensu."
Chapter 14 · 0% Book details