← Book details Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 91

Sashe 63

Aalimah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Mummy ta ce, “Taya ni gani dai Gumsun Babansu. Sun bi sun daga min hankali. To wallahi ba zai yiwu ba, ba za ku kara min hawan jini da tashin hankali kan wanda nake fama da shi ba.
Ka yi muku booking ku tafi, in ji da majinyatan da ke gadon asibitiâ€.
Khaleesat da Hamoud suka hau hararar juna, tareda janyewa daga jikin Mummy a lokaci guda, kowanne kamar ya rufe dan uwansa da duka haka yake ji. Gumsu ta yi dariya tace,
“Karshen munafurci yau ina ganinsa a gidan nan. Don Allah ku soke juna da mashi sannan zan yarda kun daina son junaâ€.
Babu wanda ya kula ta a cikin su.
Hamoud ya tashi ya bar wajen, ita ma Khaleesat haka, amma yana shiga daki ya zauna a bakin gadonsa sai ya samu kansa da sakin murmushi, wani irin lallausar murmushi wanda rabon sa da yin irinsa har ya manta. Zai iya cewa tun faruwar al’amarinnan ga ahalinsa rabon da murmushi ya ziyarci fatar bakin sa. Kalaman Khaleesat da yanayin innocent fuskarta a sanda take fadar su yake tunawa daya bayan daya suna ta sanya shi murmushi. At last she’s mine. Ya fada a hankali, ya mallake ta ta zama tasa da dadi ba dadi. Sai kawai ya hau duba travel routine na kasar Japan kamar wanda ake yiwa umarni. Koda yake umarnin ne Mummy ta yi masa amma mai kama da taimako a gare shi. Ita kuma Khaleesat tana shiga daki kayanta ta soma hadawa. Tana yi tana waiwayen kofa kada Mummy ko Gumsu su shigo su ga abinda ta ke yi.

Alhamdulillah a washegari Daddy 1 da Daddy 2 suka soma taka kafafunsu akan kasa. Da taimakon likitoci da malaman jinya, Aboubacar yana iya zama da kansa, ya samu lahani ne mai matukar hatsari, karfe ne da gilashi suka shige cikin cikinsa, kusan aikin da aka yi masa ya fi na su Daddy cin kudi, su sun taka kasa, shi kuma ya zauna da taimakon (pillow).
Suka yi hira da Hamoud sosai a wannan ranar inda ya gaya masa jibi zai koma bakin aikinsa, amma kafin nan yana matuqar son a barshi ya ga Mu’azzam. Aboubacar ya ce “idan Nebrass ya zo ka roke shi na ga alama yana da kirki. A hannunsu Mu’azzam yake a private clinic dinsaâ€.
Da shawarar Aboubacar Hamoud ya yi aiki. Washegari da Dr. Nebrass ya zo har kasa ya durkusa yana rokonshi ya bar shi ya ga Mu’azzam, shi yana yi Aboubacar na yi har da hawayen su, ya rasa yadda zai yi da su, shi da ma Daddy Ishaq bai sa aka ba. Ba su san Mu’azzam ba ne, yanzu haka ya dade da samun sauki, ba ya son ganin kowa ne. He prefers to be alone a irin wannan yanayin. Nebrass ya ce su yi masa alfarma ya fara neman izinin Mu’az din tukunna, kada su mayar masa da aiki baya.

Aboubacar ya ce,
“Ka gaya masa karfe da gilashi sun huda min hanta, ya bar ni in ganshi kafin in cikaâ€.
Hamoud kuma ya ce,
“Ka gaya masa gobe zan koma Japan, kuma sai na yi shekaru uku ban zo gida ba, zan tafi tare da kanwarsa, muna neman albarkarsaâ€.
Dr. Mansour ya ce, “Kada ka gaya masa na rasa kafa, amma ka ce masa I want to shed my tears before him, sannan ne zan daina jin rashin Aboulkhair da na yi. Sai na ganshi zuciyata za ta rage ciwo!â€

Dr. Nebrass ya ce, sakonnin sun masa yawa, ba zai iya rikewa ba, kowa ya rubuta nasa a takarda. Duk haka suka rubuta jiki na rawa suka ba shi. Ya dubi Daddy 1 (Ishaq) yana murmushi ya ce,
“Kai ba ka da sako?â€
Murmushi ya yi mai fadi (broad smile) ya ce a gajarce,

“Babu!â€.

Wanan kauna ta zahiri da badini da dan uwansa da ‘ya’yan ‘yan uwansa suka gwada wa Mu’azzam a kan idonsa, ta wadatar da shi da zuciyarsa, ya fahimci Mu’azzam din mutum ne abin so, mai matukar kima da daraja a gare su!!!.
****

Lokacin da Dr. Nebrass ya kai wa Engnr. Mu’azzam Ishaq Raazee sakon ‘yan uwansa da Baffansa, yana zaune gefen gadonsa na asibiti yana shan hot coffee. Coffee ne mai zafi da kauri wanda yayi daidai da yanayin da ake ciki na tsananin sanyi a birnin LasVegas a yammacin ranar wata Asabar. Yana sanye da thick coat ruwan toka a sama da karamar riga short-sleeved daga ciki da dogon bakin wando (Armani code). Suma ta taru a kansa sosai tasu ta buzayen usli duk da kasancewarsa ba ma’abocin tara ta ba. Amman zaman asibiti yasa yanzu ta taru sosai ta mummurde ta zama wani irin curl.
Takardun ya bi daya bayan daya cikin nutsuwa yana karantawa, Dr. Nebrass na tsaye a kansa yana son ganin reaction dinsa. A matsayinsa na likitansa komai na Mu’azzam din sai ya rubuta musamman ci gaba irin wannan ga lafiyarsa. Ana so Mu’az din ya dinga socializing da mutane na jikin sa musamman masoyansa irin haka, zasu taimaka kwarai wajen restoring farin-cikin da ya rasa.

Gani ya yi Mu’azzam ya yi dan murmushi abin da tun zuwansa gadon asibitin bai yi ba. Ya daga kai yana kallon likitan, murya a sanyaye cakude da damuwa ya ce,
“Haka Aboubacar ya ji ciwo???â€

Nebrass ya ce,

“Duk ya fi su jin mummunan rauniâ€.

Har zai gaya masa Dr. Mansour babu kafa, ya tuna ya ce kada ya gaya masa. Cikin lallashi da siyasa ya ce,
“In zuciyarka ba ta amince wa ganinsu ba zan ba su hakuri. Amma hakika sun damu sosai da son ganinka, musamman mai rauni a cikin, har hawaye yake min. Shikuma dayan dana ji sun kira, Hamoud, daga yanayin sa zai iya bada komai da ya mallaka don ya samu ganin ka ko sau daya ne kafin ya wuceâ€.
Mu’azzam ya runtse idonsa, da sauri kuma ya bude su akan likitan ya ce,

“Let them in, please…â€.

Dr. Nebrass ya bude kofar, Hamoud ya turo Aboubacar a hankali kan kujerar marasa lafiya na musamman, wadda ke hade da na’urori a jikinta, Mummy ta turo Mansour Raazee kan kujerar guragu, Mu’azzam sai ya saki kofin coffee da ke hannunsa ya zube a kasa, kofin ya fashe, ya sanya fuska a tsakanin cinyoyinsa ya sanya kuka mai tsuma rai.
“Wace irin kaddara ce ta fado wa rayuwarmu haka?â€

Gumsu ce ta karshen shigowa, ta turo Daddy Ishaq a tashi kujerar, bai rasa kafa ko hannu ba, amma raunikan jikinsa da suka sha plasta Allah ya yi yawa da su. Har gaban Mu’azzam Mummy ta kai Daddy Mansour.
Matsawa yayi kusa da Mu’azzam din sosai ya runguma shi a jikinsa, ya kai hannu bayansa yana shafawa a hankali, yana mai magana cikin taushin lafazi, yana tunasar da shi ya godewa Allah cikin kowanne hali. Ni’imominsa gare mu sun fi jarrabawarSa yawa.
“Mu’azzam ka ce Alhamdulillah! Ka yi wa dan uwanka addu’ar samun rahma da gafarar Ubangijiâ€.

Wato duk inda Gumsu ta ke, sai an san tana wuri, yanzu ma cewa ta yi cikin kulawa,
“Doctor me Mu’azzam ke son ci in dafa masa gobe?â€
A hankali Mu’azzam ya cira kai yana son ganin wace ce wannan ana ta rai da lafiya tana ta abinci?
Ganin kallon haushin da yake mata ta ce, “Kalle ni da kyau, ni ce Gumsun Daddynku. Mu’azzam komai ya yi zafi maganinsa Allah, ka daina kuka ka kama hailala. Na fi ka jin rashin dan uwanka, ni abokiyarsa ce, abokiyar shawararsa. Amma na san soyayyata da shi shi ne in ta yi masa addu’a ba zubda masa hawaye ba, ka ji Mu’azzam?â€
Cikin ransa yake tambaya, ita kuma wannan wace ce a cikin dangi??

Dr. Nebrass surutun Gumsu ya fara hawa masa kai. To balle kuma Mu’azzam ya sani, don haka ya ce su koma su bar Mu’azzam ya huta, tunda sun ganshi.
Da ma motar asibitin da suke ce ta kawo su da taimakon Nebrass, aka maida kowa inda yake.
Mu’azzam ya jingina da taga yana kallonsu, ana sanya majinyatan a mota with care, iyayensa masu tarin koshin lafiya da kuzari. Wato rayuwa gaba dayanta ba ta da tabbas! Kuma dan adam har ya mutu ba’a gama mai halitta ba; yau Baba Mansur ne ya zama gurgu. Wasu zafafan hawaye suka kwararo masa. Fata yake ya bude ido ya ga cewa duka wannan mafarki yake yi, fata yake ya juya bayansa ya ga shigowar Aboulkhair rike da magungunan da zai sha wunin yau maimakon Nebrass. Fata yake ya juya ya ga shigowarsa da jarida ya zo masa da labari. Fata yake ya juya ya ji ya ce ya sauko kasa su ci abinci Aalimarsa ta dafa musu! Fata yake ya juya ya ji shi yana hawowa upstairs din gidan sa da takun nan nashi gudu-gudu, sauri-sauri irin na zaratan matasa masu cike da koshin lafiya da kuzari.
Hakika dan adan bai hada sani da Ubangiji ba; Da ya san rayuwarsa a Las Vegas gajeriya ce da ya bar shi sun zauna tare a gidansa kamar yadda Aboulkhair din ke matukar so. Da ya san rayuwarsa gajeriya ce a Las Vegas da ko kusa bai bari sun zauna a muhalli daban-daban ba. Da ya jure wa kowacce irin hayaniya ta Aboulkhair ya zauna tare da shi har karshen rayuwarsa.....!

Inama ana maida hannun agogo baya!!!
Ina ma… Ina ma… Da na sani… Duka abubuwa ne wadanda dan Adam ba shi da maganinsu! Wadanda ba sa wanke zuciya a lokacin da suka riga suka yi wa zuciyar kawanya… Azabtar da zuciya suke don sun san cewa sun riga sun yi mata illa ta ko’ina. Kalmomi ne da ya tabbatar ba za su daina yi wa kunnuwansa azaba da amsa-kuwwa ba, daga yau har zuwa karshen rayuwarsa.
7/4/21, 10:50 AM - Buhainat: ADAMA DAUDA
Chapter 63 · 0% Book details