Sashe 8
Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Kamar kullum washegari suka yi wanka suka shisshirya. Mummy Zulaiha ta zo har dakinsu ta yi kiran Aalimah. Tare suka fita ta nuna mata duk yadda ake amfani da injinan cleaning din gidan, da yadda ake tsaftace shi. Sannan ta tambaye ta ko ta iya girki? Ta ce ba abin da ba ta iya girkawa ba. Sai ta ce, har English meals? Ta ce, ta iya wasu a wurin Mamanta. Sai ta ce, to shi kenan daga yau ita za ta dinga girki da cleaning, mai aikinta ta yi tafiya. Tana kuma son kullum ta gama abincin dare kafin dawowar Daddy. Tana kuma son wannan zancen ya tsaya a tsakaninsu. Incase su Basma za su tambaye ta wani abu a kan hakan, ta ce, ita ta sa kanta.
Aalimah ta yi motsi da bakinta tana so ta tambaye ta makarantarta kuma fa? Amma ganin ba fuska dole ta hadiye. Tun a lokacin ta fara girkin rana bayan MummyZulaiha din ta nuna mata yadda ake amfani da komai.
Ta yi cleaning, ta yi girkin rana, ta yi na dare. Ko na minti biyu ba ta huta ba. Da suka tambaye ta ko me ta ke yi haka tun safe? Ta gaya musu yadda uwarsu ta gaya mata. Ta kara da cewa, Easther ta yi tafiya shi ya sa ta ke taimaka wa Mummyn. Allah ya so tun farko Mamansu ta hore su da komai, ba ta da son jiki ko kankani.
Ranar litinin, wato washegarin ranar,Mummy Zulaiha ta kwashe ‘ya’yanta ta kai makaranta, ta bar Aalimah a kitchen. Mamaki ya kama su har hada baki suke wajen tambayarta,
“Aal, will not go to school Mum?â€
Ta lailayo ashariyar da ba su san ta iya ba ta antaya musu, ta kuma ce duk wanda ya kara yi mata zancen wata “Aal†ubansa za ta ci ciki da waje. Ta cire ta daga makarantar don ubansu, su je su gaya wa ubansu su ga yadda za ta ci mutuncinsu. Duk suka yi lakwas. Zaginta da balbalin bala’inta ya fi karfi a kan Basma, ta ce ta san ta fi kowa firirita a kan wata Aal, to in ta isa ta je ta gaya wa ubanta RAAZEE ISHAQ ta cire Aalimah daga makaranta.
Hatta abokan karatun Basma sun fahimci yau ba ta cikin walwala. Wadanda suka damu har tambayarta suke yi, me ke damunta? A gajarce ta ke cewa, “Headacheâ€.
Da yamma motar makaranta ta bi ta koma gida, Mummy ta ce su Khaleesat kawai za ta dinga maidawa gida, she’s old enough ta kula da kanta (Basman).
Ko da suka dawo a kitchen suka tadda Aalimah ko wanka ba ta samu ta yi ba saboda aiki. Har wanki Mummy ta jibga mata don ma dai da inji ne. A ranta ta ce, in kin ji wuya za ki koma inda ki ka fito.
Idanu narai-narai da hawaye Basma da ke tsaye a bakin kofa ta ke kallon Aalimah, wadda duk ta yi gumi ta yi maiko, ta takarkare sai kankarar tukunya ta ke da cokali tana ci, abinci cokali daya wannan Mummy ba ta bata ba, duk da ita ta yi girkin. Tazo ta kwashe shi tsaf ta kai ‘dining’ kuma ta kasa-ta-tsare a falon tana ta ayyukan ta cikin system dinta, bata bari Aalimah ta ganta ba ta bar wurin da sauri ta yi sama da gudu, ta fada gadonta tana hawaye. Me za ta iya a kai banda fada wa Daddy? Babu!
Haka suka wuni dukkansu sukuku da su cikin damuwa da mamakin Mummy. Su dai sun san ko a cikin iyaye tasu uwar is exceptional wajen kyautata wa ‘ya’yanta. Yaushe ta canzazuwa maketaciya?
Rayuwar da suka yi ta yi kenan har tsayin wata guda, sai Daddy zai dawo ta ke cewa ta je ta yi wanka, sai za a zauna cin abincin dare za ta samu ta ci. Amma ba ta da breakfast ba ta da lunch. Sai karshen mako kuma, shi ma don Daddy na gida tana da freedom duk da haka komai ita ta ke yi, bai taba lura ba. Yanayin abincin gidan ne kawai ya lura ya canza, kuma ya fi jin dadinshi a kan na baya. Kuma da yake Allah ya yi shi mutum mara sa ido ko bin kwakkwafi, bai taba tankawa ba. Sakin ciki yake ya ci iyakar cinsa.
Karatu fal! Ya yi wa Aalimah fintinkau, ya wuce ta, an bada assingments har ba adadi ba ta yi ko daya ba. Absentness dinta da ya yi yawa shi ya sa coordinator dinsu da wasu daga cikin course tutors suka ankara. Makarantar ta yi tracingguardian phone number dinta a file dinta suka yi mishi phone call officially.
Aalimah ta yi motsi da bakinta tana so ta tambaye ta makarantarta kuma fa? Amma ganin ba fuska dole ta hadiye. Tun a lokacin ta fara girkin rana bayan MummyZulaiha din ta nuna mata yadda ake amfani da komai.
Ta yi cleaning, ta yi girkin rana, ta yi na dare. Ko na minti biyu ba ta huta ba. Da suka tambaye ta ko me ta ke yi haka tun safe? Ta gaya musu yadda uwarsu ta gaya mata. Ta kara da cewa, Easther ta yi tafiya shi ya sa ta ke taimaka wa Mummyn. Allah ya so tun farko Mamansu ta hore su da komai, ba ta da son jiki ko kankani.
Ranar litinin, wato washegarin ranar,Mummy Zulaiha ta kwashe ‘ya’yanta ta kai makaranta, ta bar Aalimah a kitchen. Mamaki ya kama su har hada baki suke wajen tambayarta,
“Aal, will not go to school Mum?â€
Ta lailayo ashariyar da ba su san ta iya ba ta antaya musu, ta kuma ce duk wanda ya kara yi mata zancen wata “Aal†ubansa za ta ci ciki da waje. Ta cire ta daga makarantar don ubansu, su je su gaya wa ubansu su ga yadda za ta ci mutuncinsu. Duk suka yi lakwas. Zaginta da balbalin bala’inta ya fi karfi a kan Basma, ta ce ta san ta fi kowa firirita a kan wata Aal, to in ta isa ta je ta gaya wa ubanta RAAZEE ISHAQ ta cire Aalimah daga makaranta.
Hatta abokan karatun Basma sun fahimci yau ba ta cikin walwala. Wadanda suka damu har tambayarta suke yi, me ke damunta? A gajarce ta ke cewa, “Headacheâ€.
Da yamma motar makaranta ta bi ta koma gida, Mummy ta ce su Khaleesat kawai za ta dinga maidawa gida, she’s old enough ta kula da kanta (Basman).
Ko da suka dawo a kitchen suka tadda Aalimah ko wanka ba ta samu ta yi ba saboda aiki. Har wanki Mummy ta jibga mata don ma dai da inji ne. A ranta ta ce, in kin ji wuya za ki koma inda ki ka fito.
Idanu narai-narai da hawaye Basma da ke tsaye a bakin kofa ta ke kallon Aalimah, wadda duk ta yi gumi ta yi maiko, ta takarkare sai kankarar tukunya ta ke da cokali tana ci, abinci cokali daya wannan Mummy ba ta bata ba, duk da ita ta yi girkin. Tazo ta kwashe shi tsaf ta kai ‘dining’ kuma ta kasa-ta-tsare a falon tana ta ayyukan ta cikin system dinta, bata bari Aalimah ta ganta ba ta bar wurin da sauri ta yi sama da gudu, ta fada gadonta tana hawaye. Me za ta iya a kai banda fada wa Daddy? Babu!
Haka suka wuni dukkansu sukuku da su cikin damuwa da mamakin Mummy. Su dai sun san ko a cikin iyaye tasu uwar is exceptional wajen kyautata wa ‘ya’yanta. Yaushe ta canzazuwa maketaciya?
Rayuwar da suka yi ta yi kenan har tsayin wata guda, sai Daddy zai dawo ta ke cewa ta je ta yi wanka, sai za a zauna cin abincin dare za ta samu ta ci. Amma ba ta da breakfast ba ta da lunch. Sai karshen mako kuma, shi ma don Daddy na gida tana da freedom duk da haka komai ita ta ke yi, bai taba lura ba. Yanayin abincin gidan ne kawai ya lura ya canza, kuma ya fi jin dadinshi a kan na baya. Kuma da yake Allah ya yi shi mutum mara sa ido ko bin kwakkwafi, bai taba tankawa ba. Sakin ciki yake ya ci iyakar cinsa.
Karatu fal! Ya yi wa Aalimah fintinkau, ya wuce ta, an bada assingments har ba adadi ba ta yi ko daya ba. Absentness dinta da ya yi yawa shi ya sa coordinator dinsu da wasu daga cikin course tutors suka ankara. Makarantar ta yi tracingguardian phone number dinta a file dinta suka yi mishi phone call officially.